• Leadership Hausa
Saturday, April 1, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yarfe Da Kazafi Tsakanin Manyan ‘Yan Takarar Shugabancin Nijeriya: Duk Gautar Ja Ce?

by Bello Hamza
2 months ago
in Bakon Marubuci
0
Yarfe Da Kazafi Tsakanin Manyan ‘Yan Takarar Shugabancin Nijeriya: Duk Gautar Ja Ce?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ana ‘yan makonni zuwa babban zaben 2023, fagen siyasar kasar nan yana kara zafafa inda manyan jam’iyyun biyu na ci gaba da yi wa juna yarfe, kazafi da sharin aikata cin-hanci da almundahana a tsakaninsu.

Bangaren dan takarar shugabancin kasa na jam’iyyar APC, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP Alhaji Atiku Abubakar suke jifar juna da wadannan zarge-zargen.

  • Naja’atu: Cikon Banci Ce A Wurinmu, Tun Da Muka Kore Ta Take Ta Sambatu – APC   
  • Karin Bayani Kan Harin Bom Din Da Ya Kashe Fulani 39 A Nasarawa — Ganau

Jam’iyyar APC ce ta fara harbo mizal din. Kusan mako daya daya wuce ne kwamitin yakin neman zaben Tinubu/Shettima ya nemi a gaggauta kamawa tare da hukunta dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP Alhaji Atiku Abubakar saboda zargin badakalar kudade da suke zargin ya aikata tare kuma da aikata manyan laifuka.

Kungiyar ta bayyana haka ne a taron manema labarai da ta kira a Abuja inda ta kara da cewa, Atiku bashi da wani kariya na tsarin mulki da zai hana a kama shi tare da hukunta shi, shugabanin bangaren watsa labarai a kwamitin yakin neman zaben  Tinubu da suka hada da Dele Alake, Festus Keyamo, Bayo Onanuga, Femi Fani-Kayode, da kuma Idris Mohammed suka jagoranci taron manema labaran, sun kuma nemi Atiku ya gaggauta yin murabus daga takarar shugabancin kasa  da yake yi tare da ba wa al’ummar Nijeriya hakuri a kan zargin da ake yi masa na karkatar da kudaden al’umma zuwa aljihunsa.

Sun kuma yi alkawarin garzayawa kotu don dakatar da takarar da yunkurin da tsohon mataimakin shugaban kasar yake yi na zama shugaban kasa a zaben da za a gudanar wata mai zuwa. Wannan zargin yana zuwa ne bayan da wani tsohon hadimin Atiku, Mista Michael Achimugu, ya yi zargin cewa, Atiku ya yi amfani da shirin nan na sayen motocin SPB wajen kwasar kudade daga tsohon Gwamnan Jihar Filato Joshua Dariye wanda kotu ta daure saboda badakalar kudaden kare zaizayar kasa na Jihar Filato. Tuni dai Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya yi masa afuwa. A lokacin da Atiku yake mataimakin shugaban Nijeriya daga 1999 zuwa 2007, Dariye na a matsayin gwamna ne a daidai lokacin.

Labarai Masu Nasaba

Zubar Da Jini A Siyasar Nijeriya!

Dubi Ga Barazanar Da Masu Kada Kuri’a Ke Fuskanta

A ranar Lahadi 22 ga watan Janairu 2023, bangaren kwamitin yakin neman zaben Atiku suka mayar da nasu martanin, inda suka bukaci hukumar yaki da fataucin miyagin kwayoyi NDLEA da hukumar EFCC su gaggauta kama dan takarar shugabancin kasa na jam’iyyar APC, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu. Bayanin haka yana kunshe ne a jawabin da mambobin kwamitijn yakin neman zaben jam’iyyar PDP suka yi a ta bakin Bashorun Dele Momodu, Daniel Bwala, Mista Paul Ibe da kuma mataimaki na musamman ga Atiku a kan harkar yada labarai, Phrank Shaibu a ganawar da suka yi manema labarai.

