• English
  • Business News
Wednesday, August 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daga Kai Kuɗin Fansa ‘Yan Bindiga Sun Kashe Shi A Dajin Kachiya

by Abubakar Sulaiman
1 year ago
in Tsaro
0
Daga Kai Kuɗin Fansa ‘Yan Bindiga Sun Kashe Shi A Dajin Kachiya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Abdulkadir Abubakar, wani matashi ne mai jini a jika da ya kasance mai sanyin hali da sanin ya kamata wanda ya kammala Digirinsa na farko a Jami’ar Alqalam da ke Jihar Katsina a fannin kiwon lafiya.

Ya kasance abin so a cikin dangi saboda yadda yake da biyayya da haƙuri da kuma girmama na gaba da shi.

Sai dai kash! Ashe Allah bai yi shi mai tsawon kwana ba yayin da ya gamu da ajalinsa lokacin da yake ƙoƙarin taimakawa wajen ganin ‘yan bindiga sun sako wasu ‘yan uwansa maza da mata da aka yi garkuwa da su.

  • Hajjin Bana: Muna Alfahari Da Goyon Bayan Gwamnan Kaduna– Abubakar Yusuf
  • Jirgin Ƙasan Kaduna Zuwa Kano Zai Fara Aiki Farkon 2025 

Majiyarmu ta shaida mana cewa, wasu ‘yan bindiga sun yi dirar mikiya a wata ruga da ke wajen garin Jere a kan hanyar Abuja zuwa Kaduna, inda suka yi awon gaba da wasu magidanta da iyalansu zuwa dajin Kachiya da ke Kudancin Kaduna.

Saboda yadda aka yi amanna da sanyin halin ran Abdulkadir Abubakar wanda aka fi sani da Abba, sai aka nemi ya tattauna da ‘yan bindigar domin samun maslaha a kan yadda za a sako su.

Labarai Masu Nasaba

Harin Ƴan Bindiga Ya Yi Sanadin Kashe Ɗansanda Da Wasu Mutane 4 A Kwara

Edo Da Taraba : ‘Yansanda Sun Ceto Mutum 31 Da Aka Yi Garkuwa Da Su Bayan Musayar Wuta

Bayan ya tattauna da su an cimma matsaya, ana kamar babbar sallah saura sati uku, Abba tare da wasu mutum biyu suka tafi yankin Kachiya domin kai kuɗin fansa.

Majiyarmu wacce ta nemi a sakaya sunanta, ta ci gaba da cewa, “ana gobe za su tafi, a lokacin da Abba ya shiga wurin mahaifiyarsa don su yi sallama, ta ce masa, anya Abba!

Ko za ka haƙura da kai kuɗin fansar nan, ka bari wasu su kai, Abba ya ce mata Baba kar ki damu in sha Allahu babu abin da zai faru.

Ni idan na je ma zan tsaya a wurin mota ba zan shiga dajin ba. Ai kuwa ashe sallamar ƙarshe za su yi.

“Washe gari bayan sun isa wurin da ‘yan bindigar suka ce a kai kuɗin, sai suka tsaya, ‘yan bindigar suka kira waya suka ce Abba za a ba kuɗin ya kawo musu cikin daji.

“Abokan tafiyarsa suka ce Abba kar ka je, ya ce musu babu komai tun da ni suke so na kai musu kuɗin bari na je, sai ga wani mai mashin ya fito daga daji, suka ce masa ya hau.

“Ya hau sun fara tafiya kaɗan sai ga wani kuma ya sake fitowa daga daji ya hau baya suka sa Abba a tsakiya.

“To, baya sun isa can sai ‘yan bindigar suka sako mutum ɗaya daga cikin mutanen da suka sace. Aka tambayi wanda suka sako sai ya ce ai sun riƙe Abba.

“Haka aka dawo, wallahi duk jikinmu ya yi sanyi, ga shi ba su sako wadancan ba kuma sun riƙe Abba.”

Majiyar ta ƙara da cewa, bayan kudin fansar da aka kai musu fiye da Naura miliyan 10, sai suka ce a sake kai musu miliyan uku da babura huɗu sai su sako sauran mutanen tare da Abba.

“Washe garin sallah, an yi waya da su har suka ce a zo wa Abba da kaya masu kyau ya sa saboda na jikinsa duk sun lalace. Aka sake ɗaukar kudin aka kai musu. Waɗanda suka kai kudin sun jira su tun daga hantsi har zuwa la’asar ba su ga kowa ba, su kuma suna jin tsoron kar dare ya yi musu a daji sai suka dawo.

“Ana ganin motarsu ta dawo aka tarbe su da murna ana ga Abba ya dawo, ga Abba ya dawo. Sai da aka buɗe mota aka ga shiru babu Abba. Tun daga nan jikinmu ya ƙara sanyi, muka shiga fargaba.

“To, bayan sun sake kiran waya washegari shi ne suka ce a sake kawo musu kudi ko kuma su ma sauran su kashe su. Daga nan muka tabbatar da cewa lallai sun kashe Abba.

“Ashe ma sun riga sun kashe shi tun fiye da kwana 10 da suka wuce kuma suka jefa gawarsa a ruwa.

