• English
  • Business News
Saturday, May 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (2): Kyawawan Dabi’u Ke Fayyace Tsoron Allah A Musulunci

by Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
1 month ago
in Dausayin Musulunci
0
Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (2): Kyawawan Dabi’u Ke Fayyace Tsoron Allah A Musulunci
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Alhamadu lillah. Masu karatu assalamu alaikum wa rahmatullahi ta’ala wa barkatuh. Da fatan muna nan cikin koshin lafiya, Allah ya bai wa marasa lafiyarmu na gida asibiti koshin lafiya, ya kawo mana karin zaman kafiya a kasashenmu da duk duniya baki daya. Za mu kawo kashi na biyu na darussan da masu bibiya suka zakulo suka rubuto daga fahimtarsu game da zaman tafsirin da muka gabatar a Zawiyyarmu ta Ahlul Faidhati Mai Diwani Group da ke Kaduna, a watan azumin Ramadan da ya gabata.

-Kyawawan Dabi’u Ke Fayyace Tsoron Allah A Musulunci

  • Hakuri Da Baiwa (Kyautar) Manzon Allah (SAW)
  • Wasu Ruwayoyi Game Da Yafiyar Manzon Allah (SAW)

Assalamu alaikum wa rahmtullah. Ya Sayyadi barkanmu da war haka, da fatan an yi sallah lafiya, Allah ya maimaita mana amin. Da farko muna mika godiya game da koyarwar da aka yi mana a zaman tafsirin bana wanda muka bibiya a kusan kullum, alhamdu lillah. Bayanan da kuka yi game da yadda littafan annabta da suka kunshi hukunce-hukunce da kuma alluna guda goman nan da Allah ya zabar ma Annabi Musa (AS) kuma suka zama hikima ga Annabi Isa (AS), sannan suka zama Furkanu ga Annabi Muhammad (SAW), sun nuna mana yadda Allah ya aiko annabawa a kan zuri guda na asali. Haka zalika, misalan da kuka bayar game da bambanci tsakanin takawar Musulunci (kyawawan dabi’u) da kuma takawar Imani (aiki gwargwadon iko) sun kara tabbatar mana da cewa duk wanda ya kasance mai tsoron Allah, za a same shi da kyawawan dabi’u.

A kan wannan gabar, ya kamata malamanmu su kara himma da yin kira ga al’ummar musulmi a kan mu muhimmanta yin adalci da kuma kyautata fahimta tsakanin mu musulmi da mabiyan sauran addinai. Kuma musamman su kansu Malamanmu na Musulunci ya kamata su guje ma saurin yanke hukunci ga al’umma, domin wanda ya kawo addinin, Manzon Allah (SAW) ya ce ya zo ne domin ya cika kyawawan dabi’u, don haka duk yawan karatun malami idan ba shi da kyawawan halaye to kuwa za a ga barna tana biyo baya. Hadisin da ka kawo na cewa, cikakken Musulmi shi ne wanda ‘yan’uwansa Musulmai suka kubuta daga cutarwar hannunsa da bakinsa, ya nuna mana cewa musulmi na kirki yana aikata tabbatattun abubuwa na ibadu kamar Sallah da Azumi amma kuma mu sani ba su ne kadai ba, dole a hada da kyawawan dabi’u kamar yadda muka gani daga Annabi (SAW). Allah ya ba mu ikon gyara halayenmu musamman ma a wannan zamanin. Jazakumullahu khairan

Sako daaga Salisu Usman Gombe

Labarai Masu Nasaba

Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (1)

Abubuwan Da Aka Haramta Wa Mahajjaci

 

-Mun lura da ilimomin harkokin zamaninmu a cikin Alkur’ani

Cikin godiyar Allah, muna mika ziyara ga Shehu Isma’ila Umar Almadda (Mai Diwani) da kuma ban gajiya da gabatar da Tafsirin Alkur’ani mai girma na Azumin Ramadan na bana. Allah ya kai mu na badi albarkar Annabi (SAW) da Shehu (RTA).

Ya Shehi, a Tafsirinka na rana ta bakwai mun ji yadda ka yi bayani na ilimomin kiyaye hadurran hanya da ke kunshe a cikin aya ta 63 ta Suratul Furkan (Sura ta 25), “Wa Ibadur Rahman…”.

Mun kara fahimtar cewa, ayar tana nusarwa a kan tafiya cikin tsari walau sufuri ne na titin mota, ko na jirgin sama ko na ruwa ko jirgin kasa, da dukkan alamomin da ake sakawa na gane hanya da kiyaye aukuwar hadurra na ganganci da sauran ilimomin da suka kunshi dokokin hanya, duka suna nan a karkashin fahimtar ayar. Allah ya saka da alkhairi.

Game da sunan Allah na “Arrahmanu” kuwa, ya kara nuna mana cewa ya kunshi kowane ilimi. Kuma duk masana na sunan na “Arrahmanu” su ne suke zama kwararru na kowane fanni da ke tafiya a kan kasa cikin ilimi da kwarewa. Wallahi, wannan yana nuna mana cewa, mu al’umma musamman ta musulmi mu dage da neman ilimi na kowane fanni saboda inganta rayuwa da aiki da ilimin wajen nuna sanin ya kamata.

