ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dubun Wani Dan Shekara 74 Da Ake Zargi Da Sace Tabarmi A Masallaci Ta Cika

by Abubakar Abba
2 years ago
Dubun

Dubun wani tsoho dan shekara 74 mai suna Jibrin Musa mazauni a gudunmar Rigasa ta Karamar Hukumar Igabi da ke a Jihar Kaduna ta cika, biyo bayan kama shi da aka yi yana satar Tabarmar wani Masallacin unguwa da ke yankin.

Jibrin wanda yake da zama a layin Turaki da ke a yankin. An kama shi ne, bisa zargin satar Tabarma a wani Masallaci da ke a layin Sarkin Bori Sule da ke a yankin.

  • Sin Ta Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Danyen Aikin Dake Barazanar Jefa Yankin Cikin Wani Bala’i
  • 2027: Majar Atiku Da Obi Da Kwankwaso Ta Fada Shakku

A hirarsa da wakilinmu, jim kadan bayan kama shi, tsohon ya ce, “ Ba zargi bane, tun da an kama ni na saci Tabarmar, ” in ji shi.

ADVERTISEMENT

Ya ce, “Na shafe shekaru goma ina satar sabbin shinfidun Sallah a masallatai daban daban da ke a yankin da Agon Bango na masallatai, amma ban cika yawan satar Alkur’anai a masallatai ba ”.

Ya ci gaba da cewa,“ Na kan shiga cikin mallatai ne in yi satar kamar idan an idar da ko dai Sallar Azahar ko ta La’sar, wani lokacin ma da ni ake yin Sallar, sai in sace sabbin tabarmin in sanya a cikin babbar Leda in boye su a cikin babbar Rigar da nake sanye da ita, in fice daga masallacin in je in sayar da su”.

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Wani Mamba Na NYSC A Harin Fashi Da Makami A Abuja

An Cafke Mutum 7 Kan Satar Waya Da Fasa Gidaje A Jihar Yobe

Ya kara da cewa,“ Na kan sayar da kowacce daya daga Naira 1,500 zuwa Naira 2,000, wannan shi ne karo na biyu da na saci tabarma a wannan masallacin”.

Daya daga cikin ‘yan kwamitin Masallacin Miftahu Ibrahim ya shaida wa LEADERSHIP Hausa yadda su kama kama tsohon, inda ya ce, “ An dade ana yi mana satar kayayyaki a Masallacin ciki har da Tabarmin Sallah da sauran wasu kaya”.

“ Na zo Masallacin na bude na share shi aka kuma gabatar da Sallar Azahar, sai ni da wani abokina muka tashi muka fita wajen Masallacin, sai ga tsohon ya shiga cikin Masallacin, can zuwa jimawa kadan ya fito daga cikin Masallacin ya zagaya bayan Masallacin kamar zai kama ruwa,” in ji shi.

Ya kara da cewa, “Bayan da tsohon ya wuce, sai na leka cikin Masallacin na ga ba wata Tabarma, sai muka bishi a baya, muka ce masa ya dakata, bayan ya dakata sai muka ce masa ina Tabarmarmu da ya dauka a cikin Masallaci, sai ya fito da ita a nade, daga cikin babbar rigarsa”.

Shi ma Na’ibin Masallacin Malam Muhammad Shu’aibu ya shaida wa wakilinmu cewa,” Saboda yawan sace-sacen a Masallacin har ta kai ga a tsakaninmu ‘yan kwamitin Masallacin muna zargin junanmu, da sauran wasu mutanen layin”.

Shi kuwa Mai Anguwar da ke a layin, Malam Aminu Alasan ya shaida wa LEADERSHIP Hausa cewa, akwai Masallatai da dama a layin da ake korafen-korafen satar kaya a Masallati, inda muka dukufa yin addu’ar sai gashi a kama wannan tsohon.

Dubun
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Kwara Na Zuba Dala Biliyan 70 A Fannin Kiwon Dabbobi
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Cibiyar IAR Ta Gudanar Da Ayyukan Bincike 140 Kan Sabbin Amfanin Gona 

MASU ALAKA

An Kashe Wani Mamba Na NYSC A Harin Fashi Da Makami A Abuja
Kotu Da Ɗansanda

An Kashe Wani Mamba Na NYSC A Harin Fashi Da Makami A Abuja

May 2, 2026
An Kama Matashi A Kano Kan Zargin Kashe Abokinsa
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Mutum 7 Kan Satar Waya Da Fasa Gidaje A Jihar Yobe

April 25, 2026
An Sake Samun Gawar Wani Dan Nijeriya A Gidansa Da Ke Burtaniya
Kotu Da Ɗansanda

An Sake Samun Gawar Wani Dan Nijeriya A Gidansa Da Ke Burtaniya

April 25, 2026
Next Post
CAC Da Masu POS Sun Amince Da Wa’adin Mako Biyu Don Rijista

CBN Ya Kaddamar Da Sabbin Ka’idoji Ga Masu Harkar POS

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.