• English
  • Business News
Friday, July 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilan Karancin Kajin Gidan Gona A Nijeriya

by Abubakar Abba
1 year ago
in Noma Da Kiwo
0
Dalilan Karancin Kajin Gidan Gona A Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar masu kiwon kajin gidan gona ta kasa, reshen babban birnin tarayyar Abuja (PAN), ta yi kira ga Gwamnatin Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu, ya gaggauta kawo dauki, musamman wajen yawan samun hauhawar farashin abincin da ake ciyar da kajin gidan gona.

Kazalika, ta yi gargadin cewa, idan har ba a dauki matakin da ya kamata ba, ko shakka babu wannan fanni na kiwon kaji zai nakasu ta hanyar durkushewa baki-daya.

  • Tsadar Magunguna Na Barazana Ga Rayukan Majinyata A Nijeriya
  • Gwamatin Tarayya Ta Fito Da Tsarin Cin Gajiyar Ma’adanan da Ke Jihar Nasarawa

Sakataren kungiyar, Hakeem Musa ne ya yi wannan kira a babban birnin tarayya Abuja, inda ya nuna matukar damuwarsa a kan yadda ake ci gaba da fuskantar wannan hauhawar farashi na abincin kaji a daidai wannan lokaci.

Har ila yau, Musa ya yi nuni da cewa, ya kamata gwamnatin ta taikama musu a wannan sana’a tasu kiwon kaji na gidan gona, domin samun damar tsayuwa da kafafunsu.

Sakataren ya kuma buga misali da cewa, buhun abincin kajin mai dauyin kilo 25, a watan Nuwambar da ya gabata, an sayar da shi kan Naira 8,000, wanda daga baya kuma farashin budun ya karu zuwa Naira 9,100.

Labarai Masu Nasaba

Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Yin Hadaka Da Jihar Nasarawa Don Bunkasa Noma

Nijeriya Za Ta Rika Samun Naira Tiriliyan Uku A Aikin Tatsar Rogo Duk Shekara – Kashim

Ya ci gaba da cewa, a makon farko na  watan  Disambar da ya gabata, farashin budun ya karu zuwa Naira 9,350 daga bisani kuma a makon farko farashin ya kai Naira 9,550, wanda kuma a mako na uku farashin ya karu zuwa Naira  10,950.

Hakeem ya kara da cewa, babu wanda ke da masaniyar lokacin da wannan farashi na abincin kaji zai daina yin tashin gwaron zabi.

Sai dai, sakataren ya bayyana fatan cewa, Gwamnatin Tinubu za ta mayar da hankali wajen bunkasa wannan fanni da kuma samar musu da tallafi .

A cewar tasa, mun fi bukatar a samar mana da tallafin kudi, domin ci gaba da tafiyar da wannan sana’a tamu.

Sannan kuma ya danganta wannan karanci na kaji a kan matsalar hauhawar farashin abincin kajin, musamman masara da waken suya, wadanda ake amfani da su wajen hadawa tare da sarrafa abincin kajin.

A karshe, Sakataren ya bayyana cewa, hauhawar farashin abincin kajin, na matukar haifar wa masu wannan sana’a nakasu, wanda hakan ne ke jawo wa wasunsu suke dakatar da yin sana’ar baki-daya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Dabarun Kiwon Zomo A Saukake

Next Post

An Rantsar Da Ododo A Matsayin Gwamnan Kogi

Related

Abinci
Noma Da Kiwo

Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Yin Hadaka Da Jihar Nasarawa Don Bunkasa Noma

6 days ago
Shettima
Noma Da Kiwo

Nijeriya Za Ta Rika Samun Naira Tiriliyan Uku A Aikin Tatsar Rogo Duk Shekara – Kashim

6 days ago
Wa’adin Da Tinubu Ya Bai Wa Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Ya Cika
Noma Da Kiwo

Dalilin Ware Naira Biliyan 19.5 Da Asusun Bunkasa Aikin Noma Ya Yi

2 weeks ago
Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

2 weeks ago
Dalilin Kwararru Na Bukatar Kafa Cibiyoyin Bincike Kan Nau’ikan Dabbobi A Nijeriya
Noma Da Kiwo

Dalilin Kwararru Na Bukatar Kafa Cibiyoyin Bincike Kan Nau’ikan Dabbobi A Nijeriya

3 weeks ago
Tinubu Ya Kaddamar Da Sabon Shirin Aikin Noma Don Samar Da Wadataccen Abinci
Noma Da Kiwo

Tinubu Ya Kaddamar Da Sabon Shirin Aikin Noma Don Samar Da Wadataccen Abinci

3 weeks ago
Next Post
An Rantsar Da Ododo A Matsayin Gwamnan Kogi

An Rantsar Da Ododo A Matsayin Gwamnan Kogi

LABARAI MASU NASABA

Firaministan Sin Ya Jagoranci Taron Tattaunawa Tsakanin Shugabannin Sin Da EU Karo Na 25 Tare Da Shugaban Majalisar EU Da Shugabar Hukumar EU

Firaministan Sin Ya Jagoranci Taron Tattaunawa Tsakanin Shugabannin Sin Da EU Karo Na 25 Tare Da Shugaban Majalisar EU Da Shugabar Hukumar EU

July 24, 2025
Buƙatar Rijistar Sabbin Jam’iyyu Ta Kai 144 — INEC

Buƙatar Rijistar Sabbin Jam’iyyu Ta Kai 144 — INEC

July 24, 2025
Firaministan Sin Zai Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI 

Firaministan Sin Zai Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI 

July 24, 2025
Sojoji Sun Kwato Makamai Daga Hannun Ƴan Bindiga, Sun Ceto Yaro A Filato

Sojoji Sun Kwato Makamai Daga Hannun Ƴan Bindiga, Sun Ceto Yaro A Filato

July 24, 2025
Alakar Sin Da EU Na Bukatar Hadin Gwiwa Ba Raba-gari Ba

Alakar Sin Da EU Na Bukatar Hadin Gwiwa Ba Raba-gari Ba

July 24, 2025
Binciken CGTN: Masu Bayyana Raayoyi Na Turai Sun Gamsu Da Moriyar Cinikayya Tsakanin Sin Da Turai Sama Da Ta Turai Da Amurka

Binciken CGTN: Masu Bayyana Raayoyi Na Turai Sun Gamsu Da Moriyar Cinikayya Tsakanin Sin Da Turai Sama Da Ta Turai Da Amurka

July 24, 2025
Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Sabon Shugaban APC Na Ƙasa, Farfesa Yilwatda

Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Sabon Shugaban APC Na Ƙasa, Farfesa Yilwatda

July 24, 2025
Shugaban Sin Ya Aike Da Sakon Ta’aziyya Ga Takwaransa Na Rasha Sakamakon Hadarin Jirgin Saman Fasinja Da Ya Auku A Kasar

Shugaban Sin Ya Aike Da Sakon Ta’aziyya Ga Takwaransa Na Rasha Sakamakon Hadarin Jirgin Saman Fasinja Da Ya Auku A Kasar

July 24, 2025
Nijeriya Ta Gabatar Da Ƙudurin Karɓar Gasar Formula 1 A Abuja

Nijeriya Ta Gabatar Da Ƙudurin Karɓar Gasar Formula 1 A Abuja

July 24, 2025
Xi Ya Bukaci Sin Da EU Su Samar Da Kwanciyar Hankali Da Tabbaci Ga Duniya

Xi Ya Bukaci Sin Da EU Su Samar Da Kwanciyar Hankali Da Tabbaci Ga Duniya

July 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.