A cikin jawabin su, Shaibu ya lura da cewa, Nijeriya na fuskantar wai yanayi da ya kamata a yi takatsanstan wajen zaban wanda zai zama shugaban kasa nag aba , kuma duk wani kuskure da za a yi zai iya zama bala’i ga kasa baki daya. Ya kara da cewa,“Nijeriya na fuskantar matsalolin da suka hada da na ‘yan bindiga, garkuwa da mutane da sauran miyagun ayyukan ta’addanci wadanda kuma suke da alaka da tu’ammali da miyagun kwayoyi. “A saboda haka zai iya zama tashin hankali in aka zabi wanda rayuwarsa ke tattare da badakalar harkar kwaya da safarar ta.”

Ya bayyana cewa, Tinubu na fuskantar badakalar Dala 460,000 wanda ake zargin ya samu ne daga badakalar safarar miyagun kwayoyi a kasar Amurka, ya kuma kamata a kara zurfafa bincike don gano cikakiyyar gaskiyar lamarin. “A kan haka muna kira ga hukumar NDLEA su gagaggauta kama Bola Ahmed Tinubu su kuma tabbatar da hukunta shi.

Wananan takaddamar da yarfe a tsakanin manyan jam’iyyun kasar nan abu ne da zai iya tayar da kura a sararin samaniyar harkokin siyasar kasar nan kamar yadda kungiyar Afenifere ta ankarar ta bakin sakatarenta na kasa Kwamrade Jare Ajayi, amma kuma wannan yana kara fitowa ne da lamarin cin-hanci da rashawa matsayin wani abin da yakamata ya zama a kan gaba a cikin abubuwan da yakamata a rika tattauanwa a fagen yakin neman zabe a tsakanin jam’iyyun kasar nan.

Abin lura a nan shi e dukkan jam’iyyun kasar masu neman shugabancin kasar na ikiirarin za su jagoranci yaki da cin-hanci da rashawa in kai ga ci.

Za a iya fahimtar yadda matsalar cin-hanci da rashawa ta yi katutu a harkar kasar nan in aka lura da cewa, kungiyar ‘Transparency International (TI)’ ta ayyana Nijeriya a matsayin kasar da ke a kan gaba a cikin kassashen da aka fi cin-hanci da rashawa a duniya, saboda haka tabbas ya kamata lamarin cin-hanci da rashawa ya zama a kan gaba kuma ma’auni na alkawurran da manya jam’iyyumu za su yi amfani da su wajen yakin neman zaben da ake yi a halin yunzu a shirye-shiryen fuskantar zaben 2023.

Yana da matukar muhimmanci hukumomin da abin ya shafa su tabbatar da bincikar zarge-zarge biyu da bangarorin suka yi wa junansu. Bai kamata a yi watsi da zarge-zargen ba.

Ganin iri wannan zarge-zarge masu tayar da hankali ne a kan manyan ‘yan takarar shugabancin kasar a halin yanzu al’amura duk sun koma a hannun ‘yan Nijeriya masu dauke da katin zabe, ya kamata su yi karatun ta natsu su zabawa kasar nan wanda ya fi dama-dama don daga dukkan alamu tsakanin manyan ‘yan takarar shugabancin kasar nan duk gautar ja ce.

Tags: SiyasaYarfeZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Daga 2016 Zuwa 2020, An Kashe Dala Biliyan 6 Wajen Shigo Da Alkama -CBN

Next Post

An Yi Gwanjon Rigar Da Pele Ya Buga Kofin Duniya Na Karshe Da Ita

Related

Zubar Da Jini A Siyasar Nijeriya!
Bakon Marubuci

Zubar Da Jini A Siyasar Nijeriya!

