• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dan Jarida Ya Kirkiro Manhajar Bincike Ta Hausa

by Khalid Idris Doya
7 months ago
in Labarai
0
Dan Jarida Ya Kirkiro Manhajar Bincike Ta Hausa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wani dan jarida mai jin harsuna biyu, Alhassan Bala, ya karkiro da wata manhajar binciko gaskiya da sahihancin lamura da ya yi wa suna da ‘Alkalanci’ (The Arbiter).

Manhajar wacce ta maida hankali wajen gano gaskiya da hakikanin ikirarorin lafiya, harkokin siyasa da wasu bangarori daban-daban dukka a cikin harshen Hausa.

  • Xi Ya Amsa Wasikar Wakilan Daliban Da Suka Halarci Gasar Kere-Keren Kimiyya Ta Kasa Da Kasa Ta Kasar Sin
  • ÆŠaliban Kwalejin Kimiyya Ta Jega Sun Yi Zanga-Zanga Har Da Ƙone-Ƙone

Babban manufar samar da manhajar shi ne, domin a taimaka wajen kare mutane daga fadawa tarkon ‘yan damfara da masu yada karya a tsakanin jama’a.

Karin tagomashi kan wannan manhajar shi ne, za ta taimaka kuma wajen gano gaskiya ko sahihancin hotuna da bidiyoyi domin wayar da kan masu karatu da harshen Hausa a kasar Nijeriya, Kamaru, Ghana domin cire kokwonto ko shakku kan hotuna ko bidiyo na karya ko na gaskiya.

Wannan lamarin ya zo a kan gaba kuma zai taimaka matuka gaya musamman yadda a irin wannan lokacin wasu mutane suka dukufa na amfani da ‘photoshop’ da kirkirarriyar basirar (AI) wajen hada hotuna da bidiyo na bogi domin shagaltar da hankulan jama’a ko neman kudin daga wajensu.

Labarai Masu Nasaba

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

“Mun nazarci duniyar fasahar zamani, kuma mun gano yadda masu amfani da kafafen fasahar zamani da harshen Hausa ke amfani wajen shagaltar da hankula da yada karerayi a tsakanin masu jin harshen Hausa.

“Sannan ana yawan samun ikirarin yawan rashin lafiya na karya da kuma jama’a su na yarda da hakan.

“Don haka ya zama abu mai muhimmanci a garemu da mu samar da manhajar da za ta jagoranci wayar da kan masu jin harshen Hausa,” kamar yadda Bala ya shaida ta cikin sanarwar da ya fitar a ranar Lahadi.

Dan jarida ya ci gaba da cewa, “Manhajar ‘Alkalanci’ za mu dukufa wajen ilmantar da mutane kan yadda za su kare kansu daga fadawa tarkon ‘yan damfara da masu yaudara ko masu yada bayanan karya ko shaci fadi, hotuna da bidiyo.”

Alhassan Bala, wanda ya shafe shekaru masu yawa yana aikin jarida a kafafen yada labarai daban-daban, yanzu haka yana aikin jarida ne a gidan rediyon Muryar Amurka na sashin Hausa da na Ingilishi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Dan JaridaHausaManhaja
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar Da Kwamitoci Shida Domin Ƙara Inganta Jihar Zamfara

Next Post

Babban Layin Samar Da Wutar Lantarkin Nijeriya Ya Lalace Sau 7 A 2024

Related

UTME
Manyan Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

2 hours ago
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista
Labarai

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

2 hours ago
gaza
Labarai

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

4 hours ago
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa
Labarai

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

5 hours ago
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja
Labarai

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

7 hours ago
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu
Manyan Labarai

JAMB: TangarÉ—ar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

7 hours ago
Next Post
Babban Layin Samar Da Wutar Lantarkin Nijeriya Ya Lalace Sau 7 A 2024

Babban Layin Samar Da Wutar Lantarkin Nijeriya Ya Lalace Sau 7 A 2024

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: TangarÉ—ar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.