• English
  • Business News
Tuesday, October 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dan Majalisar Kano Ya Dauki Malamai 105 Aikin Wucin Gadi

bySadiq
3 years ago
inLabarai
0
Dan Majalisar Kano Ya Dauki Malamai 105 Aikin Wucin Gadi

Dan majalisar dokokin Jihar Kano, Labaran Madari, daga mazabar Warawa a jam’iyyar APC, ya dauki malaman wucin gadi 105 domin bunkasa ilimi a mazabarsa.

Mista Madari ya gabatar da wasikar daukar aikin ga sabbin malaman da aka dauka a ranar Laraba a Warawa.

  • Ranar Malamai Ta Duniya: Yadda Yajin Aikin ASUU Ya Yi Wa Ilimi Katutu A Wuya
  • Zargin Badakalar Kudade: Kotu Ta Wanke Magu

Ya ce an yi hakan ne domin a kara yawan malamai da kuma rage rashin aikin yi a tsakanin al’umma.

Dan majalisar wanda kuma shi ne shugaban masu rinjaye ya yabawa gwamna Abdullahi Ganduje bisa bullo da tsarin ilimin kyauta kuma dole a jihar.

Mista Madari ya kara da cewa, akwai bukatar a gaggauta ba da gudummawar kasonsa don samun nasarar manufofin.

Labarai Masu Nasaba

Tsaro: Gwamnan Kogi Ya Ayyana Yaƙi Da Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ka’ida Ba Da ‘Yan Bindiga

Majalisar Wakilai Ta Kafa Kwamiti Da Zai Binciki Harkokin Kirifto Da POS A Nijeriya

Dan majalisar ya bayyana cewa yana cikin tawagar da suka yi nasarar bullo da shirin bayar da ilimi kyauta kuma tilas ga yara da Ganduje ya yi.

Mista Madari, ya ce ya gina azuzuwa 35 da bandaki 11 a makarantun Firamare da Sakandare da Islamiyya.

Shugaban masu rinjayen, ya kara da cewa ya samar da kayan koyo da koyarwa, da kuma kammala ga makarantar sakandaren ‘yan mata, da ke Warawa da dai sauransu.

“Ina so in tabbatar muku da kudirina na kare muradunku ga majalisar don samar da ribar dimokuradiyya,” in ji shi.

Mista Madari, ya ce za a rika biyan malaman alawus-alawus duk wata kuma za a bi diddigin yadda gwamnatin jihar za ta karbe su a matsayin malamai na dindindin da kuma karbar fansho.

Kwamishinan Ilimi, Ya’u Yan’shana, wanda ya bayyana shirin a matsayin wanda ya dace, ya yabawa dan majalisar bisa wannan karimcin da ya yi.

Kwamishinan ya jaddada kudirin gwamnatin jihar na samar da ilimi kyauta.

Ya kuma bukaci masu hannu da shuni da su bayar da tasu gudunmawarsu ta hanyar daukar malamai aiki ga al’ummarsu.

Shugaban hukumar kula da ilimin bai daya na Jihar Kano (SUBEB), Danlami Hayyo, ya jaddada kudirin hukumar na horar da sabbin malaman domin cimma burin da ake so.

Mista Hayyo ya ce shiga tsakani zai taimaka matuka wajen habaka ilimi a matakin farko, inda ya ce bangaren ilimi na bukatar karin irin wannan kokari.

Sakataren ilimi na karamar hukumar Warawa, Ibrahim Idris ya ce an yi amfani da samfuri wajen zabar kwararrun masu matakin ilimi na NCE, a unguwanni 15 na karamar hukumar.

Tags: AikiGandujekanoMalamaiWadariWarawa
ShareTweetSendShare
Sadiq

Sadiq

Related

Tsaro: Gwamnan Kogi Ya Ayyana Yaƙi Da Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ka’ida Ba Da ‘Yan Bindiga
Labarai

Tsaro: Gwamnan Kogi Ya Ayyana Yaƙi Da Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ka’ida Ba Da ‘Yan Bindiga

2 hours ago
Majalisar Wakilai Ta Kafa Kwamiti Da Zai Binciki Harkokin Kirifto Da POS A Nijeriya
Labarai

Majalisar Wakilai Ta Kafa Kwamiti Da Zai Binciki Harkokin Kirifto Da POS A Nijeriya

3 hours ago
Ya Kamata Nijeriya Ta Ayyana Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda — Tsohon Hafsan Sojin Ƙasa
Manyan Labarai

Ya Kamata Nijeriya Ta Ayyana Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda — Tsohon Hafsan Sojin Ƙasa

4 hours ago
Next Post
NCCE Ta Garkame Kwalejojin Bogi 41 Da Ke Bayar da Shaidar NCE A Bauchi

NCCE Ta Garkame Kwalejojin Bogi 41 Da Ke Bayar da Shaidar NCE A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

Isra’ila Ta Kashe Falasɗinawa Sama Da 66,000 A Gaza Cikin Shekaru 2 – Rahoto

Isra’ila Ta Kashe Falasɗinawa Sama Da 66,000 A Gaza Cikin Shekaru 2 – Rahoto

October 7, 2025
Tsaro: Gwamnan Kogi Ya Ayyana Yaƙi Da Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ka’ida Ba Da ‘Yan Bindiga

Tsaro: Gwamnan Kogi Ya Ayyana Yaƙi Da Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ka’ida Ba Da ‘Yan Bindiga

October 7, 2025
Majalisar Wakilai Ta Kafa Kwamiti Da Zai Binciki Harkokin Kirifto Da POS A Nijeriya

Majalisar Wakilai Ta Kafa Kwamiti Da Zai Binciki Harkokin Kirifto Da POS A Nijeriya

October 7, 2025
Ya Kamata Nijeriya Ta Ayyana Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda — Tsohon Hafsan Sojin Ƙasa

Ya Kamata Nijeriya Ta Ayyana Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda — Tsohon Hafsan Sojin Ƙasa

October 7, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Tinubu Ya Bayar Da Umarnin Rage Kuɗin Aikin Hajjin 2026

October 7, 2025
Kotu Ta Aike Da Ɗan TikTok Gidan Gyaran Hali Kan Bidiyon Batsa A Kano

Kotu Ta Aike Da Ɗan TikTok Gidan Gyaran Hali Kan Bidiyon Batsa A Kano

October 6, 2025
Kada Ku Yi Sanadiyar Rugujewar Matatar Mai Ta Dangote – Shettima Ga PENGASSAN 

Kada Ku Yi Sanadiyar Rugujewar Matatar Mai Ta Dangote – Shettima Ga PENGASSAN 

October 6, 2025
Habakar Yin Sayayya A Lokacin Hutu Ta Nuna Kirkira Da Irin Ci Gaban Da Tattalin Arzikin Kasar Sin Ke Samu   

Habakar Yin Sayayya A Lokacin Hutu Ta Nuna Kirkira Da Irin Ci Gaban Da Tattalin Arzikin Kasar Sin Ke Samu   

October 6, 2025
Karamin Ofishin Jakadancin Sin Da Ke Legas Ya Yi Bikin Bunkasa Al’adu Na Bikin Tsakiyar Kaka

Karamin Ofishin Jakadancin Sin Da Ke Legas Ya Yi Bikin Bunkasa Al’adu Na Bikin Tsakiyar Kaka

October 6, 2025
Minista Nnaji Ya Yi Ƙarar Jami’ar UNN Kan Rikicin Takardun Kammala Makaranta

Minista Nnaji Ya Yi Ƙarar Jami’ar UNN Kan Rikicin Takardun Kammala Makaranta

October 6, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.