ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ambaliyar Ruwa: Majalisar Kano Ta Nemi Taimakon Gwamnatin Tarayya

by Sadiq
4 years ago
Ambaliyar Ruwa

Majalisar Dokokin Jihar Kano ta yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta kai dauki ga al’ummar da ambaliyar ruwa ta shafa a jihar.

‘Yan majalisar sun yi wannan kiran ne a zaman da suka yi a ranar Litinin, wanda shugaban majalisar, Hamisu Chidari ya jagoranta.

  • Bikin Tsakiyar Kaka Na 2022 Da CMG Ya Nuna Ya Samu Yabo Sosai Daga Masu Kallo A Gida Da Waje
  • Kashi 78 Na Dalibai Sun Ci Jarrabawar NBAIS Ta 2022 – Farfesa Shafi’u

Majalisar ta yi wannan kiran ne bayan gabatar da kudiri kan al’amuran hadin gwiwa da suka shafi rayuwar jama’a cikin gaggawa da ‘yan mazabar Kiru, Bebeji da Rano suka gabatar.

ADVERTISEMENT

Mataimakin shugaban majalisar kuma dan majalisa mai wakiltar mazabar Kiru, Kabiru Dashi ne, ya gabatar wa da majalisar.

‘Yan majalisar sun kuma bukaci gwamnatin jihar da ta yi kira ga hukumar raya kogin Hadejia da Jama’are da gwamnatin tarayya da su gaggauta magance kwararar ruwa daga madatsar ruwa ta Tiga.

LABARAI MASU NASABA

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

A cewarsu, yin hakan zai kawo karshen matsalar ambaliyar ruwa da asarar rayuka da dukiyoyi a yankin.

‘Yan majalisar sun bayyana lamarin a matsayin abin takaici da bakin ciki, yayin da suka kuma yi kira ga gwamnatin jihar Kano da gwamnatin tarayya da su kawo dauki ga al’umma.

Bayan tattaunawa ne majalisar ta amince da kudirorin, inda ta jajanta wa al’ummar da abin ya shafa tare da addu’ar Allah ya kare afkuwar wannan lamari.

Kamfanin Dillancin Labaran Nijeriya (NAN), ya ruwaito cewa ambaliyar ruwa ta Tiga a makon jiya ta yi barna tare da lalata gonaki da tituna da gidaje da kuma raba mazauna yankunan da muhallansu.

A halin da ake ciki, majalisar ta samu takarda daga gwamnan jihar, Abdullahi Ganduje na neman amincewar nadin shugaban majalisar tare da sake nada wasu mutane biyar na kwamitin gyaran doka na jihar.

Hukumar Gyaran Shari’a ta kunshi Mai Shari’a Lawan Wada mai ritaya a matsayin shugaba, sai Sadiq Garba, Muhd, Aliyu, Yahaya Rimi, Dakta Muhammad Minjibir, Garzali Zubairu da Hauwa Yusuf a matsayin mambobi.

Wasikar dai an mika ta ne ga kwamitin shari’a na majalisar kuma an ba shi mako guda ya ba da rahoto don ci gaba da ayyukan majalisa.

MASU ALAKA

Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi
Manyan Labarai

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

September 8, 2026
Next Post
Takaddama Kan Shirin Daukar Sabbin ‘Yansanda

'Yan Bindiga Sun Sace Fasto A Filato

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.