• English
  • Business News
Wednesday, August 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dawowa Hutu: Iyaye Sun Koka Kan Karin Kudin Makaranta A Yanayin Kuncin Rayuwa

by CMG Hausa
2 years ago
in Labarai
0
Dawowa Hutu: Iyaye Sun Koka Kan Karin Kudin Makaranta A Yanayin Kuncin Rayuwa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A daidai lokacin da makarantun firamare da sakandire da ke fadin kasar nan suka shiga sabon zangon karatu bayan dawowa daga hutu, galibin iyaye sun koka da karin kudin makaranta a yanayin kuncin rayuwa da ake ciki a halin yanzu, kamar yadda binciken LEADERSHIP ya nuna.

Wannan karin kudin ya zo daidai lokacin da ake samun raguwar kudaden shiga da zai dauki nauyin iyalai, saboda hauhawar farashin kayayyaki a fadin kasar nan sakamakon cire tallafin man fetur.

  • Wata Sabuwa: Gwamna Ya Kai Karar Shugaban Majalisa Gaban Tinubu Kan Nada Shugabancin Kwamiti Mai Gwabi

Iyayen daliban makarantun gaba da sakandare sun bayyana damuwarsu game da karin kudin makaranta a wasu jami’o’in Nijeriya. Wadannan jami’o’in, sun danganta karin kudaden na kashi 100 zuwa 200 bisa rashin isasshen tallafin kudi daga gwamnati da kuma hauhawar farashin kayayyaki.

Duk da kokarin da gwamnati ke yi na aiwatar da tallafin karatu ga daliban da ba su da galihu, mafi yawancin daliban ba su da tabbas game da makomarsu karatunsu.

Har ila yau, tashin hankali na kara karuwa a wasu jami’o’i, yayin da dalibai ke bayyana rashin jin dadinsu kan karin kudin makaranta da aka yi a baya-bayan nan, wanda ya haifar da zanga-zanga a fadin kasar nan. Misali, a kwanakin baya ne daliban Jami’ar Jos suka fito kan tituna domin nuna rashin amincewarsu da karin kudin makaranta da jami’a ta yi.

Labarai Masu Nasaba

Uwargidar Gwamnan Katsina Ta Nemi A Taimaka Wa Mata Wajen Yaƙi Da Ciwon Nono Da Na Mahaifa

Bello Turji Bai Yi Sulhu Da Kowa Ba – Guyawa Isa

Masu zanga-zangan karkashin jagorancin kungiyar dalibai ta kasa, sun bukaci a gaggauta dawo da kudin makarantar yadda yake a baya. Masu zanga-zangan dauke da alluna masu dauke da sako kamar haka, “Idan yaranku za su iya biyan kudin, mu ba za mu iya ba” da “Ba ma son barin makaranta,” daliban sun bayyana kokensu.

Sun jaddada cewa tuni ‘yan Nijeriya suka fara kokawa da matsalolin tattalin arziki, kuma karin kudin makarantar zai kara ta’azzara lamarin. Zanga-zangar lumana da daliban suka gudanar ta haifar da cunkoson ababen hawa tare da toshe hanyoyin shiga harabar jami’ar.

Haka kuma, a jami’ar Legas (UNILAG), an samu ta tashin hankali a harabar jami’ar, yayin da kungiyar dalibai ta kasa (NANS) ta goyi bayan daliban na shirya zanga-zanga. Hasali ma, kwanan nan NANS ta ba da wa’adin sa’o’i 48 ga hukumomin jami’ar Legas da su sauya karin kudin makaranta.
NANS ta kuma yi kira ga daukacin manyan makarantu da ke fadin kasar nan su guji kara kudin makaranta, sannan ta yi gargadin cewa a shirye suke su hada kan mambobinsu a fadin kasar domin gudanar da zanga-zanga na rashin amincewarsu da irin wadannan karin kudin makaranta.

Ta bayyana wannan matsayar ne a yayin wani taron manema labarai da aka gudanar a cibiyar ‘yan jarida ta kasa da kasa da ke Legas, biyo bayan dakile zanga-zangar lumana da ‘yansanda suka yi a UNILAG.

Kafin haka dai, NANS ta nuna rashin amincewarta da karin sama da kashi 300 na kudaden makaranta a jami’ar Ambrose Alli ta jihar Edo da ke Ekpoma. Daliban hadu a harabar kungiyar ‘yan jarida ta Nijeriya (NUJ) na Jihar Edo, daliban sun bukaci a sake duba kudaden makarantar cikin gaggawa domin a samu zaman lafiya.

Binciken LEADERSHIP ya nuna cewa tsadar rayuwa da tsadar kayayyakin aiki na kawo cikas ga ilimi, wanda hakan ya sa iyaye da dama ba su iya saka ‘ya’yansu a makaranta.
Makarantu masu zaman kansu sun kara wa daliban firamare da sakandire kudin makaranta sama da kashi 300, lamarin da ya kara haifar da fargabar cewa yawan daliban ba za su koma makaranta ba. Wasu iyaye na tunanin sanya ‘ya’yansu a makarantun gwamnati, yayin da wasu kuma ba su da tabbas kan matakin da za su dauka nan gaba, wanda haka zai kara haifar da karuwar yaran da ba sa zuwa makaranta.

