ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, November 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilan Karancin Kajin Gidan Gona A Nijeriya

by Abubakar Abba
2 years ago
Kaji

Kungiyar masu kiwon kajin gidan gona ta kasa, reshen babban birnin tarayyar Abuja (PAN), ta yi kira ga Gwamnatin Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu, ya gaggauta kawo dauki, musamman wajen yawan samun hauhawar farashin abincin da ake ciyar da kajin gidan gona.

Kazalika, ta yi gargadin cewa, idan har ba a dauki matakin da ya kamata ba, ko shakka babu wannan fanni na kiwon kaji zai nakasu ta hanyar durkushewa baki-daya.

  • Tsadar Magunguna Na Barazana Ga Rayukan Majinyata A Nijeriya
  • Gwamatin Tarayya Ta Fito Da Tsarin Cin Gajiyar Ma’adanan da Ke Jihar Nasarawa

Sakataren kungiyar, Hakeem Musa ne ya yi wannan kira a babban birnin tarayya Abuja, inda ya nuna matukar damuwarsa a kan yadda ake ci gaba da fuskantar wannan hauhawar farashi na abincin kaji a daidai wannan lokaci.

ADVERTISEMENT

Har ila yau, Musa ya yi nuni da cewa, ya kamata gwamnatin ta taikama musu a wannan sana’a tasu kiwon kaji na gidan gona, domin samun damar tsayuwa da kafafunsu.

Sakataren ya kuma buga misali da cewa, buhun abincin kajin mai dauyin kilo 25, a watan Nuwambar da ya gabata, an sayar da shi kan Naira 8,000, wanda daga baya kuma farashin budun ya karu zuwa Naira 9,100.

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

Dalilin Asusun NADF Na Yin Hadaka Da Gwamnatin Jihar Jigawa

Ya ci gaba da cewa, a makon farko na  watan  Disambar da ya gabata, farashin budun ya karu zuwa Naira 9,350 daga bisani kuma a makon farko farashin ya kai Naira 9,550, wanda kuma a mako na uku farashin ya karu zuwa Naira  10,950.

Hakeem ya kara da cewa, babu wanda ke da masaniyar lokacin da wannan farashi na abincin kaji zai daina yin tashin gwaron zabi.

Sai dai, sakataren ya bayyana fatan cewa, Gwamnatin Tinubu za ta mayar da hankali wajen bunkasa wannan fanni da kuma samar musu da tallafi .

A cewar tasa, mun fi bukatar a samar mana da tallafin kudi, domin ci gaba da tafiyar da wannan sana’a tamu.

Sannan kuma ya danganta wannan karanci na kaji a kan matsalar hauhawar farashin abincin kajin, musamman masara da waken suya, wadanda ake amfani da su wajen hadawa tare da sarrafa abincin kajin.

A karshe, Sakataren ya bayyana cewa, hauhawar farashin abincin kajin, na matukar haifar wa masu wannan sana’a nakasu, wanda hakan ne ke jawo wa wasunsu suke dakatar da yin sana’ar baki-daya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani
Noma Da Kiwo

Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

November 14, 2025
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Dalilin Asusun NADF Na Yin Hadaka Da Gwamnatin Jihar Jigawa

November 14, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Noma Da Kiwo

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
Next Post
An Rantsar Da Ododo A Matsayin Gwamnan Kogi

An Rantsar Da Ododo A Matsayin Gwamnan Kogi

LABARAI MASU NASABA

Wakilai Daga Jihohi 19 Sun Isa Ibadan Don Taron PDP Na Ƙasa

Wakilai Daga Jihohi 19 Sun Isa Ibadan Don Taron PDP Na Ƙasa

November 15, 2025
Daliban FUTA 240 Sun Samu Digiri Mai Daraja Ta Daya

Daliban FUTA 240 Sun Samu Digiri Mai Daraja Ta Daya

November 15, 2025
Shakirat Ta Tsallaka Mataki Na Ƙarshe Na Zama Gwarzuwar Ƴar Wasan Afrika

Shakirat Ta Tsallaka Mataki Na Ƙarshe Na Zama Gwarzuwar Ƴar Wasan Afrika

November 15, 2025
Wasu Mahara Sun Kashe Mata 2, Tare Da da Ƙona Gidansu A Tudun Yola

Wasu Mahara Sun Kashe Mata 2, Tare Da da Ƙona Gidansu A Tudun Yola

November 15, 2025
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje

November 15, 2025
Fashi Da Makami: An Yanke Wa ’Yan Nijeriya Hudu Mazauna Birtaniya Hukuncin Daurin Shekara 55 A Gidan Yari

Fashi Da Makami: An Yanke Wa ’Yan Nijeriya Hudu Mazauna Birtaniya Hukuncin Daurin Shekara 55 A Gidan Yari

November 15, 2025
Shugaban APC Na Kano Ya Nemi Afuwa Daga Al’ummar Fagge Kan Kalamansa

Shugaban APC Na Kano Ya Nemi Afuwa Daga Al’ummar Fagge Kan Kalamansa

November 15, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Cafke Wani Da Ake Zargin Dan Ta’adda Ne A Jihar Kebbi

November 15, 2025
Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

November 14, 2025
NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

November 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.