Wani bidiyo da ya karaɗe kafafen sada zumunta wanda ya nuna wani ɗan sanda ya durƙusa yana gyara igiyar takalmin shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje, ya jawo ce-ce-ku-ce.
Sai dai Aminu Dahiru Ahmad, ɗaya daga cikin hadiman Ganduje, ya bayyana cewa ba wani abu ne da za a tada jijiyar wuya a kansa ba.
- Radda Ya Raba Wa Manoma Taki A Jihar Katsina
- Aikin Hajjin 2025 Ya Fara A Hukumance Yayin Da Tawagar NAHCON Ta Musamman Ta Tashi Zuwa Makkah
Ya ce ɗan sandan ya gyara igiyar ne kawai domin hana Ganduje faɗuwa.
Ya ce waɗanda ke yaɗa bidiyon suna neman tada hargitsi ne saboda ba sa jin daɗin nasarorin da Ganduje ke samu a halin yanzu.
“Bidiyon yana nuna yadda dangantaka ke da kyau tsakanin Ganduje da ma’aikatansa. Yana girmama mu kuma muna jin daɗin aiki da shi,” in ji Aminu.
Ya ƙara da cewa Ganduje mutum ne da kullum yana cikin yi wa ma’aikatansa fara’a.
Ya ce masu yaɗa bidiyon na ƙoƙarin tada rikici ne domin dalilan siyasa.
“Wannan ba zai rage farin jinin Ganduje ba,” in ji shi.
“Ya yi wa Jihar Kano aiki tuƙuru, yanzu kuma yana yi wa ƙasa. ‘Yan adawa ba sa jin daɗin yadda APC ke ƙara ƙarfi a ƙarƙashin jagorancinsa.”
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp