ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daga Kai Kuɗin Fansa ‘Yan Bindiga Sun Kashe Shi A Dajin Kachiya

by Abubakar Sulaiman
2 years ago
Bindiga

Abdulkadir Abubakar, wani matashi ne mai jini a jika da ya kasance mai sanyin hali da sanin ya kamata wanda ya kammala Digirinsa na farko a Jami’ar Alqalam da ke Jihar Katsina a fannin kiwon lafiya.

Ya kasance abin so a cikin dangi saboda yadda yake da biyayya da haƙuri da kuma girmama na gaba da shi.

Sai dai kash! Ashe Allah bai yi shi mai tsawon kwana ba yayin da ya gamu da ajalinsa lokacin da yake ƙoƙarin taimakawa wajen ganin ‘yan bindiga sun sako wasu ‘yan uwansa maza da mata da aka yi garkuwa da su.

ADVERTISEMENT
  • Hajjin Bana: Muna Alfahari Da Goyon Bayan Gwamnan Kaduna– Abubakar Yusuf
  • Jirgin Ƙasan Kaduna Zuwa Kano Zai Fara Aiki Farkon 2025 

Majiyarmu ta shaida mana cewa, wasu ‘yan bindiga sun yi dirar mikiya a wata ruga da ke wajen garin Jere a kan hanyar Abuja zuwa Kaduna, inda suka yi awon gaba da wasu magidanta da iyalansu zuwa dajin Kachiya da ke Kudancin Kaduna.

Saboda yadda aka yi amanna da sanyin halin ran Abdulkadir Abubakar wanda aka fi sani da Abba, sai aka nemi ya tattauna da ‘yan bindigar domin samun maslaha a kan yadda za a sako su.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi

Bayan ya tattauna da su an cimma matsaya, ana kamar babbar sallah saura sati uku, Abba tare da wasu mutum biyu suka tafi yankin Kachiya domin kai kuɗin fansa.

Majiyarmu wacce ta nemi a sakaya sunanta, ta ci gaba da cewa, “ana gobe za su tafi, a lokacin da Abba ya shiga wurin mahaifiyarsa don su yi sallama, ta ce masa, anya Abba!

Ko za ka haƙura da kai kuɗin fansar nan, ka bari wasu su kai, Abba ya ce mata Baba kar ki damu in sha Allahu babu abin da zai faru.

Ni idan na je ma zan tsaya a wurin mota ba zan shiga dajin ba. Ai kuwa ashe sallamar ƙarshe za su yi.

“Washe gari bayan sun isa wurin da ‘yan bindigar suka ce a kai kuɗin, sai suka tsaya, ‘yan bindigar suka kira waya suka ce Abba za a ba kuɗin ya kawo musu cikin daji.

“Abokan tafiyarsa suka ce Abba kar ka je, ya ce musu babu komai tun da ni suke so na kai musu kuɗin bari na je, sai ga wani mai mashin ya fito daga daji, suka ce masa ya hau.

“Ya hau sun fara tafiya kaɗan sai ga wani kuma ya sake fitowa daga daji ya hau baya suka sa Abba a tsakiya.

“To, baya sun isa can sai ‘yan bindigar suka sako mutum ɗaya daga cikin mutanen da suka sace. Aka tambayi wanda suka sako sai ya ce ai sun riƙe Abba.

“Haka aka dawo, wallahi duk jikinmu ya yi sanyi, ga shi ba su sako wadancan ba kuma sun riƙe Abba.”

Majiyar ta ƙara da cewa, bayan kudin fansar da aka kai musu fiye da Naura miliyan 10, sai suka ce a sake kai musu miliyan uku da babura huɗu sai su sako sauran mutanen tare da Abba.

“Washe garin sallah, an yi waya da su har suka ce a zo wa Abba da kaya masu kyau ya sa saboda na jikinsa duk sun lalace. Aka sake ɗaukar kudin aka kai musu. Waɗanda suka kai kudin sun jira su tun daga hantsi har zuwa la’asar ba su ga kowa ba, su kuma suna jin tsoron kar dare ya yi musu a daji sai suka dawo.

“Ana ganin motarsu ta dawo aka tarbe su da murna ana ga Abba ya dawo, ga Abba ya dawo. Sai da aka buɗe mota aka ga shiru babu Abba. Tun daga nan jikinmu ya ƙara sanyi, muka shiga fargaba.

“To, bayan sun sake kiran waya washegari shi ne suka ce a sake kawo musu kudi ko kuma su ma sauran su kashe su. Daga nan muka tabbatar da cewa lallai sun kashe Abba.

“Ashe ma sun riga sun kashe shi tun fiye da kwana 10 da suka wuce kuma suka jefa gawarsa a ruwa.

“Yanzu haka ma an riga an yi wa Abba salatul ga’ib wanda ake yi wa mutumin da ya mutu amma babu gawarsa a kusa. Wallahi muna cikin tashin hankali, ” in ji majiyar tamu.

Duk ƙoƙarin da muka yi don jin ta bakin jami’an tsaro dai abin ya faskara amma muna ci gaba da bibiyar Jami’in hulda da jama’a na Rundunar ‘Yansandan Kaduna.

Bindiga
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Mutane 15 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsarin Mota, 17 Sun Jikkata
  • Abubakar Sulaiman
    Hukuncin Kisa Ne Ya Dace Da Ƴan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Gagdi
  • Abubakar Sulaiman
    Kotu Ta Ɗage Shari’ar Kwace Kadarori 57 Na Tsohon Minista Malami
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kashe Manoma 9, Sun Sace Da Dama A Birnin Gwari

MASU ALAKA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara
Tsaro

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi
Tsaro

Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi

June 21, 2026
Ƴan Bindiga Sun Kashe Hakimin Gundumar Gwande A Jihar Filato
Tsaro

Ƴan Bindiga Sun Kashe Hakimin Gundumar Gwande A Jihar Filato

June 19, 2026
Next Post
Alhajin Jihar Jigawa Ya Mayar Da Makudan Kudaden Da Ya Tsinta Ga Mai Shi A Makka

Alhajin Jihar Jigawa Ya Mayar Da Makudan Kudaden Da Ya Tsinta Ga Mai Shi A Makka

LABARAI MASU NASABA

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

July 6, 2026
Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

July 6, 2026
Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

July 6, 2026
Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

July 6, 2026
FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

July 6, 2026
Shugabannin Sin Da Madagascar Sun Yi Musayar Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 20 Da Kulla Alakar Diflomasiyya Tsakaninsu

Shugabannin Sin Da Madagascar Sun Yi Musayar Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 20 Da Kulla Alakar Diflomasiyya Tsakaninsu

July 6, 2026
Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

July 6, 2026
Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

July 6, 2026
ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

July 6, 2026
Rundunar Sojin Ruwan Sin Ta Yi Gwajin Makami Mai Linzami Ta Amfani Da Jirgin Ruwa Mai Nutso

Rundunar Sojin Ruwan Sin Ta Yi Gwajin Makami Mai Linzami Ta Amfani Da Jirgin Ruwa Mai Nutso

July 6, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.