Daga misalan da ka kawo na batun hanya, na fahimci cewa, idan alamar hanya ta jar danja ta tsayar da direba shi kuma ya ki tsayawa, ya nuna jahilci ko rashin aiki da ilimin, wanda hakan ne yake sa jami’an da abin ya shafa suke hukunta direbobi masu karya dokokin hanya. Su kuma jami’an, yadda suke fara tambayar mai laifin a game da shin yana da lasisin tuki domin tantance cewa, shi a cikin “Ibadur Rahman” yake ko kuma jahili ne. Idan jahili ne hukuncinsa daban, idan kuma wanda ya san abin ne, watau yana daga cikin “Ibadur Rahman”, har yana da lasisi to hukuncinsa ma yakan fi tsanani, duka ya fahimtar da mu cewa muna da komai a cikin Alkur’ani.

Allah ya saka maka da alheri bisa yadda kuma ka karfafa gwiwar masu mulki har ma da magidanta a kan koyar da duk wadanda suke karkashinsu ilimi, domin tabbas jahilci tamkar mutuwa yake. Idan an ba mutane ilimi shi ne zai zama an raya su, haka nan idan an bar su da jahilci to kuma babu makawa an kashe su.

Muna godiya ya Shehi, Allah ya kara lafiya da nisan kwana.

 

-Tabbas Ya Kamata Mu Zurfafa Bincikenmu A Cikin Alkur’ani Domin Samun Ci Gaba

Assalamu alaikum. Ya Sayyadi barkanmu da kammala watan Azumin Ramadan, Allah ya amsa ibadunmu ya sa muna cikin ‘yantattun da aka ‘yantar, amin. Hakika bayanin da ka yi a kan yadda ya kamata mu al’ummar musulmi mu kara zurfafa bincike a cikin Alkur’ani domin samar da ci gaban zamani da ake gani a ko ina cikin duniya babban lamari ne mai matukar muhimmanci da ya kamata kasashenmu na musulmi mu mayar da hankali a kai.

Musamman ma, mu kasashen Afirka da muka zama koma baya idan aka kwatanta da sauran yankuna na duniya, ya kamata mu su sake nazarin wayewar zamani da ke kunshe cikin Alkur’ani, wanda hakan zai sanya mu iya yin kafada-da-kafada da manyan kasashen duniya irin su Amurka da China ta fannin ci gaban zamani.

Duk wanda ya san tarihi da kuma ilimi, ya san cewa duk bayanan da wadannan kasashen da suka ci gaba suke takama da su da kundayen da suka mallaka na bayanan ilimi muna nan da su a cikin Alkur’ani, abin da ya kamata a yi shi ne mu fadada bincike na fahimtar zamani a cikin Alkur’ani wanda hakan zai bai wa mu Afirka damar yin kirkire-kirkire da gudanar da sabbin ayyuka na ci gaban zamani.

Yana da kyau yadda muke da yawan mahaddata a Nijeriya, ya zama kasar ta zamo kan gaba wajen zama abar koyi a fannin kawo ci gaban zamani a Afirka da kuma inganta rayuwar ‘yan Afirka. Muna da yakinin cewa, in dai an sa hakan a gaba, tabbas nan da shekaru masu zuwa za mu iya cimma duk burin da muke so mu ga mun cimmawa.

Kuma har ila yau, mun ji dadi a kan kiran da ka yi na a sake nazarin wasu abubuwa na shari’a da ba su da asali a ainihin nassin da Allah ya saukar, domin tabbas abubuwan da Allah ya haramta da hukuncinsa (Muharramatu) kuma ya kulle su da hukunce-hukunce (Muhkamatu) babu wanda ya isa ya kara ko ya rage, kuma Allah bai bar su a dunkule ba, ya yi bayaninsu dalla-dalla.

Yadda aka fara shigo da abubuwa cikin addinin nan tun daga zamanin Sahabbai ya rikita abubuwa da yawa. Wannan ba rashin kunya ba ne ko kadan, muna girmama dukkan Sahabbai wallahi, kuma a cikinsu ne wasu suka tsawatar a kan shigo da abubuwa cikin addinin. Ga misalin Hadisin Ka’abu bin Malik, lokacin da wasu matasa suka ziyarce shi, suka yi masa kirarin girmamawa, suka bukaci ya yi musu hira daga cikin rayuwarsa tare da Annabi (SAW), wanda ya ce, musu “in kun ji na yi shiru ku ma ku yi shiru, yadda kaina ya yi fari (furfura) haka kwakwalwata ta yi, kuma abubuwa ne na yadda muka yi rayuwa da Rasulullahi (SAW). Bari na fada muku duk sai da aka canja su face Sallah (kadai), ita ma ga ta nan kun fara canzawa”. Duk wannan ya nuna cewa, ya kamata mu dawo kan turba ta asali.

