• English
  • Business News
Tuesday, November 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dubun Wani Dan Shekara 74 Da Ake Zargi Da Sace Tabarmi A Masallaci Ta Cika

by Abubakar Abba
1 year ago
Dubun

Dubun wani tsoho dan shekara 74 mai suna Jibrin Musa mazauni a gudunmar Rigasa ta Karamar Hukumar Igabi da ke a Jihar Kaduna ta cika, biyo bayan kama shi da aka yi yana satar Tabarmar wani Masallacin unguwa da ke yankin.

Jibrin wanda yake da zama a layin Turaki da ke a yankin. An kama shi ne, bisa zargin satar Tabarma a wani Masallaci da ke a layin Sarkin Bori Sule da ke a yankin.

  • Sin Ta Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Danyen Aikin Dake Barazanar Jefa Yankin Cikin Wani Bala’i
  • 2027: Majar Atiku Da Obi Da Kwankwaso Ta Fada Shakku

A hirarsa da wakilinmu, jim kadan bayan kama shi, tsohon ya ce, “ Ba zargi bane, tun da an kama ni na saci Tabarmar, ” in ji shi.

Ya ce, “Na shafe shekaru goma ina satar sabbin shinfidun Sallah a masallatai daban daban da ke a yankin da Agon Bango na masallatai, amma ban cika yawan satar Alkur’anai a masallatai ba ”.

Ya ci gaba da cewa,“ Na kan shiga cikin mallatai ne in yi satar kamar idan an idar da ko dai Sallar Azahar ko ta La’sar, wani lokacin ma da ni ake yin Sallar, sai in sace sabbin tabarmin in sanya a cikin babbar Leda in boye su a cikin babbar Rigar da nake sanye da ita, in fice daga masallacin in je in sayar da su”.

LABARAI MASU NASABA

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

Ya kara da cewa,“ Na kan sayar da kowacce daya daga Naira 1,500 zuwa Naira 2,000, wannan shi ne karo na biyu da na saci tabarma a wannan masallacin”.

Daya daga cikin ‘yan kwamitin Masallacin Miftahu Ibrahim ya shaida wa LEADERSHIP Hausa yadda su kama kama tsohon, inda ya ce, “ An dade ana yi mana satar kayayyaki a Masallacin ciki har da Tabarmin Sallah da sauran wasu kaya”.

“ Na zo Masallacin na bude na share shi aka kuma gabatar da Sallar Azahar, sai ni da wani abokina muka tashi muka fita wajen Masallacin, sai ga tsohon ya shiga cikin Masallacin, can zuwa jimawa kadan ya fito daga cikin Masallacin ya zagaya bayan Masallacin kamar zai kama ruwa,” in ji shi.

Ya kara da cewa, “Bayan da tsohon ya wuce, sai na leka cikin Masallacin na ga ba wata Tabarma, sai muka bishi a baya, muka ce masa ya dakata, bayan ya dakata sai muka ce masa ina Tabarmarmu da ya dauka a cikin Masallaci, sai ya fito da ita a nade, daga cikin babbar rigarsa”.

Shi ma Na’ibin Masallacin Malam Muhammad Shu’aibu ya shaida wa wakilinmu cewa,” Saboda yawan sace-sacen a Masallacin har ta kai ga a tsakaninmu ‘yan kwamitin Masallacin muna zargin junanmu, da sauran wasu mutanen layin”.

Shi kuwa Mai Anguwar da ke a layin, Malam Aminu Alasan ya shaida wa LEADERSHIP Hausa cewa, akwai Masallatai da dama a layin da ake korafen-korafen satar kaya a Masallati, inda muka dukufa yin addu’ar sai gashi a kama wannan tsohon.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi
Kotu Da Ɗansanda

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

October 4, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

October 4, 2025
Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance
Kotu Da Ɗansanda

NDLEA Ta Farmaki Masu Safarar Muggan Kwayoyi A Sassan Nijeriya

September 27, 2025
Next Post
CAC Da Masu POS Sun Amince Da Wa’adin Mako Biyu Don Rijista

CBN Ya Kaddamar Da Sabbin Ka’idoji Ga Masu Harkar POS

LABARAI MASU NASABA

Jami’an Tsaro Sun Dawo Da Fasfo Ɗin Sanata Natasha Bayan Ƙwace Shi A Abuja

Natasha Ta Zargi Akpabio Da Sanya Jami’an Tsaro Su Ƙwace Mata Fasfo A Filin Jirgin Saman Abuja 

November 4, 2025
Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo

Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo

November 4, 2025
Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

November 4, 2025
Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

November 3, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

November 3, 2025
An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

November 3, 2025
“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

November 3, 2025
Shugabannin Wasu Kasashe Za Su Halarci Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas A Birnin Shanghai

Shugabannin Wasu Kasashe Za Su Halarci Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas A Birnin Shanghai

November 3, 2025
Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka

Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka

November 3, 2025
Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

November 3, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.