• English
  • Business News
Saturday, November 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dan Jarida Ya Kirkiro Manhajar Bincike Ta Hausa

by Khalid Idris Doya
1 year ago
Jarida

Wani dan jarida mai jin harsuna biyu, Alhassan Bala, ya karkiro da wata manhajar binciko gaskiya da sahihancin lamura da ya yi wa suna da ‘Alkalanci’ (The Arbiter).

Manhajar wacce ta maida hankali wajen gano gaskiya da hakikanin ikirarorin lafiya, harkokin siyasa da wasu bangarori daban-daban dukka a cikin harshen Hausa.

  • Xi Ya Amsa Wasikar Wakilan Daliban Da Suka Halarci Gasar Kere-Keren Kimiyya Ta Kasa Da Kasa Ta Kasar Sin
  • Ɗaliban Kwalejin Kimiyya Ta Jega Sun Yi Zanga-Zanga Har Da Ƙone-Ƙone

Babban manufar samar da manhajar shi ne, domin a taimaka wajen kare mutane daga fadawa tarkon ‘yan damfara da masu yada karya a tsakanin jama’a.

Karin tagomashi kan wannan manhajar shi ne, za ta taimaka kuma wajen gano gaskiya ko sahihancin hotuna da bidiyoyi domin wayar da kan masu karatu da harshen Hausa a kasar Nijeriya, Kamaru, Ghana domin cire kokwonto ko shakku kan hotuna ko bidiyo na karya ko na gaskiya.

Wannan lamarin ya zo a kan gaba kuma zai taimaka matuka gaya musamman yadda a irin wannan lokacin wasu mutane suka dukufa na amfani da ‘photoshop’ da kirkirarriyar basirar (AI) wajen hada hotuna da bidiyo na bogi domin shagaltar da hankulan jama’a ko neman kudin daga wajensu.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

“Mun nazarci duniyar fasahar zamani, kuma mun gano yadda masu amfani da kafafen fasahar zamani da harshen Hausa ke amfani wajen shagaltar da hankula da yada karerayi a tsakanin masu jin harshen Hausa.

“Sannan ana yawan samun ikirarin yawan rashin lafiya na karya da kuma jama’a su na yarda da hakan.

“Don haka ya zama abu mai muhimmanci a garemu da mu samar da manhajar da za ta jagoranci wayar da kan masu jin harshen Hausa,” kamar yadda Bala ya shaida ta cikin sanarwar da ya fitar a ranar Lahadi.

Dan jarida ya ci gaba da cewa, “Manhajar ‘Alkalanci’ za mu dukufa wajen ilmantar da mutane kan yadda za su kare kansu daga fadawa tarkon ‘yan damfara da masu yaudara ko masu yada bayanan karya ko shaci fadi, hotuna da bidiyo.”

Alhassan Bala, wanda ya shafe shekaru masu yawa yana aikin jarida a kafafen yada labarai daban-daban, yanzu haka yana aikin jarida ne a gidan rediyon Muryar Amurka na sashin Hausa da na Ingilishi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

November 1, 2025
Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar
Manyan Labarai

Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

November 1, 2025
An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3
Manyan Labarai

An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

November 1, 2025
Next Post
Babban Layin Samar Da Wutar Lantarkin Nijeriya Ya Lalace Sau 7 A 2024

Babban Layin Samar Da Wutar Lantarkin Nijeriya Ya Lalace Sau 7 A 2024

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

November 1, 2025
Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

November 1, 2025
An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

November 1, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Yadda Gwamnatin Tarayya Ta Dakile Yaɗuwar Ɓarkewar Cutar Dabbobi A Jihar Jigawa

November 1, 2025
Jerin Gwarazan Taurarinmu

Jerin Gwarazan Taurarinmu

November 1, 2025
CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

October 31, 2025
Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

October 31, 2025
Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

October 31, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

October 31, 2025
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

October 31, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.