ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dan Majalisar Kano Ya Dauki Malamai 105 Aikin Wucin Gadi

by Sadiq
4 years ago
Kano

Dan majalisar dokokin Jihar Kano, Labaran Madari, daga mazabar Warawa a jam’iyyar APC, ya dauki malaman wucin gadi 105 domin bunkasa ilimi a mazabarsa.

Mista Madari ya gabatar da wasikar daukar aikin ga sabbin malaman da aka dauka a ranar Laraba a Warawa.

  • Ranar Malamai Ta Duniya: Yadda Yajin Aikin ASUU Ya Yi Wa Ilimi Katutu A Wuya
  • Zargin Badakalar Kudade: Kotu Ta Wanke Magu

Ya ce an yi hakan ne domin a kara yawan malamai da kuma rage rashin aikin yi a tsakanin al’umma.

ADVERTISEMENT

Dan majalisar wanda kuma shi ne shugaban masu rinjaye ya yabawa gwamna Abdullahi Ganduje bisa bullo da tsarin ilimin kyauta kuma dole a jihar.

Mista Madari ya kara da cewa, akwai bukatar a gaggauta ba da gudummawar kasonsa don samun nasarar manufofin.

LABARAI MASU NASABA

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Dan majalisar ya bayyana cewa yana cikin tawagar da suka yi nasarar bullo da shirin bayar da ilimi kyauta kuma tilas ga yara da Ganduje ya yi.

Mista Madari, ya ce ya gina azuzuwa 35 da bandaki 11 a makarantun Firamare da Sakandare da Islamiyya.

Shugaban masu rinjayen, ya kara da cewa ya samar da kayan koyo da koyarwa, da kuma kammala ga makarantar sakandaren ‘yan mata, da ke Warawa da dai sauransu.

“Ina so in tabbatar muku da kudirina na kare muradunku ga majalisar don samar da ribar dimokuradiyya,” in ji shi.

Mista Madari, ya ce za a rika biyan malaman alawus-alawus duk wata kuma za a bi diddigin yadda gwamnatin jihar za ta karbe su a matsayin malamai na dindindin da kuma karbar fansho.

Kwamishinan Ilimi, Ya’u Yan’shana, wanda ya bayyana shirin a matsayin wanda ya dace, ya yabawa dan majalisar bisa wannan karimcin da ya yi.

Kwamishinan ya jaddada kudirin gwamnatin jihar na samar da ilimi kyauta.

Ya kuma bukaci masu hannu da shuni da su bayar da tasu gudunmawarsu ta hanyar daukar malamai aiki ga al’ummarsu.

Shugaban hukumar kula da ilimin bai daya na Jihar Kano (SUBEB), Danlami Hayyo, ya jaddada kudirin hukumar na horar da sabbin malaman domin cimma burin da ake so.

Mista Hayyo ya ce shiga tsakani zai taimaka matuka wajen habaka ilimi a matakin farko, inda ya ce bangaren ilimi na bukatar karin irin wannan kokari.

Sakataren ilimi na karamar hukumar Warawa, Ibrahim Idris ya ce an yi amfani da samfuri wajen zabar kwararrun masu matakin ilimi na NCE, a unguwanni 15 na karamar hukumar.

MASU ALAKA

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa
Manyan Labarai

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta
Manyan Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje
Manyan Labarai

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Next Post
NCCE Ta Garkame Kwalejojin Bogi 41 Da Ke Bayar da Shaidar NCE A Bauchi

NCCE Ta Garkame Kwalejojin Bogi 41 Da Ke Bayar da Shaidar NCE A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.