• English
  • Business News
Monday, August 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dan Takarar Gwamnan ZLP A Bauchi Ya Musanta Janye Takararsa

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Siyasa
0
Dan Takarar Gwamnan ZLP A Bauchi Ya Musanta Janye Takararsa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jam’iyyar ZLP a Jihar Bauchi, ta bukaci babban lauya, Eko Ejembi (SAN) da abokan aikinsa da su fara shirye-shiryen daukar matakan shari’a kan kwamitin yakin zaben shugaban kasa na jam’iyyar PDP bisa bayyana cewa dan takarar jam’iyyar a Jihar Bauchi, Ambasada Khalid Arewa ya koma PDP tare da janye takararsa.

Idan ba a manta ba a ranar Talata kwamitin yakin zaben shugaban kasa na jam’iyyar PDP, ya ziyarci Jihar Bauchi domin yakin zabensa, inda kusoshi na jam’iyyar ciki har da dan takarar shugaban kasa, Atiku Abubakar da gwamna Bala Muhammad suka halarta, inda aka bayyana sunayen wasu da suka koma PDP ciki har da ayyana sunan dan takarar gwamna na jam’iyyar ZLP.

  • Ya Kamata Amurka Ta Sauya Mahangar Ta Game Da Sin
  • Na Yi Alkawari Zan Kawar Da Matsalolin Al’umma, In Ji Tinubu

A hirarsa da LEADERSHIP Hausa a ranar Alhamis, dan takarar, ya karyata labarin, ya kuma nuna bacin ransa tare da cewa kwata-kwata babu wanda ya tuntubesa kan wannan zance.

“Ina zaune a ofis ina ganawa da wasu sai aka fara kirana a waya ana tambayata, ya aka yi aka ji sunana cewa na koma PDP?

“Na ce ban gane ba, wace magana ce wannan?. Wasa gaske na amsa kiran waya kan wannan batun a lokacin sama da 100, inda magoya bayanmu suna nuna takaicinsu da nuna bacin ransu da jin wannan maganar.

Labarai Masu Nasaba

Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina

Rikici Ya Ɓarke A Zaɓen Ribas, Ƴan PDP Sun Fito A Matsayin Ƴan Takarar APC

“Gaskiya ni ban san da wannan batu ba kuma ba a yi wannan zancen da ni ba. Kuma ba mu shirya cewa zan sauya sheka na koma wata jam’iyya ba.

“Kowa ya ga yadda muka karbu a Jihar Bauchi, babu wani matashi kamata a duk ‘yan takarar nan, ni ne mai karancin shekaru kuma matasa suna alfahari da hakan. Sun kuma shirya wajen ganin nasu ya karbi mulki. Alhamdullahi muna kallon nasara domin tsakaninmu idan har aka yi zabe bisa gaskiya to ni zan ci, sai dai idan magudi za a yi.”

Ya ce, ya fito ya barranta kansa da wannan ikirarin da PDP da ‘yan takaranta suka yi a gaban dubban jama’a.

“Na rubuta wasika zuwa ga babban lauya na kasa kuma muna jiran amsarsa, domin ka san mai neman shugaban kasa zan yi kara Atiku Abubakar da Dino Melaye da ya kira sunana, da kuma shugaban jam’iyyar PDP na kasa Iyorchia Ayu, da shugaban PDP na Jihar Bauchi, Hamza Koshe Akuyam.”

Arewa, ya sha alwashin samun nasara a zaben gwamna na 11 ga watan Maris, 2023.

“Wannan bata suna ne baro-baro a matsayina na dan takarar gwamna da nake kallon zan ci zabe, yanzu a sakamakon wannan furucin da suka yi na rasa akalla kashi 30 na magoya bayana.

“Wani daga jin wannan batun shi ke nan ya tafi da shi a ransa ke nan, wani kuma zai ga tun farko yaudararsa aka yi, wani kuma zai ga ban kyauta wa masoyana ba, kowa da yadda zai dauki batun, don haka ba lamari ne da za mu bar shi haka nan ba.”

Arewa ya ce, kwata-kwata babu wata yarjejeniya da suka yi da gwamnatin Jihar Bauchi ko PDP kan cewa zai janye takararsa ba.

“Idan ma za mu janye ya kamata a ji nunfashinmu balle ma hakan baya daga cikin manufarmu. Shin an ma fito an fadi hakan a kan mu don an fi mu cancanta ne ko don rainin da aka mana? Ko kuma a’a fahimtarmu ce ta zo daya, amma babu haka kawai mutum ya tashi kawai ya ce mun janye neman takararmu hakan ba za ta yiwuwa ba.”

A kwafin wasikar da ZLP ta aike wa Lauyoyin ta ce, “Daukan matakin shari’ar shi ne zai dawo wa jam’iyyarmu da kima da mutuncinta kan yarfen da aka mana.”

