• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daga 2016 Zuwa 2020, An Kashe Dala Biliyan 6 Wajen Shigo Da Alkama -CBN

by Abubakar Abba
2 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Daga 2016 Zuwa 2020, An Kashe Dala Biliyan 6 Wajen Shigo Da Alkama -CBN
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wani rahoton da babban bankin Nijeriya CBN ya fitar, ya nuna cewa, yawan adadin alkamar da aka shigo da ita daga kasar waje daga shekarar 2016 zuwa shekarar 2020, an kashe kimanin dala biliyan shida.

A cewar rahoton, wannan ba za ta sabu ba,  musamman ganin cewa,  za a iya nomanta da yawa a kasar nan.

  • ’Yar Kasuwa Elizabeth Homes: Labarin Tashe Da Rushewarta (II)
  • Mahaifin Da Ake Zargi Da Lalata Da ‘Yarsa Ya Gurfana A Kotu

Bisa wasu alkaluman da aka samo daga gun   hukumar kididdiga ta kasa NBS ta bayyana cewa, kudaden da aka kashe wajen shigo Alkamar daga waje a cikin zango uku na shekarar 2022 sun kai kashi 16.1 a cikin dari,  inda wannan ya nuna cewa, kudaden sun kai kasa da wanda aka kashe a shekarar 2021.

Jimmlar naira biliyan 753.597 aka yi amfani da su wajen shigo da Alkama daga kasar waje zuwa cikin kasar nan a cikin watanni tara da suka gabata a shekarar 2022.

Wannan ya nuna cewa,  kasar ce ke akan gaba wajen shigo da Alkamar daga ketaren.

Labarai Masu Nasaba

Nijeriya Da Brazil Sun Ƙulla Yarjejeniyar Horar Da Matasa Kiwon Dabbobi

Hikimar Yunƙurin Sake Farfaɗo Da Noman Filanten A Jihar Nasarawa

Har ila yau, Alkamar ita ce ta uku wajen amfanin gona zuwa cikin kasar nan baya ga man fetur.

Akasari dai, ana da matukar bukatar Alkama a cikin kasar nan,  musamman ganin yadda ake yin da ita wajen sarrafa nau’ukan abinci da ban da ban a kasar.

Bugu da kari, a cikin zango na uku ma shekarar 2022 Alkamar da aka shigo da ita daga ketaren zuwa cikin kasar nan,  bata kai yawan kudaden da aka kashe wajen shigo da sauran amfanin gona cikin Nijeriya ba

Hakazalika,  a zangon farko na watanni uku 2021, an kashe naira biliyan 898.19 da kuma naira biliyan 258.3 don shigo da ita daga ketaren.

A zangon farko na shekarar 2021 an kashe naira biliyan 324.72 da kuma kashe naira biliyan

315.17 don shigo da sauran kayan abinci,  nda kuma a zango na biyu da na uku na shekarar 2021.

 Bugu da kari, a 2022  an kashe naira biliyan 258.31 da kuma naira biliyan 242.66 tare da kashe naira biliyan 252.62 don a shigo da Alkamar daga ketaren.

Har ila yau,  a shekarar 2021 jimmalar Alkamar da aka shigo da ita daga waje zuwa cikin kasar nan, kudin da aka kashe ya kai naira tiriliyan 1.29, inda hakan ya kai karuwar kashi 71.1 a cikin dari idan aka kwatanta da naira biliyan 756.92 da aka kashe a 2020.

Hakazalika, sakamakon yakin da kasar Rasha ke ci gaba da yi da kasar Ukraine, haka ya kara haifar da hauhawan farashin na Alkamar a daukcin fadin duniya.

An ruwaito cewa ministan akin noma da raya karkara Mahmood Abubakar ya bayyana cewa, ganin,yadda yawan al’ummar kasar nan ke kara karuwa da kuma yadda ake kara ci gaba bukatar ta Alkamar a kasar, akwai bukatar a kara yawan yin nomanta a kasar don a samar da wafatacciyar ta.

A cewar ministan,  gwamnatin tarayya na ci gaba da mayar da hankali a fannin na nomanta,  inda ya kara da cewa, a duk shekara Nijeriya na bukatar kimanin tan miliyan  5.7, inda kuma yawan adadin tan, 420,000 kawai ake iya noma wa a kasar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AlkamaCBNNoma
ShareTweetSendShare
Previous Post

’Yar Kasuwa Elizabeth Homes: Labarin Tashe Da Rushewarta (II)

Next Post

Yarfe Da Kazafi Tsakanin Manyan ‘Yan Takarar Shugabancin Nijeriya: Duk Gautar Ja Ce?

Related

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)
Noma Da Kiwo

Nijeriya Da Brazil Sun Ƙulla Yarjejeniyar Horar Da Matasa Kiwon Dabbobi

5 days ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)
Noma Da Kiwo

Hikimar Yunƙurin Sake Farfaɗo Da Noman Filanten A Jihar Nasarawa

6 days ago
Jigawa Za Ta Samar Da Kashi 25 Na Shinkafar Da Nijeriya Ke Bukata – Hon Abdurahman 
Noma Da Kiwo

Jigawa Za Ta Samar Da Kashi 25 Na Shinkafar Da Nijeriya Ke Bukata – Hon Abdurahman 

6 days ago
Kin Biyan Bashi Daga Wasu Manoma Zai Kawo Cikas Ga Noman Shinkafa A Bana – Ɗan Madamin Samaru 
Noma Da Kiwo

Kin Biyan Bashi Daga Wasu Manoma Zai Kawo Cikas Ga Noman Shinkafa A Bana – Ɗan Madamin Samaru 

1 week ago
Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA
Noma Da Kiwo

Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA

2 weeks ago
Wani Gidan Gona A Jihar Ogun Zai Fitar Da Tarwada Ta Kimanin Naira Biliyan Shida A 2025
Noma Da Kiwo

Wani Gidan Gona A Jihar Ogun Zai Fitar Da Tarwada Ta Kimanin Naira Biliyan Shida A 2025

2 weeks ago
Next Post
Yarfe Da Kazafi Tsakanin Manyan ‘Yan Takarar Shugabancin Nijeriya: Duk Gautar Ja Ce?

Yarfe Da Kazafi Tsakanin Manyan ‘Yan Takarar Shugabancin Nijeriya: Duk Gautar Ja Ce?

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

June 27, 2025
Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

June 27, 2025
Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

June 27, 2025
Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

June 27, 2025
Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

June 27, 2025
Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

June 27, 2025
Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba

Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba

June 27, 2025
JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don ÆŠaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don ÆŠaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

June 27, 2025
Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai

Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai

June 27, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)

June 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.