ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dabarun Cafke ‘Yan Ta’adda Cikin Sauki A Nijeriya – Pantami

by Bello Hamza
2 years ago
Ƴan ta'adda

A daidai lokacin da al’umma ke alhinin kisan da ‘yan ta’adda suka yi wa Mai Martaba Sarkin Gobir, Isa Bawa, bayan da suka yi garkuwa da shi a dajin Sakkwato, jami’an tsaro sun dukufa wajen ganin sun cafko ‘yan ta’addan da suka aikata wannan ta’asar.

Domin samun cikakken nasara a faufukar kamo wadanna ‘yan ta’addan tsohon Ministan Sadarwa, Farfesa Ibrahim Ali Pantami ya bayar da shawarwarin dabarun da ya kamata jami’a tsaronmu su yi amfani da su domin cafko ‘yan ta’addan a cikin sauki.

  • Mun Dakile Yunkurin Kutse Ta Intanet Har Sau Miliyan 12 Lokacin Zabe – Pantami
  • AU Ta Naɗa Pantami Shugaban Tsara Manufofin Masana’antun Afrika Karo Na 4

A wani faifan bidiyo da ke yawo a kafafen sadarwa, Farfesa Pantami ya ce, za a iya kama wadannan ‘yan ta’adda a cikin sauki ta hanyar amfani nambobin SIM da NIN rajista da aka yi wa duk wani layin waya da ake amfani da shi.

ADVERTISEMENT

Ya ce, a lokacin yana minista ya tabbatar da fara aiki da Sim da NIN Registration wanda in har an bi diddigi to babu wani barna da za a yi a fadin kasar nan da ba za a iya gano wanda ya aikata ba da kuma inda aka aikata ba. “Mun sha rubuta takarda a kan haka ga jami’an tsaro muna sanar dasu hanyoyin amfani da wannan dabarun, Allah ne shaida” in ji shi.

Ya ce, zuwa lokacin da ya sauka a kan karagar minista ya bar mutum fiye da miliyan 100 masu rajistar SIM da NIN kuma a lokacinsa ne aka yi wa mutum miliyan 60 rajistar. “Manufar shi ne don a samar wa da masu tsaro wani dandamali da za su yi amfani da shi wajen cimma manufar da ake bukata.

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi

Ƴan Bindiga Sun Kashe Hakimin Gundumar Gwande A Jihar Filato

Ya kuma bayyana cewa, an sha yi masa barazana ga rayuwarsa a kan yadda ya tsayu na sai an yi amfani da tsarin yi wa Sim da NIN rajista.

Masana na ganin lallai ya kamata jami’an tsaro su rungumi wannan shawarar na Farfesa Pantami don a kawo karshen ayyukan ta’addanci a Nijeriya.

Idan za a iya tunawa a makon jiya ne al’umma sun kadu game da labarin kisan da ‘dan bindiga suka yi wa Sarkin Gobir na Gatawa Isa Bawa, bayan kwashe makwanni a hannun dan bindiga.

Lamarin ya zo ne kimanin mako daya bayan sakin wani bidiyo da ya rika yawo a shafukan sada zumunta, wanda ya nuna sarkin a hannun masu garkuwa da shi yana rokon gwamnati da iyalansa su cece shi daga hannun ‘dan bindiga.

Duk da cewa dan bindigar sun kwashe shekaru suna kashe-kashe a yankin na arewacin Najeriya, amma ba kasafai ake samun irin haka ba.

Sai dai sau da yawa bayan an gama jimami, lamarin sai ya kwanta sai kuma idan wani lamarin makamancin haka ya sake faruwa a gaba.

Gwamnatin Nijeriya dai ta dade tana cewa tana bakin kokarinta wajen shawo kan matsalar ta dan fashin daji, to amma abin na ci gaba da addabar al’ummar jihohi da dama.

Su ma gwamnonin jihohin na iyakar bakin kokarinsu ta wani fannin.

Tuni gwamnatocin jihohin yankin irin su Katsina da Zamfara da ita kanta Sokoto suka kaddamar da rundunonin dan sa-kai na jihohi domin shawo kan matsalar, amma har yanzu babu jihar da aka kawar da matsalar baki daya.

Ƴan ta'adda
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Amfani Da Matar Soja Wajen Isar Da Sakon Bukata

MASU ALAKA

Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi
Tsaro

Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi

June 21, 2026
Ƴan Bindiga Sun Kashe Hakimin Gundumar Gwande A Jihar Filato
Tsaro

Ƴan Bindiga Sun Kashe Hakimin Gundumar Gwande A Jihar Filato

June 19, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Manyan Labarai

Mata Ta Hallaka Mijinta Da Wuƙa Watanni Biyu Bayan Aure A Kano

June 17, 2026
Next Post
Xi: Sin Da Afirka A Ko Da Yaushe Al’umma Ce Mai Makomar Bai Daya

Xi: Sin Da Afirka A Ko Da Yaushe Al’umma Ce Mai Makomar Bai Daya

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.