3 weeks ago
Dubi Ga Barazanar Da Masu Kada Kuri’a Ke Fuskanta
Bakon Marubuci

Dubi Ga Barazanar Da Masu Kada Kuri’a Ke Fuskanta

1 month ago
Canji Kudi: Matakin Da Gwamnonin Arewa Suka Dauka Barazana Ce Ga Dimokuradiyya
Bakon Marubuci

Canji Kudi: Matakin Da Gwamnonin Arewa Suka Dauka Barazana Ce Ga Dimokuradiyya

1 month ago
Bashin Dala Miliyan 350 Da Kaduna Ta Ciyo: Nasara Ko Akasinta?
Bakon Marubuci

Bashin Dala Miliyan 350 Da Kaduna Ta Ciyo: Nasara Ko Akasinta?

2 months ago
Yaushe Za A Dakatar Da Yi Wa `Yan Arewa Kisan Gilla?
Bakon Marubuci

Yaushe Za A Dakatar Da Yi Wa `Yan Arewa Kisan Gilla?

2 months ago
Ya Wajaba INEC Ta Hana Yakin Neman Zabe Bisa Amfani Da Addini
Bakon Marubuci

Ya Wajaba INEC Ta Hana Yakin Neman Zabe Bisa Amfani Da Addini

2 months ago
Next Post
An Yi Gwanjon Rigar Da Pele Ya Buga Kofin Duniya Na Karshe Da Ita

An Yi Gwanjon Rigar Da Pele Ya Buga Kofin Duniya Na Karshe Da Ita

LABARAI MASU NASABA

An Yanke Wa Wasu ‘Yan China 2 Hukuncin Daurin Shekaru 12 A Sakkwato

An Yanke Wa Wasu ‘Yan China 2 Hukuncin Daurin Shekaru 12 A Sakkwato

March 31, 2023
Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Irin Su Na Farko A Duniya

Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Irin Su Na Farko A Duniya

March 31, 2023
Zababben Gwamnan Katsina Ya Gana Da Buhari, Ya Ce Matsalar Tsaro Zai Fi Bai Wa Muhimmanci 

Zababben Gwamnan Katsina Ya Gana Da Buhari, Ya Ce Matsalar Tsaro Zai Fi Bai Wa Muhimmanci 

March 31, 2023
Kasar Sin Ta Bayar Da Shawarwari Dangane Da Yadda Za A Aiwatar Da Sanarwar Vienna Yadda Ya Kamata

Kasar Sin Ta Bayar Da Shawarwari Dangane Da Yadda Za A Aiwatar Da Sanarwar Vienna Yadda Ya Kamata

March 31, 2023
Mutum 14 Sun Shiga Hannun ‘Yan Sanda A Kano Kan Aikata Fashi Da Makami

Mutum 14 Sun Shiga Hannun ‘Yan Sanda A Kano Kan Aikata Fashi Da Makami

March 31, 2023
Ana Fatan A Hada Kai Wajen Shawo Kan Kalubalen Dake Addabar Duniya

Ana Fatan A Hada Kai Wajen Shawo Kan Kalubalen Dake Addabar Duniya

March 31, 2023
Ba Zan Tsoma Baki A Gwamnatin Abba Ba –Kwankwaso

Ba Zan Tsoma Baki A Gwamnatin Abba Ba –Kwankwaso

March 31, 2023
Taron Kolin Demokuradiyya Na Amurka Ya Shaidawa Duniya Ma’auni Biyu Da Amurka Ta Dauka Kan Batun Demokuradiyya

Taron Kolin Demokuradiyya Na Amurka Ya Shaidawa Duniya Ma’auni Biyu Da Amurka Ta Dauka Kan Batun Demokuradiyya

March 31, 2023
Har Yanzu Ni Ke Da Cikakken Iko A Matsayin Gwamnan Kano —Ganduje Ga Abba Gida-Gida

Har Yanzu Ni Ke Da Cikakken Iko A Matsayin Gwamnan Kano —Ganduje Ga Abba Gida-Gida

March 31, 2023
Boao: Kasar Sin Ta Karfafa Gwiwar Kasa Da Kasa

Boao: Kasar Sin Ta Karfafa Gwiwar Kasa Da Kasa

March 31, 2023
ADVERTISEMENT
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.