• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dabarun Cafke ‘Yan Ta’adda Cikin Sauki A Nijeriya – Pantami

by Bello Hamza
1 year ago
in Tsaro
0
Dabarun Cafke ‘Yan Ta’adda Cikin Sauki A Nijeriya – Pantami
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A daidai lokacin da al’umma ke alhinin kisan da ‘yan ta’adda suka yi wa Mai Martaba Sarkin Gobir, Isa Bawa, bayan da suka yi garkuwa da shi a dajin Sakkwato, jami’an tsaro sun dukufa wajen ganin sun cafko ‘yan ta’addan da suka aikata wannan ta’asar.

Domin samun cikakken nasara a faufukar kamo wadanna ‘yan ta’addan tsohon Ministan Sadarwa, Farfesa Ibrahim Ali Pantami ya bayar da shawarwarin dabarun da ya kamata jami’a tsaronmu su yi amfani da su domin cafko ‘yan ta’addan a cikin sauki.

  • Mun Dakile Yunkurin Kutse Ta Intanet Har Sau Miliyan 12 Lokacin Zabe – Pantami
  • AU Ta Naɗa Pantami Shugaban Tsara Manufofin Masana’antun Afrika Karo Na 4

A wani faifan bidiyo da ke yawo a kafafen sadarwa, Farfesa Pantami ya ce, za a iya kama wadannan ‘yan ta’adda a cikin sauki ta hanyar amfani nambobin SIM da NIN rajista da aka yi wa duk wani layin waya da ake amfani da shi.

Ya ce, a lokacin yana minista ya tabbatar da fara aiki da Sim da NIN Registration wanda in har an bi diddigi to babu wani barna da za a yi a fadin kasar nan da ba za a iya gano wanda ya aikata ba da kuma inda aka aikata ba. “Mun sha rubuta takarda a kan haka ga jami’an tsaro muna sanar dasu hanyoyin amfani da wannan dabarun, Allah ne shaida” in ji shi.

Ya ce, zuwa lokacin da ya sauka a kan karagar minista ya bar mutum fiye da miliyan 100 masu rajistar SIM da NIN kuma a lokacinsa ne aka yi wa mutum miliyan 60 rajistar. “Manufar shi ne don a samar wa da masu tsaro wani dandamali da za su yi amfani da shi wajen cimma manufar da ake bukata.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Ya kuma bayyana cewa, an sha yi masa barazana ga rayuwarsa a kan yadda ya tsayu na sai an yi amfani da tsarin yi wa Sim da NIN rajista.

Masana na ganin lallai ya kamata jami’an tsaro su rungumi wannan shawarar na Farfesa Pantami don a kawo karshen ayyukan ta’addanci a Nijeriya.

Idan za a iya tunawa a makon jiya ne al’umma sun kadu game da labarin kisan da ‘dan bindiga suka yi wa Sarkin Gobir na Gatawa Isa Bawa, bayan kwashe makwanni a hannun dan bindiga.

Lamarin ya zo ne kimanin mako daya bayan sakin wani bidiyo da ya rika yawo a shafukan sada zumunta, wanda ya nuna sarkin a hannun masu garkuwa da shi yana rokon gwamnati da iyalansa su cece shi daga hannun ‘dan bindiga.

Duk da cewa dan bindigar sun kwashe shekaru suna kashe-kashe a yankin na arewacin Najeriya, amma ba kasafai ake samun irin haka ba.

Sai dai sau da yawa bayan an gama jimami, lamarin sai ya kwanta sai kuma idan wani lamarin makamancin haka ya sake faruwa a gaba.

Gwamnatin Nijeriya dai ta dade tana cewa tana bakin kokarinta wajen shawo kan matsalar ta dan fashin daji, to amma abin na ci gaba da addabar al’ummar jihohi da dama.

Su ma gwamnonin jihohin na iyakar bakin kokarinsu ta wani fannin.

Tuni gwamnatocin jihohin yankin irin su Katsina da Zamfara da ita kanta Sokoto suka kaddamar da rundunonin dan sa-kai na jihohi domin shawo kan matsalar, amma har yanzu babu jihar da aka kawar da matsalar baki daya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: PantamiTsaro
ShareTweetSendShare
Previous Post

KANSIEC Ta Sauya Lokacin Zaben Kananan Hukumomin Kano Zuwa Oktoba 

Next Post

Xi: Sin Da Afirka A Ko Da Yaushe Al’umma Ce Mai Makomar Bai Daya

Related

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro
Tsaro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

5 days ago
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro
Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

5 days ago
Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi
Tsaro

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

2 weeks ago
Rashin Imani Ne Kisan Mutane 63 Da Boko Haram Ta Yi A Borno – Atiku
Tsaro

Rashin Imani Ne Kisan Mutane 63 Da Boko Haram Ta Yi A Borno – Atiku

2 weeks ago
‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja
Tsaro

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

2 weeks ago
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas
Tsaro

‘Yansanda Sun Ceto Wani Dan Shekara 25 Da Aka Sace A Jihar Kebbi

3 weeks ago
Next Post
Xi: Sin Da Afirka A Ko Da Yaushe Al’umma Ce Mai Makomar Bai Daya

Xi: Sin Da Afirka A Ko Da Yaushe Al’umma Ce Mai Makomar Bai Daya

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

September 18, 2025
Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

September 18, 2025
Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

September 18, 2025
Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

September 18, 2025
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

September 18, 2025
Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

September 18, 2025
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

September 18, 2025
NNPP

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

September 18, 2025
Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 18, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.