• English
  • Business News
Thursday, July 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dan Majalisar Kano Ya Dauki Malamai 105 Aikin Wucin Gadi

by Sadiq
3 years ago
in Labarai
0
Dan Majalisar Kano Ya Dauki Malamai 105 Aikin Wucin Gadi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dan majalisar dokokin Jihar Kano, Labaran Madari, daga mazabar Warawa a jam’iyyar APC, ya dauki malaman wucin gadi 105 domin bunkasa ilimi a mazabarsa.

Mista Madari ya gabatar da wasikar daukar aikin ga sabbin malaman da aka dauka a ranar Laraba a Warawa.

  • Ranar Malamai Ta Duniya: Yadda Yajin Aikin ASUU Ya Yi Wa Ilimi Katutu A Wuya
  • Zargin Badakalar Kudade: Kotu Ta Wanke Magu

Ya ce an yi hakan ne domin a kara yawan malamai da kuma rage rashin aikin yi a tsakanin al’umma.

Dan majalisar wanda kuma shi ne shugaban masu rinjaye ya yabawa gwamna Abdullahi Ganduje bisa bullo da tsarin ilimin kyauta kuma dole a jihar.

Mista Madari ya kara da cewa, akwai bukatar a gaggauta ba da gudummawar kasonsa don samun nasarar manufofin.

Labarai Masu Nasaba

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

Dan majalisar ya bayyana cewa yana cikin tawagar da suka yi nasarar bullo da shirin bayar da ilimi kyauta kuma tilas ga yara da Ganduje ya yi.

Mista Madari, ya ce ya gina azuzuwa 35 da bandaki 11 a makarantun Firamare da Sakandare da Islamiyya.

Shugaban masu rinjayen, ya kara da cewa ya samar da kayan koyo da koyarwa, da kuma kammala ga makarantar sakandaren ‘yan mata, da ke Warawa da dai sauransu.

“Ina so in tabbatar muku da kudirina na kare muradunku ga majalisar don samar da ribar dimokuradiyya,” in ji shi.

Mista Madari, ya ce za a rika biyan malaman alawus-alawus duk wata kuma za a bi diddigin yadda gwamnatin jihar za ta karbe su a matsayin malamai na dindindin da kuma karbar fansho.

Kwamishinan Ilimi, Ya’u Yan’shana, wanda ya bayyana shirin a matsayin wanda ya dace, ya yabawa dan majalisar bisa wannan karimcin da ya yi.

Kwamishinan ya jaddada kudirin gwamnatin jihar na samar da ilimi kyauta.

Ya kuma bukaci masu hannu da shuni da su bayar da tasu gudunmawarsu ta hanyar daukar malamai aiki ga al’ummarsu.

Shugaban hukumar kula da ilimin bai daya na Jihar Kano (SUBEB), Danlami Hayyo, ya jaddada kudirin hukumar na horar da sabbin malaman domin cimma burin da ake so.

Mista Hayyo ya ce shiga tsakani zai taimaka matuka wajen habaka ilimi a matakin farko, inda ya ce bangaren ilimi na bukatar karin irin wannan kokari.

Sakataren ilimi na karamar hukumar Warawa, Ibrahim Idris ya ce an yi amfani da samfuri wajen zabar kwararrun masu matakin ilimi na NCE, a unguwanni 15 na karamar hukumar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AikiGandujekanoMalamaiWadariWarawa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Dalibai Sun Yi Zanga-Zanga Kan Korarsu Daga Cibiyar Koyar Da Sana’o’i Ta Dangote A Kano

Next Post

NCCE Ta Garkame Kwalejojin Bogi 41 Da Ke Bayar da Shaidar NCE A Bauchi

Related

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

3 hours ago
An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano
Labarai

An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

4 hours ago
Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta
Labarai

Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

6 hours ago
Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

6 hours ago
EFCC Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Ɓullar Sabbin Hanyoyin Damfarar Kuɗi
Labarai

EFCC Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Ɓullar Sabbin Hanyoyin Damfarar Kuɗi

7 hours ago
Dangote Ya Yaba Wa Tinubu Kan Samar Da Ababen More Rayuwa A Nijeriya
Labarai

Dangote Ya Yaba Wa Tinubu Kan Samar Da Ababen More Rayuwa A Nijeriya

10 hours ago
Next Post
NCCE Ta Garkame Kwalejojin Bogi 41 Da Ke Bayar da Shaidar NCE A Bauchi

NCCE Ta Garkame Kwalejojin Bogi 41 Da Ke Bayar da Shaidar NCE A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

July 10, 2025
Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

July 10, 2025
Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

July 10, 2025
Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

July 10, 2025
Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

July 10, 2025
An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

July 10, 2025
Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

July 10, 2025
Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

July 10, 2025
An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

July 10, 2025
Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

July 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.