• English
  • Business News
Tuesday, May 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dasuki Ya Kaddamar Da Shirin Tallafa Wa Masu Kananan Sana’o’i Da Manoma

by Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
9 months ago
in Noma Da Kiwo
0
Dasuki Ya Kaddamar Da Shirin Tallafa Wa Masu Kananan Sana’o’i Da Manoma
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dan majalisar da ke wakiltar mazabar Kebbe/Tambuwal a Majalisar Wakilai, Honarabul Abdussamad Dasuki ya kaddamar da shirin tallafa wa mata da matasa masu kanana da matsakaitan sana’oi da manoma.

Shirin wanda aka yi wa taken “Yana Tafe” an kaddamar da shi ne ta hanyar bayar da cakin kudi kai tsaye ga wadanda suka amfana da manufar karfafawa sana’oinsu domin su kara zama masu dogaro da kai.

Honarabul Attahiru Umar Danmadi, mataimaki na musamman kan harkokin majalisa ga Honarabul Dasuki ne ya wakilci shi ya kuma bayyana cewar za su rika ziyartar kasuwanni da gonaki domin zakulo ‘yan kasuwa da manoma da suka fi bukata domin ba su cakin kudi domin karfafawa da habaka aikin noma, cinikayyar abinci da bunkasa kanana da matsakaitan sana’oi a mazabu 10 da ke a Kebbe da 11 da ke a Tambuwal.

Ya ce shirin wanda za a rika aiwatarwa a kowane wata daga gunduma zuwa gunduma, daya ne daga cikin alkawulan da Dasuki ya dauka a lokacin yekuwar neman zabe da zummar bunkasa tattalin arzikin al’ummar mazabar tare da kusanto da sha’anin wakilci kusa da al’umma ta hanyar sauke nauyin da suka dora masa.

“Mun assasa shiraruwa da dama na ayyukan raya mazaba da ci-gaban al’umma, a kwanan baya mun kaddamar da tallafin naira miliyan 100 wanda ya kunshi kudi, tallafin karatu da kayan abinci. A watan da ya gabata mun raba takin zamani ga manoma, yanzu kuma ga tallafin karfafawa manoma da masu kananan sana’o’i domin wadata al’umma da abinci da bunkasa sana’oi domin kara zama da kafafun su.”

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu

Nazari Kan Dabarun Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi Domin Jurewa Sauyin Yanayi

A mabambantan tatttaunawarsu da LEADERSHIP Hausa, wasu daga cikin wadanda suka amfana, Maidamma Shekare, Mubarak Muhammad da Alhaji Hamisu Kuchi duka sun bayyana godiyarsu ga dan majalisar tare da alkawalin amfani da tallafin wajen inganta aikin gona da sana’o’in su.

A cewar su shirin zai taimaka kwarai ainun tare da yin tasiri a gare su manoma da masu matsakaita da kananan sana’o’i a yankunan karkara.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Dan MajalisadasukiManomamasu karamin karfiNomaSana'o'iTalakawa
ShareTweetSendShare
Previous Post

PDP Ta Lashe Zaɓen Shugabanin Ƙananan Hukumomin Bauchi Gaba Ɗaya

Next Post

Trump Ya Sha Alwashin Fatattakar Baki Daga Amurka Idan Aka Sake Zaben Sa

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu

2 days ago
Nazari Kan Dabarun Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi Domin Jurewa Sauyin Yanayi
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Dabarun Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi Domin Jurewa Sauyin Yanayi

3 days ago
Noman 2025: Dole Ne Manoma Su Kiyaye Hasashen Hukumar NiMet
Noma Da Kiwo

Noman 2025: Dole Ne Manoma Su Kiyaye Hasashen Hukumar NiMet

3 days ago
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma
Noma Da Kiwo

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

4 days ago
Nazari Kan Dabarun Gargajiya Domin Jawo Hankalin Zuma
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Dabarun Gargajiya Domin Jawo Hankalin Zuma

1 week ago
Ambaliya: Yankunan Da Ba Za Su Yi Noma A Kakar Bana Ba A Jihar Neja
Noma Da Kiwo

Ambaliya: Yankunan Da Ba Za Su Yi Noma A Kakar Bana Ba A Jihar Neja

1 week ago
Next Post
trump

Trump Ya Sha Alwashin Fatattakar Baki Daga Amurka Idan Aka Sake Zaben Sa

LABARAI MASU NASABA

Jami’ar Maryam Abacha Ta Rufe ÆŠakunan Kwanan ÆŠalibai Saboda Aikata Rashin ÆŠa’a A Kano

Jami’ar Maryam Abacha Ta Rufe ÆŠakunan Kwanan ÆŠalibai Saboda Aikata Rashin ÆŠa’a A Kano

May 13, 2025
China Da Amurka Sun Yarda Da Rage Harajin Kayayyakinsu Domin Sasanta Rikicin Kasuwanci

China Da Amurka Sun Yarda Da Rage Harajin Kayayyakinsu Domin Sasanta Rikicin Kasuwanci

May 13, 2025
Boko Haram Sun Kashe Mutum 12 A Wani Sabon Hari A Borno

Bam Ya Hallaka Ma’aikatan Hukumar Ilimi 2 A Hanyar Damboa-Maiduguri

May 13, 2025
Wike Ya GargaÉ—i PDP Kan Bai Wa ÆŠan Arewa Takara A 2027

Wike Ya GargaÉ—i PDP Kan Bai Wa ÆŠan Arewa Takara A 2027

May 13, 2025
Nijeriya Ta Biya Dukkanin Bashin IMF Na COVID-19

Nijeriya Ta Biya Dukkanin Bashin IMF Na COVID-19

May 13, 2025
Mahaifin Tsohon Gwamnan Kaduna, Ramalan Yero, Ya Rasu

Mahaifin Tsohon Gwamnan Kaduna, Ramalan Yero, Ya Rasu

May 13, 2025
Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Da Ake Iya Sarrafawa Daga Nesa

Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Da Ake Iya Sarrafawa Daga Nesa

May 12, 2025
Ƴan Ta’adda Sun Yi Garkuwa Da Tsohon Jami’in Shige Da Fice Da Fasinjoji 2 A Yobe

Ƴan Ta’adda Sun Yi Garkuwa Da Tsohon Jami’in Shige Da Fice Da Fasinjoji 2 A Yobe

May 12, 2025
He Lifeng Ya Gana Da Babbar Jami’ar WTO Ngozi Okonjo-Iweala

He Lifeng Ya Gana Da Babbar Jami’ar WTO Ngozi Okonjo-Iweala

May 12, 2025
Ma’aikatar Kasuwanci: Sanarwar Da Sin Da Amurka Suka Fitar Muhimmin Mataki Ne Na Warware Sabaninsu

Ma’aikatar Kasuwanci: Sanarwar Da Sin Da Amurka Suka Fitar Muhimmin Mataki Ne Na Warware Sabaninsu

May 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.