ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dubun Wani Dan Shekara 74 Da Ake Zargi Da Sace Tabarmi A Masallaci Ta Cika

by Abubakar Abba
2 years ago
Dubun

Dubun wani tsoho dan shekara 74 mai suna Jibrin Musa mazauni a gudunmar Rigasa ta Karamar Hukumar Igabi da ke a Jihar Kaduna ta cika, biyo bayan kama shi da aka yi yana satar Tabarmar wani Masallacin unguwa da ke yankin.

Jibrin wanda yake da zama a layin Turaki da ke a yankin. An kama shi ne, bisa zargin satar Tabarma a wani Masallaci da ke a layin Sarkin Bori Sule da ke a yankin.

  • Sin Ta Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Danyen Aikin Dake Barazanar Jefa Yankin Cikin Wani Bala’i
  • 2027: Majar Atiku Da Obi Da Kwankwaso Ta Fada Shakku

A hirarsa da wakilinmu, jim kadan bayan kama shi, tsohon ya ce, “ Ba zargi bane, tun da an kama ni na saci Tabarmar, ” in ji shi.

ADVERTISEMENT

Ya ce, “Na shafe shekaru goma ina satar sabbin shinfidun Sallah a masallatai daban daban da ke a yankin da Agon Bango na masallatai, amma ban cika yawan satar Alkur’anai a masallatai ba ”.

Ya ci gaba da cewa,“ Na kan shiga cikin mallatai ne in yi satar kamar idan an idar da ko dai Sallar Azahar ko ta La’sar, wani lokacin ma da ni ake yin Sallar, sai in sace sabbin tabarmin in sanya a cikin babbar Leda in boye su a cikin babbar Rigar da nake sanye da ita, in fice daga masallacin in je in sayar da su”.

LABARAI MASU NASABA

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

Ya kara da cewa,“ Na kan sayar da kowacce daya daga Naira 1,500 zuwa Naira 2,000, wannan shi ne karo na biyu da na saci tabarma a wannan masallacin”.

Daya daga cikin ‘yan kwamitin Masallacin Miftahu Ibrahim ya shaida wa LEADERSHIP Hausa yadda su kama kama tsohon, inda ya ce, “ An dade ana yi mana satar kayayyaki a Masallacin ciki har da Tabarmin Sallah da sauran wasu kaya”.

“ Na zo Masallacin na bude na share shi aka kuma gabatar da Sallar Azahar, sai ni da wani abokina muka tashi muka fita wajen Masallacin, sai ga tsohon ya shiga cikin Masallacin, can zuwa jimawa kadan ya fito daga cikin Masallacin ya zagaya bayan Masallacin kamar zai kama ruwa,” in ji shi.

Ya kara da cewa, “Bayan da tsohon ya wuce, sai na leka cikin Masallacin na ga ba wata Tabarma, sai muka bishi a baya, muka ce masa ya dakata, bayan ya dakata sai muka ce masa ina Tabarmarmu da ya dauka a cikin Masallaci, sai ya fito da ita a nade, daga cikin babbar rigarsa”.

Shi ma Na’ibin Masallacin Malam Muhammad Shu’aibu ya shaida wa wakilinmu cewa,” Saboda yawan sace-sacen a Masallacin har ta kai ga a tsakaninmu ‘yan kwamitin Masallacin muna zargin junanmu, da sauran wasu mutanen layin”.

Shi kuwa Mai Anguwar da ke a layin, Malam Aminu Alasan ya shaida wa LEADERSHIP Hausa cewa, akwai Masallatai da dama a layin da ake korafen-korafen satar kaya a Masallati, inda muka dukufa yin addu’ar sai gashi a kama wannan tsohon.

Dubun
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

MASU ALAKA

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Kotu Da Ɗansanda

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

June 18, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Next Post
CAC Da Masu POS Sun Amince Da Wa’adin Mako Biyu Don Rijista

CBN Ya Kaddamar Da Sabbin Ka’idoji Ga Masu Harkar POS

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.