ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daga Kai Kuɗin Fansa ‘Yan Bindiga Sun Kashe Shi A Dajin Kachiya

by Abubakar Sulaiman
2 years ago
Bindiga

Abdulkadir Abubakar, wani matashi ne mai jini a jika da ya kasance mai sanyin hali da sanin ya kamata wanda ya kammala Digirinsa na farko a Jami’ar Alqalam da ke Jihar Katsina a fannin kiwon lafiya.

Ya kasance abin so a cikin dangi saboda yadda yake da biyayya da haƙuri da kuma girmama na gaba da shi.

Sai dai kash! Ashe Allah bai yi shi mai tsawon kwana ba yayin da ya gamu da ajalinsa lokacin da yake ƙoƙarin taimakawa wajen ganin ‘yan bindiga sun sako wasu ‘yan uwansa maza da mata da aka yi garkuwa da su.

ADVERTISEMENT
  • Hajjin Bana: Muna Alfahari Da Goyon Bayan Gwamnan Kaduna– Abubakar Yusuf
  • Jirgin Ƙasan Kaduna Zuwa Kano Zai Fara Aiki Farkon 2025 

Majiyarmu ta shaida mana cewa, wasu ‘yan bindiga sun yi dirar mikiya a wata ruga da ke wajen garin Jere a kan hanyar Abuja zuwa Kaduna, inda suka yi awon gaba da wasu magidanta da iyalansu zuwa dajin Kachiya da ke Kudancin Kaduna.

Saboda yadda aka yi amanna da sanyin halin ran Abdulkadir Abubakar wanda aka fi sani da Abba, sai aka nemi ya tattauna da ‘yan bindigar domin samun maslaha a kan yadda za a sako su.

LABARAI MASU NASABA

NDLEA Ta Cafke Ƴar Shekara 67 Da Hodar Iblis Da Aka Ɓoye A Cikin Ayaba

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’

Bayan ya tattauna da su an cimma matsaya, ana kamar babbar sallah saura sati uku, Abba tare da wasu mutum biyu suka tafi yankin Kachiya domin kai kuɗin fansa.

Majiyarmu wacce ta nemi a sakaya sunanta, ta ci gaba da cewa, “ana gobe za su tafi, a lokacin da Abba ya shiga wurin mahaifiyarsa don su yi sallama, ta ce masa, anya Abba!

Ko za ka haƙura da kai kuɗin fansar nan, ka bari wasu su kai, Abba ya ce mata Baba kar ki damu in sha Allahu babu abin da zai faru.

Ni idan na je ma zan tsaya a wurin mota ba zan shiga dajin ba. Ai kuwa ashe sallamar ƙarshe za su yi.

“Washe gari bayan sun isa wurin da ‘yan bindigar suka ce a kai kuɗin, sai suka tsaya, ‘yan bindigar suka kira waya suka ce Abba za a ba kuɗin ya kawo musu cikin daji.

“Abokan tafiyarsa suka ce Abba kar ka je, ya ce musu babu komai tun da ni suke so na kai musu kuɗin bari na je, sai ga wani mai mashin ya fito daga daji, suka ce masa ya hau.

“Ya hau sun fara tafiya kaɗan sai ga wani kuma ya sake fitowa daga daji ya hau baya suka sa Abba a tsakiya.

“To, baya sun isa can sai ‘yan bindigar suka sako mutum ɗaya daga cikin mutanen da suka sace. Aka tambayi wanda suka sako sai ya ce ai sun riƙe Abba.

“Haka aka dawo, wallahi duk jikinmu ya yi sanyi, ga shi ba su sako wadancan ba kuma sun riƙe Abba.”

Majiyar ta ƙara da cewa, bayan kudin fansar da aka kai musu fiye da Naura miliyan 10, sai suka ce a sake kai musu miliyan uku da babura huɗu sai su sako sauran mutanen tare da Abba.

“Washe garin sallah, an yi waya da su har suka ce a zo wa Abba da kaya masu kyau ya sa saboda na jikinsa duk sun lalace. Aka sake ɗaukar kudin aka kai musu. Waɗanda suka kai kudin sun jira su tun daga hantsi har zuwa la’asar ba su ga kowa ba, su kuma suna jin tsoron kar dare ya yi musu a daji sai suka dawo.

“Ana ganin motarsu ta dawo aka tarbe su da murna ana ga Abba ya dawo, ga Abba ya dawo. Sai da aka buɗe mota aka ga shiru babu Abba. Tun daga nan jikinmu ya ƙara sanyi, muka shiga fargaba.

“To, bayan sun sake kiran waya washegari shi ne suka ce a sake kawo musu kudi ko kuma su ma sauran su kashe su. Daga nan muka tabbatar da cewa lallai sun kashe Abba.

“Ashe ma sun riga sun kashe shi tun fiye da kwana 10 da suka wuce kuma suka jefa gawarsa a ruwa.

“Yanzu haka ma an riga an yi wa Abba salatul ga’ib wanda ake yi wa mutumin da ya mutu amma babu gawarsa a kusa. Wallahi muna cikin tashin hankali, ” in ji majiyar tamu.

Duk ƙoƙarin da muka yi don jin ta bakin jami’an tsaro dai abin ya faskara amma muna ci gaba da bibiyar Jami’in hulda da jama’a na Rundunar ‘Yansandan Kaduna.

Bindiga
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Iyalin El-Rufai Sun Bai Ministan Tsaro Wa’adin Kwana 7 Kan Zargin Rikicin Kudancin Kaduna
  • Abubakar Sulaiman
    Atiku Ya Zargi Gwamnatin Tarayya Da Cin Bashi Kamar Mashayin Da Kuɗi Ya Ƙarewa
  • Abubakar Sulaiman
    Boko Haram Ta Kai Hari Adamawa, Ana Fargabar Mutuwar Mutane 11
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Sokoto, Sun Kashe Mutane 7, Sun Yi Garkuwa Da 12

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Tsaro

NDLEA Ta Cafke Ƴar Shekara 67 Da Hodar Iblis Da Aka Ɓoye A Cikin Ayaba

July 11, 2026
Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’
Tsaro

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’

July 9, 2026
Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara
Tsaro

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Next Post
Alhajin Jihar Jigawa Ya Mayar Da Makudan Kudaden Da Ya Tsinta Ga Mai Shi A Makka

Alhajin Jihar Jigawa Ya Mayar Da Makudan Kudaden Da Ya Tsinta Ga Mai Shi A Makka

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.