• English
  • Business News
Thursday, October 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

DSS Ta Kama Kwamandan Boko Haram a Ogun

by Sadiq
3 years ago
Boko Haram

An shiga cikin tashin hankali a wasu sassa na Abeokuta, babban birnin jihar Ogun a ranar Lahadi biyo bayan kama wani da ake zargin shugaban kungiyar Boko Haram ne.

Wani gidan rediyo mai zaman kansa a Abeokuta ne ya bayyana hakan a ranar Lahadi da yamma wanda ya haifar da firgici a tsakanin mazauna jihar.

  • Rashin Tsaro: Sanatan APC Ya Nemi Monguno Ya Yi Murabus
  • ISWAP Ce Ta Kai Wa Sojoji Hari A Dutsen Zuma – Rahoto

Rahotanni sun bayyana cewa jami’an hukumar tsaro ta farin kaya sun kama wanda ake zargin ne a daren ranar Asabar.

Labarin ya bazu a shafukan sada zumunta na jihar a ranar Lahadi.

Lamarin dai na da nasaba da shirin kai hare-hare a wasu jihohin Kudu maso Yamma da ake zargin ‘yan ta’adda na shirin yi.

LABARAI MASU NASABA

Amupitan Ya Isa Majalisar Dattawa Domin Tantance Shi A Matsayin Sabon Shugaban INEC

Majalisar Dattawa Ta Fara Tantance Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

Sai dai wata majiya mai tushe ta shaida wa wakilinmu cewa an kama wanda ake zargin shugaban kungiyar Boko Haram ne kwanaki a unguwar Ijaye da ke Abeokuta.

Majiyar ta ce tun da farko wanda ake zargin ya yi turjiya kafin ya mika wuya ta karfin tsiya ga jami’an DSS.

A cewar mai binciken, an gudanar da aikin ne a daren ranar Asabar.

A rahoton da gidan rediyon ya bayar, ya ce dan ta’addan da ake zargin ya isa Abeokuta ne daga Katsina, inda ya yi aikin tsaro a Ijaye, inda ya ke tattara bayanan sirri kan hare-haren ta’addanci.

Majiyar tsaron ta ce, “Shi (wanda ake zargin) ya koma Abeokuta ne domin ya kafa kungiyar ‘yan ta’adda domin yin garkuwa da mutane da kuma kai hare-haren ta’addanci.

“Kuma bayan wani taron sirri da aka yi, jami’an tsaro dauke da bindigogi sun kai farmaki maboyarsa sannan suka damke shi.

“Ba abu ne mai sauki ba. Amma da yardar Allah zamu shawo kan lamarin.

“Har yanzu akwai da yawa daga cikinsu, amma muna kan gabar aikinmu.”

Wakilinmu ya tattaro cewa wanda ake zargin yana hannun DSS har yanzu.

Da aka tuntubi kakakin hukumar DSS, Peter Afunanya, bai amsa sakon da aka aike masa ba.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, Abimbola Oyeyemi, ya ce bai da masaniya kan lamarin.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Amupitan Ya Isa Majalisar Dattawa Domin Tantance Shi A Matsayin Sabon Shugaban INEC
Manyan Labarai

Amupitan Ya Isa Majalisar Dattawa Domin Tantance Shi A Matsayin Sabon Shugaban INEC

October 16, 2025
Majalisar Dattawa Ta Fara Tantance Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC
Manyan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Fara Tantance Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

October 16, 2025
Baba-Ahmed Ya Zargi El-Rufai Da APC Kan Haifar Da Rashin Tsaro Don Neman Mulki
Manyan Labarai

Baba-Ahmed Ya Zargi El-Rufai Da APC Kan Haifar Da Rashin Tsaro Don Neman Mulki

October 16, 2025
Next Post
Tsawa Ta Kashe Mutane 47 A Indiya

Tsawa Ta Kashe Mutane 47 A Indiya

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Fursunoni Bayan Kammala Zaman Kurkuku

Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Fursunoni Bayan Kammala Zaman Kurkuku

October 16, 2025
Amupitan Ya Isa Majalisar Dattawa Domin Tantance Shi A Matsayin Sabon Shugaban INEC

Amupitan Ya Isa Majalisar Dattawa Domin Tantance Shi A Matsayin Sabon Shugaban INEC

October 16, 2025
Majalisar Dattawa Ta Fara Tantance Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

Majalisar Dattawa Ta Fara Tantance Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

October 16, 2025
An Dakatar Da Tashi Da Saukar Jirage A Kenya Don Karɓar Gawar Raila Odinga

An Dakatar Da Tashi Da Saukar Jirage A Kenya Don Karɓar Gawar Raila Odinga

October 16, 2025
Gwamnan Edo Ya Umarci Kwamishinoni Su Riƙa Sanya Hular Tinubu

Gwamnan Edo Ya Umarci Kwamishinoni Su Riƙa Sanya Hular Tinubu

October 16, 2025
Baba-Ahmed Ya Zargi El-Rufai Da APC Kan Haifar Da Rashin Tsaro Don Neman Mulki

Baba-Ahmed Ya Zargi El-Rufai Da APC Kan Haifar Da Rashin Tsaro Don Neman Mulki

October 16, 2025
Jami’an FRSC Sun Mayar Da N6.2m Da Suka Tsinta Bayan Aukuwar Hatsarin Mota A Katsina

Jami’an FRSC Sun Mayar Da N6.2m Da Suka Tsinta Bayan Aukuwar Hatsarin Mota A Katsina

October 16, 2025
An Kashe Mutum 13 A Wasu Sabbin Hare-Hare A Ƙauyukan Filato

An Kashe Mutum 13 A Wasu Sabbin Hare-Hare A Ƙauyukan Filato

October 16, 2025
Sauya Sheƙa: Diri Da Wasu Na Guje Wa Matsalolin Da Suka Ƙirƙiro – Dickson

Sauya Sheƙa: Diri Da Wasu Na Guje Wa Matsalolin Da Suka Ƙirƙiro – Dickson

October 16, 2025
Sashen Cinikayyar Kamfanonin Sarrafa Hajoji Na Sin Ya Bunkasa Da Kaso 4.7 Bisa Dari Cikin Watanni Tara Na Farkon Shekarar Nan

Sashen Cinikayyar Kamfanonin Sarrafa Hajoji Na Sin Ya Bunkasa Da Kaso 4.7 Bisa Dari Cikin Watanni Tara Na Farkon Shekarar Nan

October 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.