“Yanzu haka ma an riga an yi wa Abba salatul ga’ib wanda ake yi wa mutumin da ya mutu amma babu gawarsa a kusa. Wallahi muna cikin tashin hankali, ” in ji majiyar tamu.

Duk ƙoƙarin da muka yi don jin ta bakin jami’an tsaro dai abin ya faskara amma muna ci gaba da bibiyar Jami’in hulda da jama’a na Rundunar ‘Yansandan Kaduna.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BanditsKadunaKidnappersMurderTerroristTsaro
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Philippines Na Kara Hauka Kan Batun Tekun Kudancin Kasar Sin

Next Post

Alhajin Jihar Jigawa Ya Mayar Da Makudan Kudaden Da Ya Tsinta Ga Mai Shi A Makka

Related

Harin Ƴan Bindiga Ya Yi Sanadin Kashe Ɗansanda Da Wasu Mutane 4 A Kwara
Tsaro

Harin Ƴan Bindiga Ya Yi Sanadin Kashe Ɗansanda Da Wasu Mutane 4 A Kwara

3 days ago
An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa
Tsaro

Edo Da Taraba : ‘Yansanda Sun Ceto Mutum 31 Da Aka Yi Garkuwa Da Su Bayan Musayar Wuta

3 weeks ago
Kotu
Tsaro

NSCDC Ta Gurfanar Da Wanda Ake Zargi Da Badakalar Naira Miliyan 159

3 weeks ago
Fasakwauri: ‘Yansandan Indiya Sun Kama ‘Yar Nijeriya Da Kwayar Dala Miliyan 4
Tsaro

Fasakwauri: ‘Yansandan Indiya Sun Kama ‘Yar Nijeriya Da Kwayar Dala Miliyan 4

3 weeks ago
Babu Wata Sabuwar Ƙungiyar  Ƴan Ta’adda Mai Suna Fethulla A Nijeriya – DHQ
Tsaro

Babu Wata Sabuwar Ƙungiyar  Ƴan Ta’adda Mai Suna Fethulla A Nijeriya – DHQ

4 weeks ago
Sojoji Sun Kashe Kwamandan Ƙungiyar Haram/ISWAP Da Wasu 5 A Chadi
Labarai

Sojoji Sun Kashe Kwamandan Ƙungiyar Haram/ISWAP Da Wasu 5 A Chadi

4 weeks ago
Next Post
Alhajin Jihar Jigawa Ya Mayar Da Makudan Kudaden Da Ya Tsinta Ga Mai Shi A Makka

Alhajin Jihar Jigawa Ya Mayar Da Makudan Kudaden Da Ya Tsinta Ga Mai Shi A Makka

LABARAI MASU NASABA

Tinubu

Rangwame: Tinubu Ya Bada Umarnin Sake Bitar Tsarin Yadda Ake Karɓar Haraji 

August 13, 2025
Sashen Tattalin Arzikin Teku Na Sin Ya Bunkasa A Rabin Farko Na Bana

Sashen Tattalin Arzikin Teku Na Sin Ya Bunkasa A Rabin Farko Na Bana

August 13, 2025
Farfado Da Karkarar Sin: Canjin Gaisuwa Daga “Shin Ka Ci Abinci?” Zuwa “Yaya Rayuwarka A Gari?”

Farfado Da Karkarar Sin: Canjin Gaisuwa Daga “Shin Ka Ci Abinci?” Zuwa “Yaya Rayuwarka A Gari?”

August 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Kafa Sabbin Manyan Makarantu Na Tsawon Shekaru 7

Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Kafa Sabbin Manyan Makarantu Na Tsawon Shekaru 7

August 13, 2025
Aikin Hakar Kwal Ta Hanyar Amfani Da Fasahar Zamani Ya Fara Wuce 50% a Kasar Sin

Aikin Hakar Kwal Ta Hanyar Amfani Da Fasahar Zamani Ya Fara Wuce 50% a Kasar Sin

August 13, 2025
Majalisar Kano Na Shirin Zartar Da Dokar Gwajin Kwayoyin Jini, Kanjamau Da Cutar Hanta Kafin Aure

Majalisar Kano Ta Dakatar Da Shugaban Karamar Hukuma Bisa Zargin Kara Farashin Takin Gwamnati

August 13, 2025
PLA Ta Kori Jirgin Ruwan Yakin Amurka Daga Yankin Ruwan Kasar Sin A Kusa Da Huangyan Dao

PLA Ta Kori Jirgin Ruwan Yakin Amurka Daga Yankin Ruwan Kasar Sin A Kusa Da Huangyan Dao

August 13, 2025
NDLEA Ta Kama Dilolin Ƙwaya 49 A Kano

NDLEA Ta Kama Dilolin Ƙwaya 49 A Kano

August 13, 2025
Za Mu Nome Dazuka Don Magance Matsalar Tsaro A Neja – Bago

Gwamnatin Neja Ta Tabbatar Da Kama Hatsabibin Ɗan Bindiga, Abubakar Abba

August 13, 2025
ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi

ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi

August 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.