Allah ya saka da alkhairi, ya Sayyadi. Wallahi muna godiya sosai, domin mun kuma karu da bayanai a kan abubuwan da Shari’a ke kewayawa a kansu na batun da ya shafi daukar kudi daga nan zuwa nan kamar rabon gado; da tsara Iyali da yadda za a yi aure da rabuwarsa da yadda za a yi tarayya a cikin dangi; da ukuba da hukunci a tsakanin abokan hulda. Haka nan, sauran harkoki irin su kokarin tabbatar da zaman lafiya wanda ya kunshi yadda ake shirya yaki, da sulhu, da zaman lumana; da batun riba da ke bayani a kan tsarin yadda za a gudanar da kasuwanci, sai kuma abubuwan da suka shafi dabi’o’i na ‘yan’adam.

Hakika duk sauran abubuwan da ba wadannan ba, Shari’a ta bar mutane su yi hukunci da abin da ke zamaninsu, na daga kundin tsarin mulki da ake shimfidawa don maslahar al’umma wajen habaka tattalin arziki da raya kasa.

Allah ya kara ilimi da fahimta a cikin wannan addini mai fadi da Manzon Rahama, Annabi (SAW) ya zo mana da shi domin tseratar da al’umma duka sai dai wanda ya ki. Mun gode.

Sako daga Malam Miftahu Adam Zariya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AnnabiManzon Allah SAWRamadan
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnoni 20 Na Fuskantar Matsin Lambar NULGE Kan Rashin Aiwatar Da Mafi Karanci Albashi

Next Post

Ministan YaÉ—a Labarai Ya Zayyana Wa Masu Zuba Jari Na Faransa Irin Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Nijeriya

Related

Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (1)
Dausayin Musulunci

Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (1)

22 hours ago
Abubuwan Da Aka Haramta Wa Mahajjaci
Dausayin Musulunci

Abubuwan Da Aka Haramta Wa Mahajjaci

1 week ago
Shimfida A Kan Aikin Hajji Da Bayani A Kan Mikatin Da Manzon Allah (SAW) Ya Sa
Dausayin Musulunci

Shimfida A Kan Aikin Hajji Da Bayani A Kan Mikatin Da Manzon Allah (SAW) Ya Sa

3 weeks ago
Ramadan
Dausayin Musulunci

Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (4)

4 weeks ago
Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (3): Shari’ar Manzon Allah (SAW) Ta Zo Da Wayewa A Kowane Fanni
Dausayin Musulunci

Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (3): Shari’ar Manzon Allah (SAW) Ta Zo Da Wayewa A Kowane Fanni

1 month ago
Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (1)
Dausayin Musulunci

Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (1)

2 months ago
Next Post
Ministan YaÉ—a Labarai Ya Zayyana Wa Masu Zuba Jari Na Faransa Irin Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Nijeriya

Ministan YaÉ—a Labarai Ya Zayyana Wa Masu Zuba Jari Na Faransa Irin Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Za Mu Ci Gaba Da Aikin Neman Man Fetur Arewacin Nijeriya — Ojulari

Za Mu Ci Gaba Da Aikin Neman Man Fetur Arewacin Nijeriya — Ojulari

May 24, 2025
Sin Ta Bukaci Kada Amurka Ta Siyasantar Da Hadin Gwiwar Bangaren Ilimi

Sin Ta Bukaci Kada Amurka Ta Siyasantar Da Hadin Gwiwar Bangaren Ilimi

May 23, 2025
Kamfanoni Masu Jarin Waje Sun Ci Gajiyar Tsarin Kasar Sin Na Samar Da Rangwamen Gwamnati Ta Musayar Sabbin Kayayyaki Da Tsofaffi

Kamfanoni Masu Jarin Waje Sun Ci Gajiyar Tsarin Kasar Sin Na Samar Da Rangwamen Gwamnati Ta Musayar Sabbin Kayayyaki Da Tsofaffi

May 23, 2025
Hukumar NPA Ta Yi Watsi Da Zargin Cin Hanci Da Rashawa Da Aka Lakaba Mata

Hukumar NPA Ta Yi Watsi Da Zargin Cin Hanci Da Rashawa Da Aka Lakaba Mata

May 23, 2025
Sin Da ASEAN Sun Kammala Tattaunawa Game Da Kafa Yankin Ciniki Cikin ‘Yanci

Sin Da ASEAN Sun Kammala Tattaunawa Game Da Kafa Yankin Ciniki Cikin ‘Yanci

May 23, 2025
An Gudanar Da Taron Kolin Bunkasa Kasuwanci Da Zuba Jari Na Duniya Na Shekara Ta 2025 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kolin Bunkasa Kasuwanci Da Zuba Jari Na Duniya Na Shekara Ta 2025 A Beijing

May 23, 2025
Kungiyar Tsofaffin ÆŠaliban BUK Ta Karrama Dr. Sani Dauda Ibrahim Da Walimar Kammala Digiri Na 3

Kungiyar Tsofaffin ÆŠaliban BUK Ta Karrama Dr. Sani Dauda Ibrahim Da Walimar Kammala Digiri Na 3

May 23, 2025
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

May 23, 2025
Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Gwamnatin Jamus Friedrich Merz

Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Gwamnatin Jamus Friedrich Merz

May 23, 2025
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

May 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.