• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dawowa Hutu: Iyaye Sun Koka Kan Karin Kudin Makaranta A Yanayin Kuncin Rayuwa

by CMG Hausa
2 years ago
in Labarai
0
Dawowa Hutu: Iyaye Sun Koka Kan Karin Kudin Makaranta A Yanayin Kuncin Rayuwa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A daidai lokacin da makarantun firamare da sakandire da ke fadin kasar nan suka shiga sabon zangon karatu bayan dawowa daga hutu, galibin iyaye sun koka da karin kudin makaranta a yanayin kuncin rayuwa da ake ciki a halin yanzu, kamar yadda binciken LEADERSHIP ya nuna.

Wannan karin kudin ya zo daidai lokacin da ake samun raguwar kudaden shiga da zai dauki nauyin iyalai, saboda hauhawar farashin kayayyaki a fadin kasar nan sakamakon cire tallafin man fetur.

  • Wata Sabuwa: Gwamna Ya Kai Karar Shugaban Majalisa Gaban Tinubu Kan Nada Shugabancin Kwamiti Mai Gwabi

Iyayen daliban makarantun gaba da sakandare sun bayyana damuwarsu game da karin kudin makaranta a wasu jami’o’in Nijeriya. Wadannan jami’o’in, sun danganta karin kudaden na kashi 100 zuwa 200 bisa rashin isasshen tallafin kudi daga gwamnati da kuma hauhawar farashin kayayyaki.

Duk da kokarin da gwamnati ke yi na aiwatar da tallafin karatu ga daliban da ba su da galihu, mafi yawancin daliban ba su da tabbas game da makomarsu karatunsu.

Har ila yau, tashin hankali na kara karuwa a wasu jami’o’i, yayin da dalibai ke bayyana rashin jin dadinsu kan karin kudin makaranta da aka yi a baya-bayan nan, wanda ya haifar da zanga-zanga a fadin kasar nan. Misali, a kwanakin baya ne daliban Jami’ar Jos suka fito kan tituna domin nuna rashin amincewarsu da karin kudin makaranta da jami’a ta yi.

Labarai Masu Nasaba

HOTO: Ofishin Tsohon Shugaban Kasa Shagari Bayan Shekara 42

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

Masu zanga-zangan karkashin jagorancin kungiyar dalibai ta kasa, sun bukaci a gaggauta dawo da kudin makarantar yadda yake a baya. Masu zanga-zangan dauke da alluna masu dauke da sako kamar haka, “Idan yaranku za su iya biyan kudin, mu ba za mu iya ba” da “Ba ma son barin makaranta,” daliban sun bayyana kokensu.

Sun jaddada cewa tuni ‘yan Nijeriya suka fara kokawa da matsalolin tattalin arziki, kuma karin kudin makarantar zai kara ta’azzara lamarin. Zanga-zangar lumana da daliban suka gudanar ta haifar da cunkoson ababen hawa tare da toshe hanyoyin shiga harabar jami’ar.

Haka kuma, a jami’ar Legas (UNILAG), an samu ta tashin hankali a harabar jami’ar, yayin da kungiyar dalibai ta kasa (NANS) ta goyi bayan daliban na shirya zanga-zanga. Hasali ma, kwanan nan NANS ta ba da wa’adin sa’o’i 48 ga hukumomin jami’ar Legas da su sauya karin kudin makaranta.
NANS ta kuma yi kira ga daukacin manyan makarantu da ke fadin kasar nan su guji kara kudin makaranta, sannan ta yi gargadin cewa a shirye suke su hada kan mambobinsu a fadin kasar domin gudanar da zanga-zanga na rashin amincewarsu da irin wadannan karin kudin makaranta.

Ta bayyana wannan matsayar ne a yayin wani taron manema labarai da aka gudanar a cibiyar ‘yan jarida ta kasa da kasa da ke Legas, biyo bayan dakile zanga-zangar lumana da ‘yansanda suka yi a UNILAG.

Kafin haka dai, NANS ta nuna rashin amincewarta da karin sama da kashi 300 na kudaden makaranta a jami’ar Ambrose Alli ta jihar Edo da ke Ekpoma. Daliban hadu a harabar kungiyar ‘yan jarida ta Nijeriya (NUJ) na Jihar Edo, daliban sun bukaci a sake duba kudaden makarantar cikin gaggawa domin a samu zaman lafiya.

Binciken LEADERSHIP ya nuna cewa tsadar rayuwa da tsadar kayayyakin aiki na kawo cikas ga ilimi, wanda hakan ya sa iyaye da dama ba su iya saka ‘ya’yansu a makaranta.
Makarantu masu zaman kansu sun kara wa daliban firamare da sakandire kudin makaranta sama da kashi 300, lamarin da ya kara haifar da fargabar cewa yawan daliban ba za su koma makaranta ba. Wasu iyaye na tunanin sanya ‘ya’yansu a makarantun gwamnati, yayin da wasu kuma ba su da tabbas kan matakin da za su dauka nan gaba, wanda haka zai kara haifar da karuwar yaran da ba sa zuwa makaranta.

Makarantu masu zaman kansu sun kara da cewa suna fuskantar tsadar kayayyakin koyo da kamarantarwa, wanda hakan ta sa dole ne su kara kudin makaranta.
Yayin da wasu malaman makarantu masu zaman kansu sun bayyana cewa suna fuskantar karancin albashi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kudin makarantaTsadar Rayuwa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Jihar Enugu Ta Haramta Hakar Ma’adinai Ta Haramtacciyar Hanya

Next Post

An Yi Nasarar Ceto Mutum 30 Da Aka Sace Su A Jihar Bauchi

Related

HOTO: Ofishin Tsohon Shugaban Kasa Shagari Bayan Shekara 42
Labarai

HOTO: Ofishin Tsohon Shugaban Kasa Shagari Bayan Shekara 42

2 hours ago
‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

4 hours ago
An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi
Labarai

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

6 hours ago
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja
Labarai

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

9 hours ago
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?
Da ɗumi-ɗuminsa

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

9 hours ago
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 
Labarai

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

10 hours ago
Next Post
Mutum 30 Sun Halaka Tare Da Sace Mutum 19 A Abuja

An Yi Nasarar Ceto Mutum 30 Da Aka Sace Su A Jihar Bauchi

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

May 15, 2025
An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe

An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe

May 15, 2025
HOTO: Ofishin Tsohon Shugaban Kasa Shagari Bayan Shekara 42

HOTO: Ofishin Tsohon Shugaban Kasa Shagari Bayan Shekara 42

May 15, 2025
Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

May 15, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

May 15, 2025
Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

May 15, 2025
An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

May 15, 2025
NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

May 15, 2025
Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

May 15, 2025
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.