ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dabarun Cafke ‘Yan Ta’adda Cikin Sauki A Nijeriya – Pantami

by Bello Hamza
2 years ago
Ƴan ta'adda

A daidai lokacin da al’umma ke alhinin kisan da ‘yan ta’adda suka yi wa Mai Martaba Sarkin Gobir, Isa Bawa, bayan da suka yi garkuwa da shi a dajin Sakkwato, jami’an tsaro sun dukufa wajen ganin sun cafko ‘yan ta’addan da suka aikata wannan ta’asar.

Domin samun cikakken nasara a faufukar kamo wadanna ‘yan ta’addan tsohon Ministan Sadarwa, Farfesa Ibrahim Ali Pantami ya bayar da shawarwarin dabarun da ya kamata jami’a tsaronmu su yi amfani da su domin cafko ‘yan ta’addan a cikin sauki.

  • Mun Dakile Yunkurin Kutse Ta Intanet Har Sau Miliyan 12 Lokacin Zabe – Pantami
  • AU Ta Naɗa Pantami Shugaban Tsara Manufofin Masana’antun Afrika Karo Na 4

A wani faifan bidiyo da ke yawo a kafafen sadarwa, Farfesa Pantami ya ce, za a iya kama wadannan ‘yan ta’adda a cikin sauki ta hanyar amfani nambobin SIM da NIN rajista da aka yi wa duk wani layin waya da ake amfani da shi.

ADVERTISEMENT

Ya ce, a lokacin yana minista ya tabbatar da fara aiki da Sim da NIN Registration wanda in har an bi diddigi to babu wani barna da za a yi a fadin kasar nan da ba za a iya gano wanda ya aikata ba da kuma inda aka aikata ba. “Mun sha rubuta takarda a kan haka ga jami’an tsaro muna sanar dasu hanyoyin amfani da wannan dabarun, Allah ne shaida” in ji shi.

Ya ce, zuwa lokacin da ya sauka a kan karagar minista ya bar mutum fiye da miliyan 100 masu rajistar SIM da NIN kuma a lokacinsa ne aka yi wa mutum miliyan 60 rajistar. “Manufar shi ne don a samar wa da masu tsaro wani dandamali da za su yi amfani da shi wajen cimma manufar da ake bukata.

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2, Sun Yi Garkuwa Da 30 A Kogi

NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano

Ya kuma bayyana cewa, an sha yi masa barazana ga rayuwarsa a kan yadda ya tsayu na sai an yi amfani da tsarin yi wa Sim da NIN rajista.

Masana na ganin lallai ya kamata jami’an tsaro su rungumi wannan shawarar na Farfesa Pantami don a kawo karshen ayyukan ta’addanci a Nijeriya.

Idan za a iya tunawa a makon jiya ne al’umma sun kadu game da labarin kisan da ‘dan bindiga suka yi wa Sarkin Gobir na Gatawa Isa Bawa, bayan kwashe makwanni a hannun dan bindiga.

Lamarin ya zo ne kimanin mako daya bayan sakin wani bidiyo da ya rika yawo a shafukan sada zumunta, wanda ya nuna sarkin a hannun masu garkuwa da shi yana rokon gwamnati da iyalansa su cece shi daga hannun ‘dan bindiga.

Duk da cewa dan bindigar sun kwashe shekaru suna kashe-kashe a yankin na arewacin Najeriya, amma ba kasafai ake samun irin haka ba.

Sai dai sau da yawa bayan an gama jimami, lamarin sai ya kwanta sai kuma idan wani lamarin makamancin haka ya sake faruwa a gaba.

Gwamnatin Nijeriya dai ta dade tana cewa tana bakin kokarinta wajen shawo kan matsalar ta dan fashin daji, to amma abin na ci gaba da addabar al’ummar jihohi da dama.

Su ma gwamnonin jihohin na iyakar bakin kokarinsu ta wani fannin.

Tuni gwamnatocin jihohin yankin irin su Katsina da Zamfara da ita kanta Sokoto suka kaddamar da rundunonin dan sa-kai na jihohi domin shawo kan matsalar, amma har yanzu babu jihar da aka kawar da matsalar baki daya.

Ƴan ta'adda
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dole Ne Afirka Ta Zamanantar Da Sufurin Jiragen Ruwa —Ɗantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Yadda Oyetola Ya Ƙaddamar Da Babban Taron Ƙungiyar  PMAWCA A Legas
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Lokaci Ya Yi Da Matasan Nijeriya Za Su Ƙwato Ƙasarsu — Kwamred Yahaya Abdullahi
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kamfanin Dangote Na Kara Karfafa Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Jihar Neja

MASU ALAKA

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2, Sun Yi Garkuwa Da 30 A Kogi
Tsaro

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2, Sun Yi Garkuwa Da 30 A Kogi

June 1, 2026
NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
Tsaro

NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano

May 31, 2026
Yadda Muka Kashe Masu Garkuwa 4 Da Suke Shirin Kai Hari Kan Attajirai A Legas —CP
Tsaro

Yadda Muka Kashe Masu Garkuwa 4 Da Suke Shirin Kai Hari Kan Attajirai A Legas —CP

May 31, 2026
Next Post
Xi: Sin Da Afirka A Ko Da Yaushe Al’umma Ce Mai Makomar Bai Daya

Xi: Sin Da Afirka A Ko Da Yaushe Al’umma Ce Mai Makomar Bai Daya

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.