ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Noman Daminar Bana: Kisan Manoma Na Mayar Da Hannun Agogo Baya

by Abubakar Abba
2 years ago
Noman

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

A yayin da daminar bana ta fara kankama a wasu jihohin kasar nan, hare-haren da ‘yan bindiga ke kai wa a kan manoma sai kara kamari yake yi inda hakan ke janyo karin asarar rayukann manoman.

Masu bibiyar al’amura a kasar nan, sun bayyana cewa, kisan da ‘yan bindiga ke yi wa manoma ya yi kamari ne daga zamanin tsohuwar Gwamnatin Shugaban Kasa Muhammadu Buhari, kuma ko da aka rantsar da sabuwar gwamnati, ‘yan bindigar sun ci gaba da cin karen su babu babbaka duk da nasarorin da mai bai wa shugaban kasa shawara kan tsaron kasa, Malam Nuhu Ribadu ya ce jami’an tsaro suna samu a kansu.

  • Za A Bude Shafin Karbar Bashin Dalibai A Ranar 24 Ga Mayu
  • Shugabannin Sin Da Rasha Sun Tattauna Da Juna

Rahotanin sun bayyana cewa, wannan lamarin ya janyo wasu manoman yin watsi da gonakinsu musamman a jihohin da hare-haren na ‘yan bindiga ya fi kamari a kamar su Zamfara, Benuwai, Sakkkwato, Neja, Filato, Kaduna da kuma Katsina.

Bugu da kari, a wasu jihohin kamar Zamfara, Neja, Kaduna Sokoto, an jima ana zargin ‘yan bindigar da sanya wa manoman haraji kafin su ba su damar noma gonakinsu ko kuma girbe amfanin da suka noma.

An ruwaito shugaban kungiyar manoma ta kasa (AFAN) na Jihar Sokoto, Jamilu Sanusi, yana bayyana cewa, ’yan kungiyarsu sun yi asarar fiye da Naira biliyan 3 wajen biyan kudin fansa ga ‘yan bindiga.

Ya kara da cewa, sama da kashi 80 na ‘yan gudun hijira da ke zaune a sansanin ‘yan gudun hijira daban-daban a jihar manoma ne.

A cewarsa, kasa da kadada 10,000 a jihar manoma suka gaza nomawa a kusan sama da shekaru uku, inda kuma ‘yan bindiga suka hallaka sama da manoma 28 a cikin wannan shekarar a jihar.

A wani ra’ayi da Jaridar Punch ta wallafa a ranar 25 ga Maris, 2024, cikin wata uku daga farkon shekarar nan kawai, kimain manoma 165 ne ‘yan bindiga suka hallaka har lahira. Al’amarin bai tsaya nan ba domin ko a makon da ya gabata, akalla manoma 30 ciki har da wani malamin addini aka yi wa kisan gilla a Jihar Zamfara.

Mai magana da yawun rundunar ‘yansandan jihar, ASP Yazid Abu Abubakar, ya tabbatar da aukuwar wannan kisan a kananan hukumomi biyu na jihar.

Kafafen yada labarai sun ruwaito cewa, harin ya auku ne a kananan hukumomin Maradun da Tsafe a yayin da manoman ke aikin sharar gonakansu.

Masana sun yi nuni da cewa, hauhawan farashin kayan abinci a daukacin fadin Nijeriya na da nasaba da ta’asar da ‘yan bindiga ke ci gaba da yi.

Wasu alkaluma sun bayyana cewa, hauhawan farashin kayan abinci a watan Maris, 2024, ya kai kashi 40 a cikin dari, inda ya rika karuwa tun daga na watan Janairun 2024 wanda yake kashi 35.41 a cikin dari

A kwanan baya, an ruwaito shugaban Karamar Hukumar Agatu da ke Benuwe, Yakubu Ochepo yana tabbatar da wani harin da ‘yan bindigar suka kai a a yankin Ogbaulu inda suka yi wa manoma uku yankan Rago a cikin gonakansu.

Kazalika, an ruwaito wani shugaban kungiyar manoma a Jihar Nasarawa Mista Denis Utsa, yana tabbatar da kisan wasu manoma uku a yankin Kadarko da ke a Karamar Hukumar Keana ta jihar, tare da kuma hallaka wasu manoma uku a yankin Tse-Abir Azer da ke a Kadarko.

