An fara babbar jarrabawar kammala sakandare, watau jarrabawar neman shiga jami’a ta kasar Sin da aka fi sani da Gaokao.
A cewar ma’aikatar ilimi ta kasar, jimillar dalibai miliyan 13.35 ne ake sa ran za su rubuta jarrabawar a bana.
- Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu
- Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2
Yayin rangadin da ya yi a makarantar midil ta Taiyuan dake lardin Shanxi na arewacin kasar Sin, mataimakin firaministan Sin Ding Xuexiang, ya nanata bukatar tsare adalci da tabbatar da tsaro yayin jarrabawar ta kasa.
Ding Xuexiang wanda kuma mamba ne na kwamitin dindindin na ofishin siyasa na kwamitin kolin JKS ya kara da cewa, jarrabawar na da muhimmanci ga ayyukan raya kasa da makomar iyalai.
Ya kuma bukaci hukumomi su daukaka adalci a matsayin kashin bayan jarrabawar da na samun gurbin karatu da tsarin jarrabawar ta Gaokao. Yana mai bayyana muhimmancin tabbatar da matakan tsaro yayin jarrabawar da matakan yaki da magudin jarrabawa da ma ba dalibai goyon baya. (Fa’iza Mustapha)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp