ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mun Dakile Yunkurin Kutse Ta Intanet Har Sau Miliyan 12 Lokacin Zabe – Pantami

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Pantami

Ministan Sadarwa da Inganta Tattalin Arziki na zamani, Farfesa Isa Ali Ibrahim Pantami, ya bayyana yadda hadin gwiwar hukumoni  da ke karkashin ma’aikatarsa da suka hada da Hukumar Kula da Sadarwa ta Kasa (NCC), hukumar kula da fasahar sadarwar zamani (NITDA) da Galady Backbone (GBB) za su tabbatar da kare yunkurin yin kutse a intanet ga ‘yan Nijeriya gabanin zabe da lokacin zabe  da kuma bayan zaben 2023.

A wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Uwa Suleiman ta fitar, Ministan ya bayyana cewa an dakile yunkurin kutse a intanet har sau miliyan 12, wanda hakan ya kara kwarin gwiwa ga ‘yan kasar tare da kai ga gudanar da zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisun tarayya cikin gaskiya da adalci.

  • Xi Ya Ba Da Sabon Tunani Da Shawarar Wayewar Kai Ta Duniya Don Inganta Zamanantar Da Daukacin Bil-Adama
  • Binciken Kayan Zabe: Atiku Ya Janye Sabbin Ƙorafe-Ƙorafe Da Ya Shigar A Kan INEC

Pantami ya kara da cewa matakin ya yi daidai da manufofi da hukumar tsara manufofin tattalin arziki na zamani ta kasa (NDEPS), inda ya kara da cewa bukatar tabbatar da tsaron intanet a Nijeriya ya sanya aka kafa wani tawaga daga hukumar NITDA da za ta dunga amsar bayanan gaggawa daga kwamfuta (CERRT) da kwamitin ba da kulawar kutse na kwamfuta (CSIRT) da cibiyar tsaro ta GBB (SOC).

ADVERTISEMENT

An kafa cibiyoyin ne tsakanin shekarar 2020 zuwa 2022, bisa tsarin manufofin ministar kuma sun rika sanya ido a shafukan intanet na Nijeriya kan yiwuwar yin barazana kutse da daukar matakan da suka dace domin dakile su, a dai-daikunsu da kuma a kungiyance tare da hadin gwiwar sauran masu ruwa da tsaki.

Sanarwar ta ce, “Yana da kyau a lura cewa, a tunkarar babban zabe na 2023, bayanan sirri sun nuna karuwar barazanar intanet a Nijeriya. Saboda haka, barazanar ga gidajen intanet na jama’a da tashoshinsu sun kai kusan 1,550,000 kowace rana. Duk da haka, wannan ya haura zuwa 6,997,277 a ranar zaben shugaban kasa.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

“Ministan sadarwa da inganta tattalin arziki na zamani, a matsayinsa na Farfesa kan tsaro ta intanet kuma wanda ke da sha’awar tabbatar da tsaro da ta yanar gizo, ya umurci duk masu fafutuka da su inganta ayyukan su na awoyi 24 har zuwa kwanaki 7 na hanyoyin sadarwa domin dakile yunkurin kai kutse tun daga ranar 24 ga Fabrairun 2023 zuwa 27 ga Fabrairu 2023.”

Sanarwar ta tuna cewa a ranar 24 ga Fabrairun 2023, ministan ya kaddamar da kwamitin bayar da shawarwari ga taron intanet a Nijeriya da hanyoyin sadarwa na fasahar sadarwa.

Ta ce kwamitin da ke karkashin shugabancin shugaban hukumar NCC, tare da shugabannin NCC, NITDA da GBB a matsayin mambobi, an dora musu alhakkin ayyuka kamar haka, sa ido kan hanyoyin sadarwar don samun nasarar gudanar da sahihin zabe, habakawa da aiwatar da tsare-tsare masu muhimmanci kan ayyukan fasahar zamani, dakile barazanar kutse a intanet, kirkirar hanyoyin da amfani da fasaha, mayar da martani ga hare-haren intanet da kuma dawowa daga duk wani lalacewa da aka yi da sauri.

Sauran sun hada da samar da cikakkiyar tantance hadarin, da yin nazari kan iyawar al’umma ta intanet a halin yanzu, da gano gibin da ya kamata a magance, da kuma ba da shawarwari na kwararru ga gwamnati kan ingantaccen amfani da fasahar zamani wajen gudanar da babban zaben 2023.

“An samu adadin yunkurin yin kutse har 12,988,978, wadanda suka samo asali daga ciki da wajen Nijeriya. Yana da kyau a lura cewa cibiyoyin sun yi nasarar toshe wadannan hare-hare da kuma kara fadada cibiyoyin da hanyar da suka dace.

“Hukumomin karkashin kulawar ma’aikatar sadarwa da inganta tattalin arziki na zamani sun taka muhimmiyar rawa wajen samar da yanayi mai dacewa don samun nasarar gudanar da sahihin zabe.

“Ministan ya yaba wa duk masu ruwa da tsaki a tsarin inganta tattalin arzikin zamani don goyon bayansu wanda ya haifar da wannan nasarar da ba a taba samu ba. Abu mafi muhimmanci shi ne, ministan ya lura cewa wadannan nasarorin sun samo asali ne sakamakon jajircewar gwamnatin Shugaba kasa Muhammadu Buhari, na tabbatar da samun nasarar sauye-sauyen da Nijeriya ta samu a fannin tattalin arziki na zamani.

“Sashin inganta tattalin arzikin zamani ya sami ci gaba da goyon bayan shugaban kasa kuma abun a yaba ne. Ya kuma yi fatan za a yi amfani da darussan da aka koya a lokacin aikin yadda ya kamata a zabukan da ke tafe”.

Pantami
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Kwararren Birtaniya: Gwamnatin Sin Tana Sauraron Abin Da Jama’a Ke So Yayin Yanke Shawara

Kwararren Birtaniya: Gwamnatin Sin Tana Sauraron Abin Da Jama’a Ke So Yayin Yanke Shawara

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.