ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, June 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Majar Atiku Da Obi Da Kwankwaso Ta Fada Shakku

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Majar

Akwai alamun da ke nuna cewa tattaunawar maja a tsakanin Atiku Abubakar, Peter Obi, da kuma Rabiu Kwankwaso ta cika da shakku game da yiwuwarta.

Shakkun dai ya dabaibaye majan ne tun lokacin daKwankwaso, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP a zaben 2023, ya bayyana cewa shi ne zai lashe zaben shugaban kasa a 2027.

  • Bangaren Sin Ya Yi Kira Ga Bangarori Biyu Dake Rikici A Sudan Da Su Yayyafawa Rikicin Kasar Ruwa
  • Dakta Gadan-ƙaya Ya Bada Haƙuri Kan Zargin Auren Jinsi Da Ya Yi A Bauchi

Rahotanni sun nuna cewa jagorar jam’iyyar NNPP ya yi wannan furuci ne a lokacin da ya kaddamar da sakatariyar jam’iyyar a Jihar Katsina kwanan nan.

ADVERTISEMENT

Tsohon gwamnan Jihar Kano, wanda Atiku da Obi suka yi zawarcinsa, ya ci gaba da cewa jam’iyyarsa ta NNPP a shirye take ta karbi ragamar shugabancin kasa, jihohi da sauran mukamai a fadin Nijeriya a zaben 2027.

Baya ga sanarwar tasa, Kwankwaso ya yi ikirarin cewa jam’iyyar PDP ta riga ta mutu, kuma ta fita daga kan layi.

LABARAI MASU NASABA

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

“Ina so in tunatar da ku cewa jam’iyyar PDP ta riga ta mutu, saboda da muna cikin jam’iyyar, tun da suka fita daga kan layi, muka yanke shawarar barin jam’iyyar,” in ji shi.

Kafin kalamun na Kwankwaso, jam’iyyar PDP ta bayyana cewa manyan jiga-jigan ‘yan adawa na neman hadaka domin kalubalantar APC a zab0en 2027.

Mataimakin sakataren yada labarai na jam’iyyar PDP na asa, Ibrahim Abdullahi, ne ya bayyana haka a lokacin da yake tattaunawa a gidan talabijin na Channels.

Abdullahi ya tabbatar da cewa Atiku, Obi, da Kwankwaso suna tattaunawa kan yiwuwar yin kawance.

Ya koka da yadda jam’iyyar ta yi asarar kuri’u sama da miliyan daya, inda ya kara da cewa da Kwankwaso ko Obi sun ci gaba da zama a jam’iyyar, “da mun rufe gibi da kuma kauce wa matsalolin siyasa da tattalin arziki da ake ciki a yanzu.

“Tabbas. Ana ci gaba da tattaunawa. Kun ga Peter Obi yana tattaunawa da Atiku. Kun ga Peter Obi yana ganawa da el-Rufai,” inji Abdullahi, inda ya kara da cewa jam’iyyarsu na kokarin ganin Obi, Kwankwaso, da sauran shugabannin da suka bar PDP sun jam’iyyar kafin zaben 2027.

“Daya daga cikinsu zai yarda da sauran, sannan za mu sami alkibla. Damuwarmu a matsayin jam’iyya da kuma wadannan mutanen da na ambata shi ne za su ceto ‘yan Nijeriya daga irin wannan kunci da yunwa da fatara da rashin tsaro da ke damun kasar nan,” ya kara shaidawa.

Idan za a iya tuna kafin zaben 2023, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Atiku, a wata hira da BBC, ya yi nuni da cewa akwai yiwuwar kawance da Obi da Kwankwaso, amma hakan bai faruwa ba.

Bugu da kari, an kuma samu rashin nasara a tattaunawar da aka yi kan kawance tsakanin Peter Obi na jam’iyyar LP da Rabiu Kwankwaso na NNPP, a daya bangaren.

Da yake magana a wata hira da ya yi da gidan talabijin na News Central, Obi ya ce ba ya neman shugabancin Nijeriya ta kowacce hanya.

Ya ce zai amince a yi aiki tare da wasu ne kawai idan ya ga mutanen da za su iya yin aikin da kyau.

A cewarsa, ba zai hada kai da kowa ba don manufar kama jihar ko kuma ya ci zabe.

Masana harkokin siyasa na nuna shakku kan kawancin Atiku da Kwankwaso da kuma Obi wajen kawar da jam’iyyar APC daga kan karagar mulkin Nijeriya. Wanda suke ganin kamar an samu matsala duba da irin kalamun da Kwankwaso ya furta da kuma irin martanin da PDP ta mayar masa.

Majar
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Hukuncin Kotu Na Barazana Ga Zaben 2027 —INEC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana

MASU ALAKA

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Tambarin Dimokuradiyya

Zaben Fitar Da Gwani Na APC: Tinubu Zai Shiga Tsakani Wajen Warware Rikicin Jam’iyyar

June 5, 2026
Next Post
Rawar Da Masu Sa Ido Ke Takawa Wajen Magudin Zabe A Nijeriya

Rawar Da Masu Sa Ido Ke Takawa Wajen Magudin Zabe A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Harba Taurarin Dan Adam 8 Zuwa Sararin Samaniya

Kasar Sin Ta Harba Taurarin Dan Adam 8 Zuwa Sararin Samaniya

June 15, 2026
Mujallar Qiushi Za Ta Buga Muhimmin Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Ciyar Da Ilimi, Fasaha Da Kwararru Gaba Tare”

Mujallar Qiushi Za Ta Buga Muhimmin Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Ciyar Da Ilimi, Fasaha Da Kwararru Gaba Tare”

June 15, 2026
Amfani Da Matar Soja Wajen Isar Da Sakon Bukata

Amfani Da Matar Soja Wajen Isar Da Sakon Bukata

June 15, 2026
Ɗan Kwankwaso Ya Zama Mataimakin Ɗan Takarar Gwamnan NDC A Zaɓen Kano na 2027

Ɗan Kwankwaso Ya Zama Mataimakin Ɗan Takarar Gwamnan NDC A Zaɓen Kano na 2027

June 15, 2026
2023: Tinubu Ya Zaɓi Kashim Shettima A Matsayin Mataimaki

Shin Har Yanzu Shettima Ne Abokin Takarar Tinubu?

June 15, 2026
Dunkulewar Kasa Shi Ne Burin Bai Daya Na Jama’ar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan

Dunkulewar Kasa Shi Ne Burin Bai Daya Na Jama’ar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan

June 15, 2026
Daraktoci Da Jami’an FCT 7 Na Fuskantar Tuhume-tuhume Kan Badakar Fili

Mariya Mahmoud: Aiki A karkashin Jagorancin Wike

June 15, 2026
Auren Gata: Babu Saki Sai Da Amincewar Hisbah – Daurawa

Gwamnatin Kano Ta Ware Naira Biliyan 1.5 Domin Aurar Da Ma’aurata 1,500

June 15, 2026
Sin Na Gina Karfin Sojinta Ne Saboda Kare Moriyar Tsaron Kasa

Sin Na Gina Karfin Sojinta Ne Saboda Kare Moriyar Tsaron Kasa

June 15, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Fara Shari’ar Fiye Da Mutane 400 Da Ake Zargi Da Ta’addanci A Abuja

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Shari’ar Fiye Da Mutane 400 Da Ake Zargi Da Ta’addanci A Abuja

June 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.