ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dannau Ba Matsalar Aljanu Ba Ce, Aikin Kwakwalwa Ne -Dakta Maryam (Adon Gari)

by Najib Sani
4 years ago
maryam

Wata masaniyar aikin likitanci ‘yar asalin Jihar Bauchi da ke zaune a Birnin Tarayya Abuja, Dakta Maryam Almustapha ta warware tunanin da jama’a da dama ke yi na cewa matsalar Dannau a lokacin tashi daga bacci aljanu ne ke haifar da shi, wanda ake ganin kamar aljanu ne ke danne mutum, tana mai nuni da cewa matsala ce da kwakwalwa ke haddasawa.

A hirar da ta yi da jaridar LEADERSHIP, Dakta Maryam ta bayyana cewa matsalar Dannau tana sanya mutum ya kasa motsi a lokacin da ya farka daga bacci, wanda hakan kai tsaye aikin kwakwalwa ne da tsokokin jiki (Muscles).

  • A Nijeriya Idan Ka Ce Za Ka Rike Aikin Gwamnati Shi Kadai Akwai Kalubale – Fatima (Adon Gari)

Ta ce matsalar wacce take iya firgita wanda ya samu kansa a ciki, ta kan saka mutum ba kawai ya kasa motsi ba, har ma ya gagara numfashi duk da cewa yana farke a gadonsa kuma yana cikin hankalinsa.

ADVERTISEMENT

“Matsala ce da ta kan auku ga mutane da yawa wacce kan sa mutum ya kasa motsi, yin numfashi da kuma gane-gane da jiye-jiye”, in ji ta.

Ta ce matsalar za ta iya faruwa ga mutum kafin ya yi bacci ko bayan ya farka kuma za ta iya daukar dakikoki ko wasu mintuna kafin ya saki mutum, tana mai karawa da cewa Dannau ya zamo ruwan dare cikin al’umma yadda in ka samu mutum 100, akalla mutum hudu su kan fuskanci matsalar daga lokaci zuwa lokaci.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

Me Kashim Imam Ke Yi A Yanzu?

Dadin dadawa, Dakta Maryam ta ce bacci ya kasu kashi biyu; da bacci mai nauyi da ake kira da ‘REM sleep’ da mara nauyi wanda ake kira da ‘non REM sleep’ a turance.

maryam
Dakta Maryam

Masaniyar aikin likitancin ta cigaba da cewa a lokacin bacci mai nauyi ne mutane suke mafarki wanda yake sanya kwakwalwa ta kashe tsokokin jiki don hana mutum ya buga jikinsa ko kuma ya fado kasa daga gado sakamakon motsawar jikinsa lokacin da yake mafarki.

Maryam ta ce matsalar Dannau ta kan faru ne idan kwakwalwa ta ki kunna tsokokin jiki don su cigaba da motsi bayan mutum ya farka daga bacci, sannan kuma ba a gano hakikanin abin da yake janyo matsalar Dannau ba lokacin farkawa daga bacci.

Sai dai ta ce wasu daga cikin abubuwan da suke janyo matsalar sun hada da mutum ya yi bacci a kan bayansa, rashin yin bacci akai-akai, shan giya da sauran kayan da suke sa maye, yin gadon matsalar daga dangi, gajiya, damuwa, da tsoro za su iya haddasa ta.

Da take bayyana cewa Dannau baya da magani, akwai abubuwan da in mutum ya kiyaye zai guje wa fuskantar matsalar.

Abubuwan sun hada da daina kwanciya ta baya, kauracewa wa shan giya, yin bacci akai-akai, yin bacci lokacin da ka saba yi, samun isasshen bacci kamar awa shida zuwa takwas ko wace rana, kashe wuta da rage sauti mai hana bacci lokacin da mutum zai kwanta.

maryam
Najib Sani
+ postsBio
  • Najib Sani
    https://hausa.leadership.ng/author/najib-sani/
    Kur’ani Bai Halatta Cin Naman Kare Ba-Sheikh Masussuka
  • Najib Sani
    https://hausa.leadership.ng/author/najib-sani/
    Yajin Aikin ASUU: Malamin Jami’a Ya Yi Barazanar Ajiye Aiki Kan Rashin Albashi

MASU ALAKA

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya
Rahotonni

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

June 13, 2026
Me Kashim Imam Ke Yi A Yanzu?
Rahotonni

Me Kashim Imam Ke Yi A Yanzu?

June 8, 2026
Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana
Rahotonni

Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana

June 6, 2026
Next Post
bwari

Masarautar Bwari Jiya Da Yau

LABARAI MASU NASABA

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

June 13, 2026
Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

June 13, 2026
Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

June 13, 2026
Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

June 12, 2026
Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

June 12, 2026
Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

June 12, 2026
Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

June 12, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.