ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mun Dakile Yunkurin Kutse Ta Intanet Har Sau Miliyan 12 Lokacin Zabe – Pantami

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Pantami

Ministan Sadarwa da Inganta Tattalin Arziki na zamani, Farfesa Isa Ali Ibrahim Pantami, ya bayyana yadda hadin gwiwar hukumoni  da ke karkashin ma’aikatarsa da suka hada da Hukumar Kula da Sadarwa ta Kasa (NCC), hukumar kula da fasahar sadarwar zamani (NITDA) da Galady Backbone (GBB) za su tabbatar da kare yunkurin yin kutse a intanet ga ‘yan Nijeriya gabanin zabe da lokacin zabe  da kuma bayan zaben 2023.

A wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Uwa Suleiman ta fitar, Ministan ya bayyana cewa an dakile yunkurin kutse a intanet har sau miliyan 12, wanda hakan ya kara kwarin gwiwa ga ‘yan kasar tare da kai ga gudanar da zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisun tarayya cikin gaskiya da adalci.

  • Xi Ya Ba Da Sabon Tunani Da Shawarar Wayewar Kai Ta Duniya Don Inganta Zamanantar Da Daukacin Bil-Adama
  • Binciken Kayan Zabe: Atiku Ya Janye Sabbin Ƙorafe-Ƙorafe Da Ya Shigar A Kan INEC

Pantami ya kara da cewa matakin ya yi daidai da manufofi da hukumar tsara manufofin tattalin arziki na zamani ta kasa (NDEPS), inda ya kara da cewa bukatar tabbatar da tsaron intanet a Nijeriya ya sanya aka kafa wani tawaga daga hukumar NITDA da za ta dunga amsar bayanan gaggawa daga kwamfuta (CERRT) da kwamitin ba da kulawar kutse na kwamfuta (CSIRT) da cibiyar tsaro ta GBB (SOC).

ADVERTISEMENT

An kafa cibiyoyin ne tsakanin shekarar 2020 zuwa 2022, bisa tsarin manufofin ministar kuma sun rika sanya ido a shafukan intanet na Nijeriya kan yiwuwar yin barazana kutse da daukar matakan da suka dace domin dakile su, a dai-daikunsu da kuma a kungiyance tare da hadin gwiwar sauran masu ruwa da tsaki.

Sanarwar ta ce, “Yana da kyau a lura cewa, a tunkarar babban zabe na 2023, bayanan sirri sun nuna karuwar barazanar intanet a Nijeriya. Saboda haka, barazanar ga gidajen intanet na jama’a da tashoshinsu sun kai kusan 1,550,000 kowace rana. Duk da haka, wannan ya haura zuwa 6,997,277 a ranar zaben shugaban kasa.

LABARAI MASU NASABA

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

“Ministan sadarwa da inganta tattalin arziki na zamani, a matsayinsa na Farfesa kan tsaro ta intanet kuma wanda ke da sha’awar tabbatar da tsaro da ta yanar gizo, ya umurci duk masu fafutuka da su inganta ayyukan su na awoyi 24 har zuwa kwanaki 7 na hanyoyin sadarwa domin dakile yunkurin kai kutse tun daga ranar 24 ga Fabrairun 2023 zuwa 27 ga Fabrairu 2023.”

Sanarwar ta tuna cewa a ranar 24 ga Fabrairun 2023, ministan ya kaddamar da kwamitin bayar da shawarwari ga taron intanet a Nijeriya da hanyoyin sadarwa na fasahar sadarwa.

Ta ce kwamitin da ke karkashin shugabancin shugaban hukumar NCC, tare da shugabannin NCC, NITDA da GBB a matsayin mambobi, an dora musu alhakkin ayyuka kamar haka, sa ido kan hanyoyin sadarwar don samun nasarar gudanar da sahihin zabe, habakawa da aiwatar da tsare-tsare masu muhimmanci kan ayyukan fasahar zamani, dakile barazanar kutse a intanet, kirkirar hanyoyin da amfani da fasaha, mayar da martani ga hare-haren intanet da kuma dawowa daga duk wani lalacewa da aka yi da sauri.

Sauran sun hada da samar da cikakkiyar tantance hadarin, da yin nazari kan iyawar al’umma ta intanet a halin yanzu, da gano gibin da ya kamata a magance, da kuma ba da shawarwari na kwararru ga gwamnati kan ingantaccen amfani da fasahar zamani wajen gudanar da babban zaben 2023.

“An samu adadin yunkurin yin kutse har 12,988,978, wadanda suka samo asali daga ciki da wajen Nijeriya. Yana da kyau a lura cewa cibiyoyin sun yi nasarar toshe wadannan hare-hare da kuma kara fadada cibiyoyin da hanyar da suka dace.

“Hukumomin karkashin kulawar ma’aikatar sadarwa da inganta tattalin arziki na zamani sun taka muhimmiyar rawa wajen samar da yanayi mai dacewa don samun nasarar gudanar da sahihin zabe.

“Ministan ya yaba wa duk masu ruwa da tsaki a tsarin inganta tattalin arzikin zamani don goyon bayansu wanda ya haifar da wannan nasarar da ba a taba samu ba. Abu mafi muhimmanci shi ne, ministan ya lura cewa wadannan nasarorin sun samo asali ne sakamakon jajircewar gwamnatin Shugaba kasa Muhammadu Buhari, na tabbatar da samun nasarar sauye-sauyen da Nijeriya ta samu a fannin tattalin arziki na zamani.

“Sashin inganta tattalin arzikin zamani ya sami ci gaba da goyon bayan shugaban kasa kuma abun a yaba ne. Ya kuma yi fatan za a yi amfani da darussan da aka koya a lokacin aikin yadda ya kamata a zabukan da ke tafe”.

Pantami
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

MASU ALAKA

Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 
Labarai

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
Manyan Labarai

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Next Post
Kwararren Birtaniya: Gwamnatin Sin Tana Sauraron Abin Da Jama’a Ke So Yayin Yanke Shawara

Kwararren Birtaniya: Gwamnatin Sin Tana Sauraron Abin Da Jama’a Ke So Yayin Yanke Shawara

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

July 15, 2026
Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.