Wasikar mai dauke da sanya hannun Ambasada Khalid Arewa, dan takarar gwamna na jam’iyyar, “Kwasam a ranar 7 ga watan Fabrairu, 2023 PDP-PCC ya kira sunan dan takarar gwamnanmu a jihar Bauchi, Ambasada Khalid Arewa da cewa ya koma jam’iyyar PDP, wannan furucin ya janyo mana asara sosai da jawo damuwa.”

“Tun lokacin da PDP ta fito ta yi wannan furucin, magoya baya da masoyan ZLP sun shiga damuwa sun kuma nuna rashin jin dadinsu a sassa daban-daban na kananan hukumomin jihar Bauchi.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ArewaBauchiSiyasaZLP
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ya Kamata Amurka Ta Sauya Mahangar Ta Game Da Sin

Next Post

Sin Ta Ba Da Agajin Kayayyakin Aikin Jinya Ga Syria

Related

Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina
Labarai

Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina

12 hours ago
Rikici Ya Ɓarke A Zaɓen Ribas, Ƴan PDP Sun Fito A Matsayin Ƴan Takarar APC
Siyasa

Rikici Ya Ɓarke A Zaɓen Ribas, Ƴan PDP Sun Fito A Matsayin Ƴan Takarar APC

16 hours ago
Sanata Buba Ya ƙaryata Jita-jitar Cewa Majalisa Ta Amince da ƙirƙiro Sabbin Jihohi 12
Siyasa

Sanata Buba Ya ƙaryata Jita-jitar Cewa Majalisa Ta Amince da ƙirƙiro Sabbin Jihohi 12

1 day ago
Sauya Sheƙa: Sanatoci Biyu APC Ke Buƙata Wajen Samun Kashi Biyu Cikin Uku A Majalisar Dattawa
Siyasa

Sauya Sheƙa: Sanatoci Biyu APC Ke Buƙata Wajen Samun Kashi Biyu Cikin Uku A Majalisar Dattawa

2 days ago
2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa
Siyasa

2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa

3 days ago
Majalisar Dokokin Sokoto Ta Aike Wa  Kwamishina Sammaci, Duba Dalili
Siyasa

Majalisar Dokokin Sokoto Ta Aike Wa  Kwamishina Sammaci, Duba Dalili

3 days ago
Next Post
Sin Ta Ba Da Agajin Kayayyakin Aikin Jinya Ga Syria

Sin Ta Ba Da Agajin Kayayyakin Aikin Jinya Ga Syria

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Kano Za Ta Mayar Da Gidan Gyaran Hali Na Kurmawa Gidan Tarihi

Gwamnatin Kano Za Ta Mayar Da Gidan Gyaran Hali Na Kurmawa Gidan Tarihi

August 4, 2025
Kashe N712bn Kan Gyaran Filin Jiragen Saman Legas Rashin Sanin Ya Kamata Ne – ADC 

Kashe N712bn Kan Gyaran Filin Jiragen Saman Legas Rashin Sanin Ya Kamata Ne – ADC 

August 4, 2025
Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina

Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina

August 3, 2025
Sanata Shehu Buba Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Da Rigakafin Shanu A Bauchi

Sanata Shehu Buba Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Da Rigakafin Shanu A Bauchi

August 3, 2025
Waɗanne Ƙasashe Ne Suka Amince Da Kafa Ƙasar Falasɗinu?

Waɗanne Ƙasashe Ne Suka Amince Da Kafa Ƙasar Falasɗinu?

August 3, 2025
Dangote Ya Ɗauki Nauyin Bikin Baje Kolin Gidajen Afrika Da Mahalarta Ƙasashe 21

Dangote Ya Ɗauki Nauyin Bikin Baje Kolin Gidajen Afrika Da Mahalarta Ƙasashe 21

August 3, 2025
An Fara Bayar Da Hidimomin Da Suka Shafi Sauka Da Tashi Domin Gasar Wasanni Ta Duniya Ta Chengdu

An Fara Bayar Da Hidimomin Da Suka Shafi Sauka Da Tashi Domin Gasar Wasanni Ta Duniya Ta Chengdu

August 3, 2025
Rikici Ya Ɓarke A Zaɓen Ribas, Ƴan PDP Sun Fito A Matsayin Ƴan Takarar APC

Rikici Ya Ɓarke A Zaɓen Ribas, Ƴan PDP Sun Fito A Matsayin Ƴan Takarar APC

August 3, 2025
Ana Gaggauta Ayyukan Gyara Tituna Da Gadojin Da Ambaliya Ta Lalata A Arewacin Kasar Sin

Ana Gaggauta Ayyukan Gyara Tituna Da Gadojin Da Ambaliya Ta Lalata A Arewacin Kasar Sin

August 3, 2025
Shugabar Tanzania Ta Kaddamar Da Cibiyar Cinikayya Da Jigila Da Sin Ta Gina A Kasar

Shugabar Tanzania Ta Kaddamar Da Cibiyar Cinikayya Da Jigila Da Sin Ta Gina A Kasar

August 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.