ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masarautar Bwari Jiya Da Yau

by Idris Umar
4 years ago
bwari

A ranar Asabar din nan ne ake bai wa mai martaba Sarkin Bwari, Alhaji Awwal Musa Ijakoro sandan girma.

Bikin bayar da sandan girman wanda Ministan Babban Birnin Tarayya Abuja, Mohammed Musa Bello zai shugabanta, zai gudana ne a Cibiyar Bunkasa Al’amuran Mata da ke Kuduru a yankin Bwari da ke Abuja.

  • Martanin Wike Ga Lamido: Ba Ka Da Sauran Wata Kima A Siyasa

Wanda ake sa ran farawa daga karfe 11 na safe, bikin zai samu halartar manyan baki da suka kunshi sarakuna, shugabannin siyasa da na al’umma da kuma sauran masu ruwa da tsaki.

ADVERTISEMENT

Shin wanene mai martaba Alhaji Awwal Musa Ijakoro?
Mai girma Alhaji Awwal Musa Ijakoro, wani bawan Allah ne da za a ce al’ummar kasar Bwari da ke Abuja suka yi sa’ar samu a cikinsu kuma har ya zama sarki. Wannan duk yana daga cikin hikimar Allah.

Koda yake ya fito ne daga gidan sarauta tun asali, amma tun kafin ya zama sarki al’ummar kasar Bwari da dama suke girmama shi a matsayin shugaba wanda yeke da tausayin jama’a, kwarjini da ilmin sanin yadda ake zama lafiya da al’umma kamar yadda ya taso ya ga mahaifinsa na yi.

LABARAI MASU NASABA

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja

Tarihi ya nuna cewa an haifi mai martaba Alhaji Awwal Musa Ijakoro ne a garin Bwari da ke Babban Birnin Tarayya Abuja, a ranar 9 ga watan Yunin shekarar 1977.

A ranar 24 ga watan Oktobar 2017 ne Ministan Abuja, Malam Mohammed Musa Bello ya nada Alhaji Awwal Musa Ijakoro a matsayin sabon Sarkin Bwari domin ya gaji mahaifinsa, Alhaji Muhammad Musa Ijakoro, da ya riga mu gidan gaskiya a ranar 29 ga Agustan 2017.

A hannun mahaifisa Alhaji Musa Muhammad Ijakoro ne masarautar ta zama mai daraja ta biyu a ranar 12 ga watan Yunin 1997.

Bincike ya nuna daukakar da masarautar tasu ta samu ta biyo bayan umurnin da marigayi shugaban kasa Janar Sani Abacha ya bai wa ministan Abuja na wancan lokacin ne Laftanar Janar Jeremiah Useni, da ya kara daukaka jdarajar masarautun da ke Birnin Tarayya Abuja.

A shekarun da mai martaba Alhaji Awwal Musa Ijakoro ya yi a kan karaga ya samu nasarar hada kan al’umarsa waje guda wanda hakan ya kawo zaman lafiya da daukaka a masarautar baki daya.

Dangane da batun ilmi kuma mai martaba Alhaji Awwal Musa Iajkoro ya yi karatun firamere ne a Suleja a shekarar 1984 zuwa 1989 a makarantar da ake kira Aliyu Wali. Sannan ya yi karatun sakandare a Makarantar GSS Kwali Abuja inda ya kammala a 1997.

Daga 2001 zuwa 2003 mai martaba ya yi karatun difuloma a kan harkokin gwamnati a Jami’ar Abuja wanda daga nan ne aka fara nada shi sarauta.

Ya kuma yi digiri a kan harkokin mulki (B.Sc Public Administration) a Jami’ar Nasarawa da ke Keffi. Kafin zaman sa Sarkin Bwari dai an nada shi Ciroman Bwari.

Ya yi aikin gwamnati musamman a makarantar Shari’a ta Nijeriya reshen Bwari daga 2000 zuwa 2010.

Kamar yadda Jagaban Shere Koro, Bala Ahmad Shere ya taba bayyana wa jaridar Daily Trust, “An daga darajar masarautar Bwari sama da shekara 25 da suka gabata tare da wasu hakimai na Birnin Tarayya Abuja.

Sun hada da Gundumomin Kwali da Kuje da sauran wasu masarautu na dagatai.
“Marigayi Dr. Musa Muhammad Ijakoro ya kasance wani basarake na daban a tsakanin wadanda suka mulki Bwari tun daga 1902 zuwa 1975. Bwari tana da dagatai guda 10 wadanda su ne suke zaben hakimi a Gundumar Bwari. Kuma a cikin wadannan dagatai akwai Koro, kuma akwai Gwari.”

