ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dare Daya Allah Kan Yi Bature: Yadda Adam Zango Ya Zama Daraktan Gidan Qausain TB

by Rabilu Sanusi Bena
2 years ago
Adam

Kwanakin baya Gidan Talabijin na Kausain TB wanda yake daya daga cikin rukunin kamfanonin Kauisain ya bayyana wasu sabbin nade naden da ya yi domin su jagoranci kamfanin a bangarori da dama, a cikin sanarwar Kausain TB ta ce ta nada fitaccen jarumin fina-finan Kannywood kuma mawaki Adam A. Zango a matsayin Darakta Janar na gidan Talabijin din.

Shugaban kungiyar Kausain, Alh Nasir Idris, a wata sanarwa a ranar a Abuja, ya bayyana cewa nadin Adam Zango a matsayin Darakta Janar ya fara aiki nan take, a cewar sanarwar an amince da nadin ne yayin wani taron kwamitin gudanarwar kamfanin da aka gudanar.

  • Gyaran Mama Ga Matan Da Suka Haihu
  • An Gudanar Da Zaɓen Ƙananan Hukumomi Cikin Kwanciyar Hankali A Kaduna – Gwamna Sani

Malam Idris ya kara da cewa an nada tsohon Gwamnan Soja na Jihar Kano, Kanar Sani Bello (mai ritaya) a matsayin Shugaban Amintattun kamfanin, ya kuma ce an nada tsohon ministan sadarwa, kirkire-kirkire da tattalin arzikin dijital, Farfesa Isa Pantami a matsayin Darakta mai zaman kansa, sai kuma nadin da aka yiwa tsohon mai watsa shirye-shiryen sashen Hausa na BBC, Ahmad Abdullahi a matsayin Darakta mara zartarwa.

ADVERTISEMENT

Ya ce nadin nasu ya zo ne bayan dogon nazari da hangen nesa ta inda ake fatan dukkansu za su hada kai wajen bayar da shawarwarin da suka dace wajen ciyar da kamfani gaba duba da cewa dukkansu kwararru ne a wannan harka.

Ayyukansa sun hada tsare tsare ga Kausain TB, samar da sabbin dabaru wajen gudanar da kamfani da kuma kawo sauye sauye a bangaren tallace tallace na kamfani inji shi.

LABARAI MASU NASABA

Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

Ya bukaci wadanda aka nada da su yi amfani da kwarewarsu wajen ciyar da kamfanin gaba inda ya ce, muna da tabbacin cewa kwarewarku da zurfin fahimtar ku za su taimaka wajen ciyar da kamfanin gaba da kuma samun manyan nasarori in ji shi.

Nan take bayan wannan sanarwar jarumi Adam Zango kuma sabon Darakta Janar na Kausain TB ya wallafa a shafinsa na Facebook domin yan uwa da abokan arziki su taya shi murna akan wannan sabon mukami da ya samu, daga cikin wadanda suka taya shi murna akwai shugaban hukumar Fina Finai ta Nijeriya Ali Nuhu Muhammad wanda ya yi mashi fatan alheri da addu’ar samun nasara.

Adam
Rabilu Sanusi Bena
+ postsBio
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Messi Da Mbappé Na Jagorantar Cin Ƙwallaye A Gasar Kofin Duniya

MASU ALAKA

Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina
Nishadi

Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina

June 14, 2026
Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi
Nishadi

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

June 14, 2026
Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro
Nishadi

Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro

May 31, 2026
Next Post
Bai Kamata Mutum Ya Dogara Da Harkar Fim Kadai Ba -Hamza Talle Mai Fata

Bai Kamata Mutum Ya Dogara Da Harkar Fim Kadai Ba -Hamza Talle Mai Fata

LABARAI MASU NASABA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Yadda Jana’izar Ruhullah Khomeini Ta Shiga Kundin Tarihi Na Guinness

July 10, 2026
NIMC Ta Yi Haɗin Gwuiwa Da Ma’aikatun Gwamnati Don Faɗaɗa Rajistar NIN

NIMC Ta Yi Haɗin Gwuiwa Da Ma’aikatun Gwamnati Don Faɗaɗa Rajistar NIN

July 10, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

“Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

July 10, 2026
Falalar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW

Falalar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW

July 10, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

July 10, 2026
Shugaban Miyetti Allah, Bodejo Ya Karyata Zargin Halatta Kudin Haram A Zaman Kotu

Shugaban Miyetti Allah, Bodejo Ya Karyata Zargin Halatta Kudin Haram A Zaman Kotu

July 10, 2026
Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisar Kan Gyaran Kudirin Dokar Shari’ar Manyan Laifuka

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisar Kan Gyaran Kudirin Dokar Shari’ar Manyan Laifuka

July 10, 2026
Taƙaddamar Kafa Hukumar Bogi: Tinubu Ya Umarci A Yi Binciken Ƙwaƙwaf

Taƙaddamar Kafa Hukumar Bogi: Tinubu Ya Umarci A Yi Binciken Ƙwaƙwaf

July 10, 2026
Ana Ci Gaba Da Tafka Muhawara Kan Shirin Gwamnati Na Haramta Masana’atun Sarrafa Robobi

Ana Ci Gaba Da Tafka Muhawara Kan Shirin Gwamnati Na Haramta Masana’atun Sarrafa Robobi

July 10, 2026
Asusun IMF Ya Rage Hasashen Bunkasar Tattalin Arzikin Duniya, Ya Kuma Kara Na Sin

Asusun IMF Ya Rage Hasashen Bunkasar Tattalin Arzikin Duniya, Ya Kuma Kara Na Sin

July 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.