• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dabarun Cafke ‘Yan Ta’adda Cikin Sauki A Nijeriya – Pantami

by Bello Hamza
1 year ago
Ƴan ta'adda

A daidai lokacin da al’umma ke alhinin kisan da ‘yan ta’adda suka yi wa Mai Martaba Sarkin Gobir, Isa Bawa, bayan da suka yi garkuwa da shi a dajin Sakkwato, jami’an tsaro sun dukufa wajen ganin sun cafko ‘yan ta’addan da suka aikata wannan ta’asar.

Domin samun cikakken nasara a faufukar kamo wadanna ‘yan ta’addan tsohon Ministan Sadarwa, Farfesa Ibrahim Ali Pantami ya bayar da shawarwarin dabarun da ya kamata jami’a tsaronmu su yi amfani da su domin cafko ‘yan ta’addan a cikin sauki.

  • Mun Dakile Yunkurin Kutse Ta Intanet Har Sau Miliyan 12 Lokacin Zabe – Pantami
  • AU Ta Naɗa Pantami Shugaban Tsara Manufofin Masana’antun Afrika Karo Na 4

A wani faifan bidiyo da ke yawo a kafafen sadarwa, Farfesa Pantami ya ce, za a iya kama wadannan ‘yan ta’adda a cikin sauki ta hanyar amfani nambobin SIM da NIN rajista da aka yi wa duk wani layin waya da ake amfani da shi.

Ya ce, a lokacin yana minista ya tabbatar da fara aiki da Sim da NIN Registration wanda in har an bi diddigi to babu wani barna da za a yi a fadin kasar nan da ba za a iya gano wanda ya aikata ba da kuma inda aka aikata ba. “Mun sha rubuta takarda a kan haka ga jami’an tsaro muna sanar dasu hanyoyin amfani da wannan dabarun, Allah ne shaida” in ji shi.

Ya ce, zuwa lokacin da ya sauka a kan karagar minista ya bar mutum fiye da miliyan 100 masu rajistar SIM da NIN kuma a lokacinsa ne aka yi wa mutum miliyan 60 rajistar. “Manufar shi ne don a samar wa da masu tsaro wani dandamali da za su yi amfani da shi wajen cimma manufar da ake bukata.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ

Ya kuma bayyana cewa, an sha yi masa barazana ga rayuwarsa a kan yadda ya tsayu na sai an yi amfani da tsarin yi wa Sim da NIN rajista.

Masana na ganin lallai ya kamata jami’an tsaro su rungumi wannan shawarar na Farfesa Pantami don a kawo karshen ayyukan ta’addanci a Nijeriya.

Idan za a iya tunawa a makon jiya ne al’umma sun kadu game da labarin kisan da ‘dan bindiga suka yi wa Sarkin Gobir na Gatawa Isa Bawa, bayan kwashe makwanni a hannun dan bindiga.

Lamarin ya zo ne kimanin mako daya bayan sakin wani bidiyo da ya rika yawo a shafukan sada zumunta, wanda ya nuna sarkin a hannun masu garkuwa da shi yana rokon gwamnati da iyalansa su cece shi daga hannun ‘dan bindiga.

Duk da cewa dan bindigar sun kwashe shekaru suna kashe-kashe a yankin na arewacin Najeriya, amma ba kasafai ake samun irin haka ba.

Sai dai sau da yawa bayan an gama jimami, lamarin sai ya kwanta sai kuma idan wani lamarin makamancin haka ya sake faruwa a gaba.

Gwamnatin Nijeriya dai ta dade tana cewa tana bakin kokarinta wajen shawo kan matsalar ta dan fashin daji, to amma abin na ci gaba da addabar al’ummar jihohi da dama.

Su ma gwamnonin jihohin na iyakar bakin kokarinsu ta wani fannin.

Tuni gwamnatocin jihohin yankin irin su Katsina da Zamfara da ita kanta Sokoto suka kaddamar da rundunonin dan sa-kai na jihohi domin shawo kan matsalar, amma har yanzu babu jihar da aka kawar da matsalar baki daya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara
Tsaro

Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara

October 5, 2025
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ
Tsaro

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ

October 4, 2025
Bayan Sulhu  Da Ƴan Bindiga, An Saki Mutane 70 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Katsina
Tsaro

Bayan Sulhu  Da Ƴan Bindiga, An Saki Mutane 70 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Katsina

September 22, 2025
Next Post
Xi: Sin Da Afirka A Ko Da Yaushe Al’umma Ce Mai Makomar Bai Daya

Xi: Sin Da Afirka A Ko Da Yaushe Al’umma Ce Mai Makomar Bai Daya

LABARAI MASU NASABA

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.