ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ambaliyar Ruwa: Majalisar Kano Ta Nemi Taimakon Gwamnatin Tarayya

by Sadiq
4 years ago
Ambaliyar Ruwa

Majalisar Dokokin Jihar Kano ta yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta kai dauki ga al’ummar da ambaliyar ruwa ta shafa a jihar.

‘Yan majalisar sun yi wannan kiran ne a zaman da suka yi a ranar Litinin, wanda shugaban majalisar, Hamisu Chidari ya jagoranta.

  • Bikin Tsakiyar Kaka Na 2022 Da CMG Ya Nuna Ya Samu Yabo Sosai Daga Masu Kallo A Gida Da Waje
  • Kashi 78 Na Dalibai Sun Ci Jarrabawar NBAIS Ta 2022 – Farfesa Shafi’u

Majalisar ta yi wannan kiran ne bayan gabatar da kudiri kan al’amuran hadin gwiwa da suka shafi rayuwar jama’a cikin gaggawa da ‘yan mazabar Kiru, Bebeji da Rano suka gabatar.

ADVERTISEMENT

Mataimakin shugaban majalisar kuma dan majalisa mai wakiltar mazabar Kiru, Kabiru Dashi ne, ya gabatar wa da majalisar.

‘Yan majalisar sun kuma bukaci gwamnatin jihar da ta yi kira ga hukumar raya kogin Hadejia da Jama’are da gwamnatin tarayya da su gaggauta magance kwararar ruwa daga madatsar ruwa ta Tiga.

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

A cewarsu, yin hakan zai kawo karshen matsalar ambaliyar ruwa da asarar rayuka da dukiyoyi a yankin.

‘Yan majalisar sun bayyana lamarin a matsayin abin takaici da bakin ciki, yayin da suka kuma yi kira ga gwamnatin jihar Kano da gwamnatin tarayya da su kawo dauki ga al’umma.

Bayan tattaunawa ne majalisar ta amince da kudirorin, inda ta jajanta wa al’ummar da abin ya shafa tare da addu’ar Allah ya kare afkuwar wannan lamari.

Kamfanin Dillancin Labaran Nijeriya (NAN), ya ruwaito cewa ambaliyar ruwa ta Tiga a makon jiya ta yi barna tare da lalata gonaki da tituna da gidaje da kuma raba mazauna yankunan da muhallansu.

A halin da ake ciki, majalisar ta samu takarda daga gwamnan jihar, Abdullahi Ganduje na neman amincewar nadin shugaban majalisar tare da sake nada wasu mutane biyar na kwamitin gyaran doka na jihar.

Hukumar Gyaran Shari’a ta kunshi Mai Shari’a Lawan Wada mai ritaya a matsayin shugaba, sai Sadiq Garba, Muhd, Aliyu, Yahaya Rimi, Dakta Muhammad Minjibir, Garzali Zubairu da Hauwa Yusuf a matsayin mambobi.

Wasikar dai an mika ta ne ga kwamitin shari’a na majalisar kuma an ba shi mako guda ya ba da rahoto don ci gaba da ayyukan majalisa.

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Next Post
Takaddama Kan Shirin Daukar Sabbin ‘Yansanda

'Yan Bindiga Sun Sace Fasto A Filato

LABARAI MASU NASABA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.