A karamar hukumar Bokkos ta Jihar Filato an ruwaito wani manomi mai suna Stephen Garuba yana cewa, bai san adadin manoman da ‘yan bindiga suka sace ba, inda ya ce, sun kuma kona amfanin gona na miliyoyin Naira.

A cewarsa, hare-haren na ‘yan bindigar ya fi kamari a Kanannan Hukumomin Munya, Shiroro, Meriga, Paikoro, Rafi Mashegu, Wushishi da Borgu.

A Jihar Borno, nan ma abin bai sauya zani ba, sai dai, babu wanda zai iya fadar adadin manoman da ‘yan bindiga duka kashe.

Bugu da kari, a Jihar Kaduna, manoma nusamman na Shinkafa a jihar na ci gaba da kokawa kan hare-haren da ‘yan bindiga ke kai masu wanda haka ya dakatar da su zuwa gonakansu don nomawa.

An ruwaito shugaban kunkiyar, Alhaji Mohammed Umar Numbu yana bayyana cewa, kimanin ‘ya’yan kungiyar 72,000 a yanzu, ba sa iya zuwa gonakansu.

Sakamakon ta’asar da ‘yan ta’addan ke tafkwa, ‘Yan Nijeria na ci gaba da rayuwa cikin mawuyacin hali. Inda sabbin rahotannin da ke fitowa ke nunar da cewa manoma na barin gonakinsu a jihohi da dama saboda ta’addanci da sauran nau’o’in rashin tsaro.

A cikin wani rahoto da aka fitar ranar 20 ga Maris, Rundunar Sojan Nijerriya ta bayyana cewa manoma suna mutuwa a sababin hare-haren ‘yan ta’addan daji. Wasu kuma ana garkuwa da su. Jihohin da suka fi fama da wannan lamari sun hada da Binuwe, Sokoto, Neja, Pilato. Kaduna, Zamfara, da Katsina.

Ba abin mamaki ba ne yadda tsadar kayan abinci ke kara ta’azzara a fadin kasar nan, yayin da manoma ke watsi da sana’ar da suka gada iyaye da kakanni saboda tashe-tashen hankula.

Ana ci gaba da kiraye-kiraye ga Gwamnatin Bola Tinubu da ta kawo karshen kashe-kashen da ake yi wa manoma a fadin kasar nan, ta hanyar daukar kwararan matakai na sabunta tsaro.

Baya ga manoma 165 da aka ruwaito sun rasa rayukansu a zuwa Maris, 2024. A Benuwai, ‘yan bindiga sun yi wa manoma 15 kisan gilla a Karamar Hukumar Apa inda hakan ya kara adadin wadanda aka kashe a yankunan jihar zuwa 130. Hakazalika, kashe-kashen manoman a Sakkwato, ya yi sanadin mutuwar 28, in ji kungiyar manoman Nijeriya. Haka nan ta ce ‘yan bindigar sun kori manoma a Neja da Filato.

Wata sanarwa da wata kungiyar tattara bayanan sirri ta SBM ta fitar a watan Maris, ta ce ana garkuwa da ‘yan Nijeriya biyar a kullum a shekarar 2024. ‘Yan bindiga suna garkuwa da daruruwan mutane musamman a jihohin Kaduna, Sokoto da Borno, in ji ta.

Bayan kisan da ‘yan ta’addan ke wa manoma a farkon damina, har ila yau kalilan da suka samu dama suka noma dan abin da za su ci, su ma ba su tsira ba domin ‘yan ta’addan sukan sanya haraji ga manoman kafin su kyale su, su girbe amfanin gonakinsu musamman a sassan jihohin Neja da Kaduna, lamarin da ya tilasta wa manoma zama a gida cikin yunwa da rashin taimako.

Gwamnatin Tinubu dai ta yi alkawarin tabbatar da aikin gona na rani da damina ta hanyar ware makudan kudade daban-daban ciki har da na noman masara akalla na Naira Biliyan 200, bayan cire tallafin mai, sai dai har yanzu babu wani abin a zo a gani kan hakan.

Noman
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC
Manyan Labarai

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026
Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 3, Sun Ƙwato Makamai A Sakkwato
Manyan Labarai

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

July 14, 2026
Next Post
…Nijeriya Na Asarar Naira Biliyan 4.8 Duk Shekara Kan Rikicin Manoma Da Makiyaya -Mercy Corps

…Nijeriya Na Asarar Naira Biliyan 4.8 Duk Shekara Kan Rikicin Manoma Da Makiyaya -Mercy Corps

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.