Makarantu masu zaman kansu sun kara da cewa suna fuskantar tsadar kayayyakin koyo da kamarantarwa, wanda hakan ta sa dole ne su kara kudin makaranta.
Yayin da wasu malaman makarantu masu zaman kansu sun bayyana cewa suna fuskantar karancin albashi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kudin makarantaTsadar Rayuwa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Jihar Enugu Ta Haramta Hakar Ma’adinai Ta Haramtacciyar Hanya

Next Post

An Yi Nasarar Ceto Mutum 30 Da Aka Sace Su A Jihar Bauchi

Related

Uwargidar Gwamnan Katsina Ta Nemi A Taimaka Wa Mata Wajen Yaƙi Da Ciwon Nono Da Na Mahaifa
Labarai

Uwargidar Gwamnan Katsina Ta Nemi A Taimaka Wa Mata Wajen Yaƙi Da Ciwon Nono Da Na Mahaifa

3 hours ago
Bello Turji Bai Yi Sulhu Da Kowa Ba – Guyawa Isa
Labarai

Bello Turji Bai Yi Sulhu Da Kowa Ba – Guyawa Isa

5 hours ago
Sojoji Sun Kama Mai Yi Wa Boko Haram Safarar Man Fetur A Borno
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Mai Yi Wa Boko Haram Safarar Man Fetur A Borno

6 hours ago
Matar Marigayi MKO Abiola, Ta Rasu Tana Da Shekaru 82
Manyan Labarai

Matar Marigayi MKO Abiola, Ta Rasu Tana Da Shekaru 82

7 hours ago
Remi Tinubu Ta Bai Wa Waɗanda Ambaliya Ta Shafa A Neja Tallafin N1bn
Labarai

Remi Tinubu Ta Bai Wa Waɗanda Ambaliya Ta Shafa A Neja Tallafin N1bn

9 hours ago
Gwamnatin Tarayya Za Ta Farfaɗo Da Noman Dabino – Shettima
Labarai

Gwamnatin Tarayya Za Ta Farfaɗo Da Noman Dabino – Shettima

10 hours ago
Next Post
Mutum 30 Sun Halaka Tare Da Sace Mutum 19 A Abuja

An Yi Nasarar Ceto Mutum 30 Da Aka Sace Su A Jihar Bauchi

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Samar Da Yuan Biliyan Daya Domin Ayyukan Jin Kai Sakamakon Ibtila’in Ambaliyar Ruwa

Sin Ta Samar Da Yuan Biliyan Daya Domin Ayyukan Jin Kai Sakamakon Ibtila’in Ambaliyar Ruwa

August 6, 2025
Uwargidar Gwamnan Katsina Ta Nemi A Taimaka Wa Mata Wajen Yaƙi Da Ciwon Nono Da Na Mahaifa

Uwargidar Gwamnan Katsina Ta Nemi A Taimaka Wa Mata Wajen Yaƙi Da Ciwon Nono Da Na Mahaifa

August 6, 2025
Bello Turji Bai Yi Sulhu Da Kowa Ba – Guyawa Isa

Bello Turji Bai Yi Sulhu Da Kowa Ba – Guyawa Isa

August 6, 2025
Sojoji Sun Kama Mai Yi Wa Boko Haram Safarar Man Fetur A Borno

Sojoji Sun Kama Mai Yi Wa Boko Haram Safarar Man Fetur A Borno

August 6, 2025
Matar Marigayi MKO Abiola, Ta Rasu Tana Da Shekaru 82

Matar Marigayi MKO Abiola, Ta Rasu Tana Da Shekaru 82

August 6, 2025
Remi Tinubu Ta Bai Wa Waɗanda Ambaliya Ta Shafa A Neja Tallafin N1bn

Remi Tinubu Ta Bai Wa Waɗanda Ambaliya Ta Shafa A Neja Tallafin N1bn

August 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Farfaɗo Da Noman Dabino – Shettima

Gwamnatin Tarayya Za Ta Farfaɗo Da Noman Dabino – Shettima

August 6, 2025
Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano

Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano

August 6, 2025
Hare-haren Boko Haram Da ‘Yan Bindiga Ya Ragu A Cikin Shekaru Biyu – Ribadu

Hare-haren Boko Haram Da ‘Yan Bindiga Ya Ragu A Cikin Shekaru Biyu – Ribadu

August 5, 2025
Kasar Sin Ta Sanar Da Matakan Fara Bayar Da Ilimin Kafin Firamare Kyauta

Kasar Sin Ta Sanar Da Matakan Fara Bayar Da Ilimin Kafin Firamare Kyauta

August 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.