Shi ma da yake jawabi, Ciroman Bwari, Abubakar Musa Ijakoro, ya bayyana cewa, biyo bayan ritayar dole da Gwamnan Soja na Jihar Arewa maso Yamma, Kwamishinan ‘yan sanda, Usman Faruk, ya yi wa Hakimin Bwari, Abubakar Barau Musa Angulu, a tsakanin shekarar 1954 zuwa 1975, an yi dokar soja da ta bayar da umurnin cewa a nada ‘yan asalin yanki a mukaman sarauta a gurabun da aka samar.

Ya ce yayin da aka bayar da damar fitowa domin neman kujerar Hakimin Bwari wadanda suka nema “sun hada da Malam Danladi Zuma – daga Bwari (Gbagyi), Samaila Mainasara – daga Ija-Gbagyi (Gbagyi), Salihu Sunbwada – daga Diko (Gbagyi), da Musa Muhammad – daga Ijakoro (Koro).

Ya yi nuni da cewa yayin da shugabannin kauyen Koro suka gabatar da dan takara daya tilo, sai su Gbagyi suka gabatar da ‘yan takara uku wadanda Ijakoro ya kayar da su.

“A halin da ake ciki, ya kamata duk duniya su sani cewa gundumar Bwari ba kawai ta kunshi Gbagyi da Koro da Hausawa da Fulani ne kadai ba. An kafa Zangon Hausawa na Bwari sama da shekara 89 kafin a tilasta wa Gbagyi su sauko daga tsauni.

“Hakazalika, muna so mu bayyana baro-baro a nan cewa Koro ya yi hijira zuwa Abuja da wuri tun kafin Gbagyi. Bisa ga takardun tarihi, duk inda ka ga Gbagyi, tabbas sun zo ne bayan Koro. Kuma sun girmama Koro. Shi ya sa Gbagyi kawai suke kiran Koro da ‘Apoyi’, ma’ana mai ceton rai.

Sarakunan Koro ne suka yi wa sarakunan Gbagyi rawani, wanda ke nufin sun kasance talakawan Koro a tsawon tarihin masarautar Abuja.

“Kafin zuwan ’yan mulkin mallaka da kuma bayan da Nijeriya ta samu ‘yancin kai a 1960; a koyaushe Dagacin Bwari ne yake nada Sarkin Dogon Kurmi.

Hakazalika, Hakimin kauyen Ushafa ya kasance Sarkin Ijakoro ne yake nada masa rawani,” ya bayyana.

Ciroman Bwari ya kuma ce dukkan abubuwan tarihi ko alamomin da ke Abuja mallakin Koro ne, ba wai Gwari da ke ikirarin mallakin Abuja ba.

Ya yi ikirarin cewa shahararren dutsen Aso Rock da Zuma Rock mallakin Koro ne. “Ko kuwa akwai wani Gbagyi da zai iya yin da’awar wadannan alamomin?” Ya tambaya.

Yayin hada wannan labarin ne kuma muka sami labarin rasuwar mahaifiyar mai martaba Alhaji Awwal Musa, da fatan Allah ya rahamshe ta, Allah ya bai wa mai martaba da sauran iyalanta hakurin jure rashin.

Bwari
Idris Umar
+ postsBio
  • Idris Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-umar/
    Sanata Shehu Sani Ya Nemi Gwamnonin Arewa Su Tallafa Wa Bikin Al’adu Na ABU Zariya
  • Idris Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-umar/
    Yadda Dakta A’isha Mustapha Ta Zama Shugabar Ƙungiyar Likitocin Jihar Kaduna
  • Idris Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-umar/
    Kafafen Sadarwa Na Zamani Wuri Ne Na Bunƙasa Tattalin Arziƙi — Ubale Kiru
  • Idris Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-umar/
    Kungiyar Daliban Jami’ar ABU Ta Gudanar Gasar Girke-girken Abincin Gargajiya A Bude Bikin Al’adu Na Bana

MASU ALAKA

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu
Rahotonni

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Gwamnatin Neja Ta Bayar Da Umarnin Kawo Karshen Matsalar Tsaro
Rahotonni

Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja

September 5, 2026
Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed
Rahotonni

Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed

September 5, 2026
Next Post
Yadda ‘Yan Kasuwar Kwari Ke Tafka Asara Saboda Ambaliyar Ruwa A Kano

Yadda 'Yan Kasuwar Kwari Ke Tafka Asara Saboda Ambaliyar Ruwa A Kano

LABARAI MASU NASABA

Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

September 10, 2026
Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

September 10, 2026
Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

September 10, 2026
Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

September 10, 2026
Bwari

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
Bwari

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.