ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dasuki Ya Kaddamar Da Shirin Tallafa Wa Masu Kananan Sana’o’i Da Manoma

by Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
1 year ago
Talla

Dan majalisar da ke wakiltar mazabar Kebbe/Tambuwal a Majalisar Wakilai, Honarabul Abdussamad Dasuki ya kaddamar da shirin tallafa wa mata da matasa masu kanana da matsakaitan sana’oi da manoma.

Shirin wanda aka yi wa taken “Yana Tafe” an kaddamar da shi ne ta hanyar bayar da cakin kudi kai tsaye ga wadanda suka amfana da manufar karfafawa sana’oinsu domin su kara zama masu dogaro da kai.

Honarabul Attahiru Umar Danmadi, mataimaki na musamman kan harkokin majalisa ga Honarabul Dasuki ne ya wakilci shi ya kuma bayyana cewar za su rika ziyartar kasuwanni da gonaki domin zakulo ‘yan kasuwa da manoma da suka fi bukata domin ba su cakin kudi domin karfafawa da habaka aikin noma, cinikayyar abinci da bunkasa kanana da matsakaitan sana’oi a mazabu 10 da ke a Kebbe da 11 da ke a Tambuwal.

ADVERTISEMENT

Ya ce shirin wanda za a rika aiwatarwa a kowane wata daga gunduma zuwa gunduma, daya ne daga cikin alkawulan da Dasuki ya dauka a lokacin yekuwar neman zabe da zummar bunkasa tattalin arzikin al’ummar mazabar tare da kusanto da sha’anin wakilci kusa da al’umma ta hanyar sauke nauyin da suka dora masa.

“Mun assasa shiraruwa da dama na ayyukan raya mazaba da ci-gaban al’umma, a kwanan baya mun kaddamar da tallafin naira miliyan 100 wanda ya kunshi kudi, tallafin karatu da kayan abinci. A watan da ya gabata mun raba takin zamani ga manoma, yanzu kuma ga tallafin karfafawa manoma da masu kananan sana’o’i domin wadata al’umma da abinci da bunkasa sana’oi domin kara zama da kafafun su.”

LABARAI MASU NASABA

An Horas Da Masu Kiwon Dabbobi Dabarun Kiwon Zamani

Mataimakin Shugaban Kasa Ya Yaba Da Tsarin Aikin Noma Na Jihar Jigawa

A mabambantan tatttaunawarsu da LEADERSHIP Hausa, wasu daga cikin wadanda suka amfana, Maidamma Shekare, Mubarak Muhammad da Alhaji Hamisu Kuchi duka sun bayyana godiyarsu ga dan majalisar tare da alkawalin amfani da tallafin wajen inganta aikin gona da sana’o’in su.

A cewar su shirin zai taimaka kwarai ainun tare da yin tasiri a gare su manoma da masu matsakaita da kananan sana’o’i a yankunan karkara.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Abubuwa Biyar Game Da Kiwon Talotalo
Noma Da Kiwo

An Horas Da Masu Kiwon Dabbobi Dabarun Kiwon Zamani

December 20, 2025
Mataimakin Shugaban Kasa Ya Yaba Da Tsarin Aikin Noma Na Jihar Jigawa
Noma Da Kiwo

Mataimakin Shugaban Kasa Ya Yaba Da Tsarin Aikin Noma Na Jihar Jigawa

December 19, 2025
Kiwon Dabbobi Da Fasahar Kimiyyar Zaman
Noma Da Kiwo

Kiwon Dabbobi Da Fasahar Kimiyyar Zaman

December 14, 2025
Next Post
trump

Trump Ya Sha Alwashin Fatattakar Baki Daga Amurka Idan Aka Sake Zaben Sa

LABARAI MASU NASABA

Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.