Rundunar ‘yan sandan Jihar Osun ta ce wani dalibin Kwalejin Fasahar Ipetu-Ijesa mai suna Olonade Tomiwa mai shekaru 19 ya kashe kansa a garin Ilesa.
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, SP Yemisi Opalola, ya fitar a Osogbo.
Opalola ya ce an samu mamacin yana rataye a harabar gidan da wayar tarho.
Ta ce an kai rahoton lamarin ne a sashen Ilesa ‘A’, daga hannun wani Agboola Olusola, shugaban matasa a garin.
Kakakin rundunar ‘yan sandan ya ce ba a samu wani rauni a jikin gawar marigayin ba lokacin da ‘yan sanda suka ziyarci wurin da lamarin ya faru.
Opalola ya ce ‘yan sanda sun dauki hotunan inda lamarin ya faru tare da ajiye gawar a dakin ajiye gawa na asibitin Wesley Guild da ke Ilesa.
Ta ce an fara bincike kan lamarin.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp