ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dubun Wani Dan Shekara 74 Da Ake Zargi Da Sace Tabarmi A Masallaci Ta Cika

by Abubakar Abba
2 years ago
Dubun

Dubun wani tsoho dan shekara 74 mai suna Jibrin Musa mazauni a gudunmar Rigasa ta Karamar Hukumar Igabi da ke a Jihar Kaduna ta cika, biyo bayan kama shi da aka yi yana satar Tabarmar wani Masallacin unguwa da ke yankin.

Jibrin wanda yake da zama a layin Turaki da ke a yankin. An kama shi ne, bisa zargin satar Tabarma a wani Masallaci da ke a layin Sarkin Bori Sule da ke a yankin.

  • Sin Ta Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Danyen Aikin Dake Barazanar Jefa Yankin Cikin Wani Bala’i
  • 2027: Majar Atiku Da Obi Da Kwankwaso Ta Fada Shakku

A hirarsa da wakilinmu, jim kadan bayan kama shi, tsohon ya ce, “ Ba zargi bane, tun da an kama ni na saci Tabarmar, ” in ji shi.

ADVERTISEMENT

Ya ce, “Na shafe shekaru goma ina satar sabbin shinfidun Sallah a masallatai daban daban da ke a yankin da Agon Bango na masallatai, amma ban cika yawan satar Alkur’anai a masallatai ba ”.

Ya ci gaba da cewa,“ Na kan shiga cikin mallatai ne in yi satar kamar idan an idar da ko dai Sallar Azahar ko ta La’sar, wani lokacin ma da ni ake yin Sallar, sai in sace sabbin tabarmin in sanya a cikin babbar Leda in boye su a cikin babbar Rigar da nake sanye da ita, in fice daga masallacin in je in sayar da su”.

LABARAI MASU NASABA

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

Ya kara da cewa,“ Na kan sayar da kowacce daya daga Naira 1,500 zuwa Naira 2,000, wannan shi ne karo na biyu da na saci tabarma a wannan masallacin”.

Daya daga cikin ‘yan kwamitin Masallacin Miftahu Ibrahim ya shaida wa LEADERSHIP Hausa yadda su kama kama tsohon, inda ya ce, “ An dade ana yi mana satar kayayyaki a Masallacin ciki har da Tabarmin Sallah da sauran wasu kaya”.

“ Na zo Masallacin na bude na share shi aka kuma gabatar da Sallar Azahar, sai ni da wani abokina muka tashi muka fita wajen Masallacin, sai ga tsohon ya shiga cikin Masallacin, can zuwa jimawa kadan ya fito daga cikin Masallacin ya zagaya bayan Masallacin kamar zai kama ruwa,” in ji shi.

Ya kara da cewa, “Bayan da tsohon ya wuce, sai na leka cikin Masallacin na ga ba wata Tabarma, sai muka bishi a baya, muka ce masa ya dakata, bayan ya dakata sai muka ce masa ina Tabarmarmu da ya dauka a cikin Masallaci, sai ya fito da ita a nade, daga cikin babbar rigarsa”.

Shi ma Na’ibin Masallacin Malam Muhammad Shu’aibu ya shaida wa wakilinmu cewa,” Saboda yawan sace-sacen a Masallacin har ta kai ga a tsakaninmu ‘yan kwamitin Masallacin muna zargin junanmu, da sauran wasu mutanen layin”.

Shi kuwa Mai Anguwar da ke a layin, Malam Aminu Alasan ya shaida wa LEADERSHIP Hausa cewa, akwai Masallatai da dama a layin da ake korafen-korafen satar kaya a Masallati, inda muka dukufa yin addu’ar sai gashi a kama wannan tsohon.

Dubun
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Yadda Bikin Girke-girke Ya Karfafa Alaka Tsakanin Musulmai Da Kiristoci A Kaduna
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

MASU ALAKA

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota
Kotu Da Ɗansanda

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

July 18, 2026
An Kama Matashi A Kano Kan Zargin Kashe Abokinsa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

July 18, 2026
Disu
Kotu Da Ɗansanda

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

June 26, 2026
Next Post
CAC Da Masu POS Sun Amince Da Wa’adin Mako Biyu Don Rijista

CBN Ya Kaddamar Da Sabbin Ka’idoji Ga Masu Harkar POS

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.