• English
  • Business News
Tuesday, July 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Majar Atiku Da Obi Da Kwankwaso Ta Fada Shakku

by Yusuf Shuaibu
9 months ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
2027: Majar Atiku Da Obi Da Kwankwaso Ta Fada Shakku
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Akwai alamun da ke nuna cewa tattaunawar maja a tsakanin Atiku Abubakar, Peter Obi, da kuma Rabiu Kwankwaso ta cika da shakku game da yiwuwarta.

Shakkun dai ya dabaibaye majan ne tun lokacin daKwankwaso, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP a zaben 2023, ya bayyana cewa shi ne zai lashe zaben shugaban kasa a 2027.

  • Bangaren Sin Ya Yi Kira Ga Bangarori Biyu Dake Rikici A Sudan Da Su Yayyafawa Rikicin Kasar Ruwa
  • Dakta Gadan-ƙaya Ya Bada Haƙuri Kan Zargin Auren Jinsi Da Ya Yi A Bauchi

Rahotanni sun nuna cewa jagorar jam’iyyar NNPP ya yi wannan furuci ne a lokacin da ya kaddamar da sakatariyar jam’iyyar a Jihar Katsina kwanan nan.

Tsohon gwamnan Jihar Kano, wanda Atiku da Obi suka yi zawarcinsa, ya ci gaba da cewa jam’iyyarsa ta NNPP a shirye take ta karbi ragamar shugabancin kasa, jihohi da sauran mukamai a fadin Nijeriya a zaben 2027.

Baya ga sanarwar tasa, Kwankwaso ya yi ikirarin cewa jam’iyyar PDP ta riga ta mutu, kuma ta fita daga kan layi.

Labarai Masu Nasaba

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

“Ina so in tunatar da ku cewa jam’iyyar PDP ta riga ta mutu, saboda da muna cikin jam’iyyar, tun da suka fita daga kan layi, muka yanke shawarar barin jam’iyyar,” in ji shi.

Kafin kalamun na Kwankwaso, jam’iyyar PDP ta bayyana cewa manyan jiga-jigan ‘yan adawa na neman hadaka domin kalubalantar APC a zab0en 2027.

Mataimakin sakataren yada labarai na jam’iyyar PDP na asa, Ibrahim Abdullahi, ne ya bayyana haka a lokacin da yake tattaunawa a gidan talabijin na Channels.

Abdullahi ya tabbatar da cewa Atiku, Obi, da Kwankwaso suna tattaunawa kan yiwuwar yin kawance.

Ya koka da yadda jam’iyyar ta yi asarar kuri’u sama da miliyan daya, inda ya kara da cewa da Kwankwaso ko Obi sun ci gaba da zama a jam’iyyar, “da mun rufe gibi da kuma kauce wa matsalolin siyasa da tattalin arziki da ake ciki a yanzu.

“Tabbas. Ana ci gaba da tattaunawa. Kun ga Peter Obi yana tattaunawa da Atiku. Kun ga Peter Obi yana ganawa da el-Rufai,” inji Abdullahi, inda ya kara da cewa jam’iyyarsu na kokarin ganin Obi, Kwankwaso, da sauran shugabannin da suka bar PDP sun jam’iyyar kafin zaben 2027.

“Daya daga cikinsu zai yarda da sauran, sannan za mu sami alkibla. Damuwarmu a matsayin jam’iyya da kuma wadannan mutanen da na ambata shi ne za su ceto ‘yan Nijeriya daga irin wannan kunci da yunwa da fatara da rashin tsaro da ke damun kasar nan,” ya kara shaidawa.

Idan za a iya tuna kafin zaben 2023, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Atiku, a wata hira da BBC, ya yi nuni da cewa akwai yiwuwar kawance da Obi da Kwankwaso, amma hakan bai faruwa ba.

Bugu da kari, an kuma samu rashin nasara a tattaunawar da aka yi kan kawance tsakanin Peter Obi na jam’iyyar LP da Rabiu Kwankwaso na NNPP, a daya bangaren.

Da yake magana a wata hira da ya yi da gidan talabijin na News Central, Obi ya ce ba ya neman shugabancin Nijeriya ta kowacce hanya.

Ya ce zai amince a yi aiki tare da wasu ne kawai idan ya ga mutanen da za su iya yin aikin da kyau.

A cewarsa, ba zai hada kai da kowa ba don manufar kama jihar ko kuma ya ci zabe.

Masana harkokin siyasa na nuna shakku kan kawancin Atiku da Kwankwaso da kuma Obi wajen kawar da jam’iyyar APC daga kan karagar mulkin Nijeriya. Wanda suke ganin kamar an samu matsala duba da irin kalamun da Kwankwaso ya furta da kuma irin martanin da PDP ta mayar masa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 2027AtikuKwankwasoMajaObiSiyasa
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Gudanar Da Bikin “A Rubuce A Sama: Labarina Na Kasar Sin” Don Murnar Cika 75 Da Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Kasar Sin A Abuja

Next Post

Rawar Da Masu Sa Ido Ke Takawa Wajen Magudin Zabe A Nijeriya

Related

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

2 weeks ago
APC
Tambarin Dimokuradiyya

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

2 weeks ago
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

3 weeks ago
‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

1 month ago
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

1 month ago
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

1 month ago
Next Post
Rawar Da Masu Sa Ido Ke Takawa Wajen Magudin Zabe A Nijeriya

Rawar Da Masu Sa Ido Ke Takawa Wajen Magudin Zabe A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

June 30, 2025
Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

June 30, 2025
Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

June 30, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

June 30, 2025
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

June 30, 2025
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

June 30, 2025
CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

June 30, 2025
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

June 30, 2025
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

June 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.