• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dannau Ba Matsalar Aljanu Ba Ce, Aikin Kwakwalwa Ne -Dakta Maryam (Adon Gari)

byNajib Sani
3 years ago
maryam

Wata masaniyar aikin likitanci ‘yar asalin Jihar Bauchi da ke zaune a Birnin Tarayya Abuja, Dakta Maryam Almustapha ta warware tunanin da jama’a da dama ke yi na cewa matsalar Dannau a lokacin tashi daga bacci aljanu ne ke haifar da shi, wanda ake ganin kamar aljanu ne ke danne mutum, tana mai nuni da cewa matsala ce da kwakwalwa ke haddasawa.

A hirar da ta yi da jaridar LEADERSHIP, Dakta Maryam ta bayyana cewa matsalar Dannau tana sanya mutum ya kasa motsi a lokacin da ya farka daga bacci, wanda hakan kai tsaye aikin kwakwalwa ne da tsokokin jiki (Muscles).

  • A Nijeriya Idan Ka Ce Za Ka Rike Aikin Gwamnati Shi Kadai Akwai Kalubale – Fatima (Adon Gari)

Ta ce matsalar wacce take iya firgita wanda ya samu kansa a ciki, ta kan saka mutum ba kawai ya kasa motsi ba, har ma ya gagara numfashi duk da cewa yana farke a gadonsa kuma yana cikin hankalinsa.

“Matsala ce da ta kan auku ga mutane da yawa wacce kan sa mutum ya kasa motsi, yin numfashi da kuma gane-gane da jiye-jiye”, in ji ta.

Ta ce matsalar za ta iya faruwa ga mutum kafin ya yi bacci ko bayan ya farka kuma za ta iya daukar dakikoki ko wasu mintuna kafin ya saki mutum, tana mai karawa da cewa Dannau ya zamo ruwan dare cikin al’umma yadda in ka samu mutum 100, akalla mutum hudu su kan fuskanci matsalar daga lokaci zuwa lokaci.

LABARAI MASU NASABA

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya

Dadin dadawa, Dakta Maryam ta ce bacci ya kasu kashi biyu; da bacci mai nauyi da ake kira da ‘REM sleep’ da mara nauyi wanda ake kira da ‘non REM sleep’ a turance.

maryam
Dakta Maryam

Masaniyar aikin likitancin ta cigaba da cewa a lokacin bacci mai nauyi ne mutane suke mafarki wanda yake sanya kwakwalwa ta kashe tsokokin jiki don hana mutum ya buga jikinsa ko kuma ya fado kasa daga gado sakamakon motsawar jikinsa lokacin da yake mafarki.

Maryam ta ce matsalar Dannau ta kan faru ne idan kwakwalwa ta ki kunna tsokokin jiki don su cigaba da motsi bayan mutum ya farka daga bacci, sannan kuma ba a gano hakikanin abin da yake janyo matsalar Dannau ba lokacin farkawa daga bacci.

Sai dai ta ce wasu daga cikin abubuwan da suke janyo matsalar sun hada da mutum ya yi bacci a kan bayansa, rashin yin bacci akai-akai, shan giya da sauran kayan da suke sa maye, yin gadon matsalar daga dangi, gajiya, damuwa, da tsoro za su iya haddasa ta.

Da take bayyana cewa Dannau baya da magani, akwai abubuwan da in mutum ya kiyaye zai guje wa fuskantar matsalar.

Abubuwan sun hada da daina kwanciya ta baya, kauracewa wa shan giya, yin bacci akai-akai, yin bacci lokacin da ka saba yi, samun isasshen bacci kamar awa shida zuwa takwas ko wace rana, kashe wuta da rage sauti mai hana bacci lokacin da mutum zai kwanta.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya
Rahotonni

Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya

October 4, 2025
Bashin Karatun Dalibai: Arewa Maso Yamma Ce Kan Gaba Wajen Cin Gajiyar Shirin
Rahotonni

Bashin Karatun Dalibai: Arewa Maso Yamma Ce Kan Gaba Wajen Cin Gajiyar Shirin

October 3, 2025
Next Post
bwari

Masarautar Bwari Jiya Da Yau

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version