• English
  • Business News
Friday, October 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilan Karancin Kajin Gidan Gona A Nijeriya

by Abubakar Abba
2 years ago
Kaji

Kungiyar masu kiwon kajin gidan gona ta kasa, reshen babban birnin tarayyar Abuja (PAN), ta yi kira ga Gwamnatin Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu, ya gaggauta kawo dauki, musamman wajen yawan samun hauhawar farashin abincin da ake ciyar da kajin gidan gona.

Kazalika, ta yi gargadin cewa, idan har ba a dauki matakin da ya kamata ba, ko shakka babu wannan fanni na kiwon kaji zai nakasu ta hanyar durkushewa baki-daya.

  • Tsadar Magunguna Na Barazana Ga Rayukan Majinyata A Nijeriya
  • Gwamatin Tarayya Ta Fito Da Tsarin Cin Gajiyar Ma’adanan da Ke Jihar Nasarawa

Sakataren kungiyar, Hakeem Musa ne ya yi wannan kira a babban birnin tarayya Abuja, inda ya nuna matukar damuwarsa a kan yadda ake ci gaba da fuskantar wannan hauhawar farashi na abincin kaji a daidai wannan lokaci.

Har ila yau, Musa ya yi nuni da cewa, ya kamata gwamnatin ta taikama musu a wannan sana’a tasu kiwon kaji na gidan gona, domin samun damar tsayuwa da kafafunsu.

Sakataren ya kuma buga misali da cewa, buhun abincin kajin mai dauyin kilo 25, a watan Nuwambar da ya gabata, an sayar da shi kan Naira 8,000, wanda daga baya kuma farashin budun ya karu zuwa Naira 9,100.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Osun Ta Horar Da Mata 500 Amfani Da Takin Gargajiya

Dalilin IFAD Na Zuba Naira Biliyan 16 A Fannin Noma A Benuwe

Ya ci gaba da cewa, a makon farko na  watan  Disambar da ya gabata, farashin budun ya karu zuwa Naira 9,350 daga bisani kuma a makon farko farashin ya kai Naira 9,550, wanda kuma a mako na uku farashin ya karu zuwa Naira  10,950.

Hakeem ya kara da cewa, babu wanda ke da masaniyar lokacin da wannan farashi na abincin kaji zai daina yin tashin gwaron zabi.

Sai dai, sakataren ya bayyana fatan cewa, Gwamnatin Tinubu za ta mayar da hankali wajen bunkasa wannan fanni da kuma samar musu da tallafi .

A cewar tasa, mun fi bukatar a samar mana da tallafin kudi, domin ci gaba da tafiyar da wannan sana’a tamu.

Sannan kuma ya danganta wannan karanci na kaji a kan matsalar hauhawar farashin abincin kajin, musamman masara da waken suya, wadanda ake amfani da su wajen hadawa tare da sarrafa abincin kajin.

A karshe, Sakataren ya bayyana cewa, hauhawar farashin abincin kajin, na matukar haifar wa masu wannan sana’a nakasu, wanda hakan ne ke jawo wa wasunsu suke dakatar da yin sana’ar baki-daya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamnatin Osun Ta Horar Da Mata 500 Amfani Da Takin Gargajiya
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Osun Ta Horar Da Mata 500 Amfani Da Takin Gargajiya

October 11, 2025
Dalilin IFAD Na Zuba Naira Biliyan 16 A Fannin Noma A Benuwe
Noma Da Kiwo

Dalilin IFAD Na Zuba Naira Biliyan 16 A Fannin Noma A Benuwe

October 11, 2025
Yadda Haɗa Jinsin Shanu A Zamance Zai Ƙara Samar Da Madara
Noma Da Kiwo

Yadda Haɗa Jinsin Shanu A Zamance Zai Ƙara Samar Da Madara

October 11, 2025
Next Post
An Rantsar Da Ododo A Matsayin Gwamnan Kogi

An Rantsar Da Ododo A Matsayin Gwamnan Kogi

LABARAI MASU NASABA

Manzon Allah

Manzon Allah (SAW) Ne Ya Kafa Tushen Wayewar Kai A Duniya

October 17, 2025
An Kashe Mutane Da Dama Da Kone Gidajensu A Wani Hari Da Aka Kai Benuwai

Yadda ‘Yan Bindiga Ke Zafafa Hare-hare A Jihohin Arewa Maso Yamma

October 17, 2025
Shugaban Najeriya Ya Kaddamar Da Aikin Samar Da Ruwa Da Kamfanin Sin Ya Gudanar A Birnin Abuja

Afuwar Tinubu Ga Masu Manyan Laifuka: Ta Bar Baya Da Ƙura

October 17, 2025
Tsohon Ɗan Majalisar Bayelsa Ya Shawarci Jonathan Ya Guji Neman Takara A 2027

Tsohon Ɗan Majalisar Bayelsa Ya Shawarci Jonathan Ya Guji Neman Takara A 2027

October 17, 2025
Sin Da Afrika Sun Yi Alkawarin Tabbatar Da Nasarar Shirin TVET Na Nahiyar Afrika

Sin Da Afrika Sun Yi Alkawarin Tabbatar Da Nasarar Shirin TVET Na Nahiyar Afrika

October 16, 2025
NAWIA

Ranar Abinci Ta Duniya: NAWIA Ta Tallafawa Mata 114  Da Kayan Aikin Gona A Zamfara

October 16, 2025
Xi Ya Taya Hukumar FAO Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwa

Xi Ya Taya Hukumar FAO Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwa

October 16, 2025
Gaza

Wane Ci Gaba Yarjejeniyar Tsagaita Wuta A Gaza Ta Haifar?

October 16, 2025
Tsohon Ɗan Wasan Dambe, Ricky Hatton Ya Rataye Kansa

Tsohon Ɗan Wasan Dambe, Ricky Hatton Ya Rataye Kansa

October 16, 2025
Alkaluman Jin Ra’ayi na CGTN Sun Shaida Amincewar Al’umma Da Karfin Tattalin Arzikin Kasar Sin

Alkaluman Jin Ra’ayi na CGTN Sun Shaida Amincewar Al’umma Da Karfin Tattalin Arzikin Kasar Sin

October 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.