ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilan Karuwar Talauci A Nijeriya

by Leadership Hausa
2 years ago
Talauci

A watan Fabrairu na wannan shekarar, fusatattun matasa suka mamaye titunan garin Minna babban birnin Jihar Neja da wasu kuma matasan a Kano da suka gudanar da zanga-zanga a kan abin da suka kira tsadar rayuwa a kasar nan.Irin wannan zanga-zangar ta kuma barke a Jihar Ondo da wasu sassan kudu masu yammacin kasar nan.

Kungiyoyin addini sun lura da cewa rayuwa ga talaka a Nijeriya tana kara tsauwwala musamman abin da ya shafi farashin kayan abinci da kudin sufuri da kuma sauran al’amurran yau da kullum duk suna neman su gagari yawancin ‘yan Nijeriya.

  • Za A Bude Shafin Karbar Bashin Dalibai A Ranar 24 Ga Mayu
  • Sin: Karbuwar Hajojin Sin Masu Nasaba Da Sabbin Makamashi Ba Shi Da Nasaba Da Samar Da Tallafi

Kungiyar Kiristoci ta kasa CAN ta bayyana cewa, al’amarin yana kara ta’azarra ne sakamakon matsalar tsaro da ake fama da ita wanda kuma shi ya haifar da kashe-kashe da kuma garkuwa da mutane don mena kudin fansa.

ADVERTISEMENT

Idan za a iya tunawa, wannan jaridar ta ruwaito cewa, mai alfarma Sultan na Sakkwato, Alhaji Muhammadu Sa’ad Abubakar lll wanda kuma shi ne shugaban kungiyar Jama’atu Nasril Islam (JNI) ya bukaci gwamnatocin tarayya da na jihohi su gaggauta kawo dauki domin magance matsalar tsadar rayuwa wadda ita ce ta tunzura al’umma yin zanga-zanga a wasu sassan Nijeriya.

Kasar nan tana fuskantar matsanancin  tattalin arziki da ba a taba ganin irinsa ba a tarihin Nijeriya, al’umma na fama da talauci da tashin hankali a kowane lungu da sako na kasa.

LABARAI MASU NASABA

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

A yayin da wannan gwamnatin ke neman cika shekara daya da dare wa kan karagar mulki,mun lura cewa,babu wani abin da ya canja a cikin wannan shekarar sai da karin talauci da yunwa a tsakanin ‘yan Nijeriya.

Shugaban kasa Tinubu ya janye tallafin man fetur a ranar 29 ga watan Mayu 2024 yayin da aka tanstar da shi a matsayin shugaban kasa daga nan farashin man fetur ya yi tashi da ninkin baninkin 300 hakan kuma shi ya haifar da hauhawar farashin kayan abinci da sauran kayan amfani na yau da kullum.

Karuwar farashin man fetur da aka samu ta haifar da tsadar kayayyakin aiki ga kamfanoni da kuma kudin zirga-zirga haka kuma ya kai ga dora wadannan kudaden a kan talakawa masu amfani da kayan da kamfanonin ke sarrafawa.

Karuwar yanwa ta kuma haifar da tashin hankali a tsakanin matasa, har an fara samun fusasasstun matasa da suke tare hanya suna wasoson kayan abinci, dukkan wadannan kuma sakamakon tsare-tsare ne na Shugaban Kasa Bola Tinubu, musamman tsarinsa na karya darajar naira.

Sakamakon wadannan manufofin ne na tsare-tsaren tattalin arzikin Shugaba Tinubu ya haifar da matsanancin wahalar rayuwa ga al’ummar Nijeriya gaba daya.

Farashin kayan masarufi sun yi tashin gwauron zabo, kayan abinci kamar shinkafa,wake, masara tumatur da sauransu sun tashi da kashi 25.34 zuwa 40.01 a kididdigar da aka yi a watan Maris na shekarar 2024.

Ana cikin wannan matsin ne na tattalin arzikin sai kuma ga shi gwamnati ta kara kudin wutar lantarki da kashi 603 inda ya zama naira 225 a kan kilowat daya.

Duk da wannan karin ba wai ana samun wutan lantarkin yadda ya kamata ba ne,hakan kuma ya kai durkushewar kananan masana’antu da dama.

Babu ko kokwanto, mastalar tattalin arzikin da ake fama da ita a halin yanzu, tsanannin talauci da tsadar farashin abinci suna yin barazana ga rayuwar talakan Nijeriya.

Tsadar rayuwa na ci gaba da takura ‘yan Nijeriya,musamman matasa wadanda ke hankoron barin kasar domin samun ingantaccen rayuwa a kasashen waje.

A wani binciike da wata kungiya mai zaman kanta mai suna NOIPolls ta gudanar a watan Agusta na 2024 ta gano cewa kashi 63 na ‘yan Nijeriya a fadin kasar nan a shirye suke su yi kaura zuwa kasashen waje in sun samu damar yin haka.

Binciken ya kuma gano cewa matasa masu shekaru tsakanin 18 zuwa 35 sune a kan gaba wajen neman hanyar yin kaura zuwa kasashen waje.

Binciken ya kuma gano cewa, kashi 60 na masu neman fita kasashen waje suna yi ne domin samun ingantacciyar rayuwa a kasashen waje.

Amma kashi 3 na masu hankoron fita sun bayyana matsalar tsaro a matsayin dalilin su na neman fita kasashen waje.

A halin yanzu yunwa da matsalar tsaro na ci gaba da wahalar da ‘yan Nijeriya sai kuma ga hauhawar farashi ya kara kunno kai,tabbas al’umma na cikin wahala a Nijeriya.

Duk bangaren da ka duba a Nijeriya zaka lura da yadda garkuwa da mutane, ta’addanci, harkokin ‘yan bindiga suke aukuwa a kullum garin Allah ya waye.

Ci gaba da tabarbarewar darajar naira da kuma yadda gwamnati ta kasa shawo kan lamarin ya kara jefa ‘yan Nijeriya cikin halin ni ‘yasu.

Yayin da lamarin yake kara ta’azzara,dole gwamnati ta gaggauta daukar matakan ta yin maganin matsalar tattalin arzikin da ake fuskanta da kuma matsalar tsaro a sassan Nijeriya wadanda sune suka haifar da tsadar rayuwa ga talakawa.

Talauci
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
  • Leadership Hausa
    Ikirarin Cewa Sanata Abdul’aziz Yari Abubakar, Marafan Sokoto, Nauyi Ne Ga Jihar Zamfara Da Jam’iyyar APC Ba Ta Da Tushe
  • Leadership Hausa
    Nazarin Kisan Gillar Da ‘Yan Kato Da Gora Suka Yi Wa Wani Matashi A Biniwe

MASU ALAKA

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Waɗanda Suka Kai Hari Cocin Owo Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya
Manyan Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Waɗanda Suka Kai Hari Cocin Owo Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya

June 3, 2026
Next Post
Noman Daminar Bana: Kisan Manoma Na Mayar Da Hannun Agogo Baya

Noman Daminar Bana: Kisan Manoma Na Mayar Da Hannun Agogo Baya

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.