• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dannau Ba Matsalar Aljanu Ba Ce, Aikin Kwakwalwa Ne -Dakta Maryam (Adon Gari)

by Najib Sani
3 years ago
in Rahotonni
0
maryam
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wata masaniyar aikin likitanci ‘yar asalin Jihar Bauchi da ke zaune a Birnin Tarayya Abuja, Dakta Maryam Almustapha ta warware tunanin da jama’a da dama ke yi na cewa matsalar Dannau a lokacin tashi daga bacci aljanu ne ke haifar da shi, wanda ake ganin kamar aljanu ne ke danne mutum, tana mai nuni da cewa matsala ce da kwakwalwa ke haddasawa.

A hirar da ta yi da jaridar LEADERSHIP, Dakta Maryam ta bayyana cewa matsalar Dannau tana sanya mutum ya kasa motsi a lokacin da ya farka daga bacci, wanda hakan kai tsaye aikin kwakwalwa ne da tsokokin jiki (Muscles).

  • A Nijeriya Idan Ka Ce Za Ka Rike Aikin Gwamnati Shi Kadai Akwai Kalubale – Fatima (Adon Gari)

Ta ce matsalar wacce take iya firgita wanda ya samu kansa a ciki, ta kan saka mutum ba kawai ya kasa motsi ba, har ma ya gagara numfashi duk da cewa yana farke a gadonsa kuma yana cikin hankalinsa.

“Matsala ce da ta kan auku ga mutane da yawa wacce kan sa mutum ya kasa motsi, yin numfashi da kuma gane-gane da jiye-jiye”, in ji ta.

Ta ce matsalar za ta iya faruwa ga mutum kafin ya yi bacci ko bayan ya farka kuma za ta iya daukar dakikoki ko wasu mintuna kafin ya saki mutum, tana mai karawa da cewa Dannau ya zamo ruwan dare cikin al’umma yadda in ka samu mutum 100, akalla mutum hudu su kan fuskanci matsalar daga lokaci zuwa lokaci.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

Dadin dadawa, Dakta Maryam ta ce bacci ya kasu kashi biyu; da bacci mai nauyi da ake kira da ‘REM sleep’ da mara nauyi wanda ake kira da ‘non REM sleep’ a turance.

maryam
Dakta Maryam

Masaniyar aikin likitancin ta cigaba da cewa a lokacin bacci mai nauyi ne mutane suke mafarki wanda yake sanya kwakwalwa ta kashe tsokokin jiki don hana mutum ya buga jikinsa ko kuma ya fado kasa daga gado sakamakon motsawar jikinsa lokacin da yake mafarki.

Maryam ta ce matsalar Dannau ta kan faru ne idan kwakwalwa ta ki kunna tsokokin jiki don su cigaba da motsi bayan mutum ya farka daga bacci, sannan kuma ba a gano hakikanin abin da yake janyo matsalar Dannau ba lokacin farkawa daga bacci.

Sai dai ta ce wasu daga cikin abubuwan da suke janyo matsalar sun hada da mutum ya yi bacci a kan bayansa, rashin yin bacci akai-akai, shan giya da sauran kayan da suke sa maye, yin gadon matsalar daga dangi, gajiya, damuwa, da tsoro za su iya haddasa ta.

Da take bayyana cewa Dannau baya da magani, akwai abubuwan da in mutum ya kiyaye zai guje wa fuskantar matsalar.

Abubuwan sun hada da daina kwanciya ta baya, kauracewa wa shan giya, yin bacci akai-akai, yin bacci lokacin da ka saba yi, samun isasshen bacci kamar awa shida zuwa takwas ko wace rana, kashe wuta da rage sauti mai hana bacci lokacin da mutum zai kwanta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Za A Hana ‘Yan Kasar Waje Sayen Amfanin Gona Kai-tsaye A Gonaki

Next Post

Masarautar Bwari Jiya Da Yau

Related

Ahlul Faidhati Mai Diwani Group
Rahotonni

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

5 days ago
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Rahotonni

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

1 week ago
Arewa
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Gwamnonin Arewa Sun Bullo Da Sabbin Matakan Yaki Da Ta’addanci

1 week ago
'Yan Bindiga
Rahotonni

Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Haifar Da Da Mai Ido A Katsina

2 weeks ago
Gidauniyar ‘Ya’yan Sarakunan Arewa Sun Marawa Sarkin Musulmi A Matsayin Shugaban Majalisar Sarakuna
Rahotonni

Babban Taron Lauyoyi Na Kasa: Sarkin Musulmi Ya Gargadi Alkalai Kan Tabbatar Da Adalci

3 weeks ago
Sin Ta Fara Amfani Da Tauraron Dan Adam Wajen Duba Manyan Hanyoyin Wutar Lantarki A Karo Na Farko
Rahotonni

Cire Tallafin Wutar Lantarki Zai Kara Kuntata Rayuwar ‘Yan Nijeriya – Kungiyar Kwadago

3 weeks ago
Next Post
bwari

Masarautar Bwari Jiya Da Yau

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

September 17, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja

September 17, 2025
Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

September 17, 2025
Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

September 17, 2025
Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

September 17, 2025
Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

September 16, 2025
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

September 16, 2025
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

September 16, 2025
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

September 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.