ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, November 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilan Karancin Kajin Gidan Gona A Nijeriya

by Abubakar Abba
2 years ago
Kaji

Kungiyar masu kiwon kajin gidan gona ta kasa, reshen babban birnin tarayyar Abuja (PAN), ta yi kira ga Gwamnatin Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu, ya gaggauta kawo dauki, musamman wajen yawan samun hauhawar farashin abincin da ake ciyar da kajin gidan gona.

Kazalika, ta yi gargadin cewa, idan har ba a dauki matakin da ya kamata ba, ko shakka babu wannan fanni na kiwon kaji zai nakasu ta hanyar durkushewa baki-daya.

  • Tsadar Magunguna Na Barazana Ga Rayukan Majinyata A Nijeriya
  • Gwamatin Tarayya Ta Fito Da Tsarin Cin Gajiyar Ma’adanan da Ke Jihar Nasarawa

Sakataren kungiyar, Hakeem Musa ne ya yi wannan kira a babban birnin tarayya Abuja, inda ya nuna matukar damuwarsa a kan yadda ake ci gaba da fuskantar wannan hauhawar farashi na abincin kaji a daidai wannan lokaci.

ADVERTISEMENT

Har ila yau, Musa ya yi nuni da cewa, ya kamata gwamnatin ta taikama musu a wannan sana’a tasu kiwon kaji na gidan gona, domin samun damar tsayuwa da kafafunsu.

Sakataren ya kuma buga misali da cewa, buhun abincin kajin mai dauyin kilo 25, a watan Nuwambar da ya gabata, an sayar da shi kan Naira 8,000, wanda daga baya kuma farashin budun ya karu zuwa Naira 9,100.

LABARAI MASU NASABA

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

Ya ci gaba da cewa, a makon farko na  watan  Disambar da ya gabata, farashin budun ya karu zuwa Naira 9,350 daga bisani kuma a makon farko farashin ya kai Naira 9,550, wanda kuma a mako na uku farashin ya karu zuwa Naira  10,950.

Hakeem ya kara da cewa, babu wanda ke da masaniyar lokacin da wannan farashi na abincin kaji zai daina yin tashin gwaron zabi.

Sai dai, sakataren ya bayyana fatan cewa, Gwamnatin Tinubu za ta mayar da hankali wajen bunkasa wannan fanni da kuma samar musu da tallafi .

A cewar tasa, mun fi bukatar a samar mana da tallafin kudi, domin ci gaba da tafiyar da wannan sana’a tamu.

Sannan kuma ya danganta wannan karanci na kaji a kan matsalar hauhawar farashin abincin kajin, musamman masara da waken suya, wadanda ake amfani da su wajen hadawa tare da sarrafa abincin kajin.

A karshe, Sakataren ya bayyana cewa, hauhawar farashin abincin kajin, na matukar haifar wa masu wannan sana’a nakasu, wanda hakan ne ke jawo wa wasunsu suke dakatar da yin sana’ar baki-daya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Noma Da Kiwo

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi
Noma Da Kiwo

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci
Noma Da Kiwo

Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci

November 2, 2025
Next Post
An Rantsar Da Ododo A Matsayin Gwamnan Kogi

An Rantsar Da Ododo A Matsayin Gwamnan Kogi

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 3 Tare Da Sace Babur A Nasarawa

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 3 Tare Da Sace Babur A Nasarawa

November 12, 2025
‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi Sama Da 200 A Katsina

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi Sama Da 200 A Katsina

November 12, 2025
Injiniya Sagir Ibrahim Ƙoƙi Ya Fice Daga Jam’iyyar NNPP

Injiniya Sagir Ibrahim Ƙoƙi Ya Fice Daga Jam’iyyar NNPP

November 12, 2025
Bayanan Da Muka Samu Sun Nuna An Fara Samun Tsaro A Nijeriya – Hafsan Sojin Ƙasa

Bayanan Da Muka Samu Sun Nuna An Fara Samun Tsaro A Nijeriya – Hafsan Sojin Ƙasa

November 12, 2025
Yadda Ɓarawo Ya Shiga Gidan Gwamnatin Kano Ya Saci Motar Ayarin Mataimakin Gwamna

Yadda Ɓarawo Ya Shiga Gidan Gwamnatin Kano Ya Saci Motar Ayarin Mataimakin Gwamna

November 12, 2025
Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba

Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba

November 12, 2025
Coas

Bayan Ganawa Da Tinubu, COAS Ya Tabbatar Wa ‘Yan Nijeriya Samun Ingantaccen Tsaro

November 11, 2025
Sin: Amurka Ba Ta Sa Lura Ga Kare Hakkin Dan Adam

Sin: Amurka Ba Ta Sa Lura Ga Kare Hakkin Dan Adam

November 11, 2025
Bikin CIIE Ya Nuna Yadda Sin Ke Ba Da Jagora Kan Harkokin Bude Kofa

Bikin CIIE Ya Nuna Yadda Sin Ke Ba Da Jagora Kan Harkokin Bude Kofa

November 11, 2025
Za Mu Ci Gaba Da Tallafa Wa ’Yansanda Domin Inganta Ayyukan Su A Zamfara – Gwamna Lawal

Za Mu Ci Gaba Da Tallafa Wa ’Yansanda Domin Inganta Ayyukan Su A Zamfara – Gwamna Lawal

November 11, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.