• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Duk Sanda Na Dora Biro Zan Yi Rubutu, Nishadi Da Annashuwa Na Lullube Zuciyata – Maryam

by Sulaiman
1 year ago
in Adabi
0
Duk Sanda Na Dora Biro Zan Yi Rubutu, Nishadi Da Annashuwa Na Lullube Zuciyata – Maryam
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

MARYAM ABDUL’AZIZ wacce aka fi sani da MAI KOSAI tana daya daga cikin matasa marubutu musaman a kafofin sadarwa na zamani. Ta bayyana wa masu karatun irin gwagwarmayar da ta sha wajen ganin ta fara isar da sakonni ga al’umma ta fannin rubuce-rubuce, har ma da wasu bayanan masu yawa. Ga dai tattaunawarta tare da PRINCESS FATIMA ZARAH MAZADU Kamar haka:

Ya sunan marubuciyar?
Sunana Maryam Abdulaziz, wacce a duniyar Marubuta a ka fi sanina da Mai Kosai.

Ko za ki fada wa masu karatu dan takaitaccen tarihinki?
An haife ni a garin Kano na taso a garin Kano, inda na yi karatun firamare da karamar sakandare a makarantar ‘Ikramul-Adfal’, daga nan na zana jarrabawar ‘Science and Technical’ inda na samu nasara har na tafi makarantar ‘Girls Science College (Garko), na kammala babbar sakandare a shekarar 2016 ban samu damar ci gaba da karatuna ba sai a shekarar 2019 in da na tafi makarantar ‘Aminu Kano College Of Education (Akcoe)’ na yi NCE a can. Yanzu haka ina nan ina kasuwancina kasancewar an gama karatu amma ba a samu aiki ba. Bangaren karatun islamiyya kuwa na yi makarantu da dama, daga ciki na yi ‘Madarasutul Tahfizul Kur’an’ da ke nan Mandawari kusa da ‘Sahad Store’, a nan na sauke alkur’ani mai girma, na kuma haddace wani abu daga ciki, na yi ‘As’habul khafi’, ita ma na yi sauka a nan, na yi ‘Sheik Jafar’, sai dai ban kai ga yin sauka ba wani uzuri ya yanko wa rayuwata na bar makarantar, kadan daga cikin makarantun da na yi ke nan na islamiyya. Ina da aure, sannan ina kuma tare da iyayena da kuma kannena.

Me ya ja hankalinki har ki ka tsunduma fannin rubutu?
Abin da ya ja hankalina na fara rubutu shi ne; Ganin yadda mutane da dama suke kaunar karanta littafi, sai na ce to ai zan iya ni ma rubuta labarina wanda daga haka zan isar da sakona cikin sauki ga al’umma, tun da na ga sun raja’a kan karatun littafi da saurara, kuma ta wannan hanyar ana iya nunawa al’umma hanyar gyara da ci gaba.

Ya gwagwarmayar farawar ta kasance?
To gwagwarmaya an sha ba a sha ba, sai dai zan iya cewa lokacin da na fara rubutu Alhamdu lillah, kuma a duk sanda na dora biro kan littafi na yi rubutu ina jin wani nishadi da anshuwa suna lullube zuciyata, sai dai kawai na ce Alhamdulillah amma dai an sha gwagwarmaya, musamman da ya kasance lokacin ina Jss 2 na fara rubutu, to ko gida iyayena ba su sani ba haka kuma kullum cikin taka-tsan-tsan nake ka da wani ya ankara, saboda ko littafin idan na yi rubutu cikinsa ajjiya nake bayarwa gudun kada a gani a ce za a hana ni zuwa makarantar ma gaba daya, tun da za a ce ke nan ba karatu nake yi ba sai wasa.

Labarai Masu Nasaba

Marubutan Batsa Ku Ji Tsoron Allah -Emili

Dr. Maryam Yola Ta Zama Farfesa Mace Ta Farko Kan Magungunan Gargajiya Da Al’adun Hausa

nishadi

Ya farkon farawar ya kasance?
To farkon fara rubutuna da dare nake yi, saboda ina ganin kar na yi rubutu a gwasale ni, a ce sam-sam bai yi ba, sannan kuma ga gida ba su sani ba, ko lokacin da nake ‘boarding’ idan na ji ‘idea’ ta fado na kan dau littafi na rubuta, don har ‘yan ajinmu suka gano ai ina rubuta littafi, tunda wani lokacin za a ari littafina to a tsakiya ko can karshe za a ci karo da labari. Haka bayan na gama makaranta ko da na dawo gida ban saki jikina ba saboda gudun kar a gano a yi min fada, wanda daga karshe kuma na jajirce na yi ta maza na cire tsoro na tunkari mamanmu da batun, Alhamdu lillah kuma ta goya min baya ta karfafa min guiwa, mahaifina kuwa da ta sanar masa bai hana ba ya ce ai abu ne mai kyau amma indai san abin da zan dinga rubutawa wanda zai kawo wa al’umma ci gaba, wanda mutane idan sun karanta za su karu ba wanda za a yi Alla-wadai da ni ba.

Kamar wane bangare kika fi maida hankali a kai wajen yin rubutu?
Na fi mayar da hankalina wajen rubuta labarin Soyayya, zamantakewa, musamman tsakanin ma’aurata da kuma yanayin rayuwa.

Za ki yi kamar shekara nawa da fara rubutu?
Na shafe a kalla shekaru goma zuwa sha daya, idan a online ne kuma shekaru takwas.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan Mataadabin rubutuNishadin rayuwa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci Fitar Da Dala Miliyan Biyar Daga Asusun IFAD Don Bunkasa Noma

Next Post

Jami’ar MAU Ta Yaye Dalibai Dubu 5,545 A Yola

Related

Marubutan Batsa Ku Ji Tsoron Allah -Emili
Adabi

Marubutan Batsa Ku Ji Tsoron Allah -Emili

2 months ago
Dr. Maryam Yola Ta Zama Farfesa Mace Ta Farko Kan Magungunan Gargajiya Da Al’adun Hausa
Al'adu

Dr. Maryam Yola Ta Zama Farfesa Mace Ta Farko Kan Magungunan Gargajiya Da Al’adun Hausa

5 months ago
Farfesa Zaynab Alkali: Mace Ta Farko Da Ta Zama Marubuciyar Littattafai Daga Arewacin Nijeriya
Adabi

Farfesa Zaynab Alkali: Mace Ta Farko Da Ta Zama Marubuciyar Littattafai Daga Arewacin Nijeriya

6 months ago
Na Fi Jin Dadin Rubutu In Na Gaji Tibis – Maryam Faruk
Adabi

Na Fi Jin Dadin Rubutu In Na Gaji Tibis – Maryam Faruk

7 months ago
Mahaifiyata Ce Ta Karfafe Ni Shiga Harkar Rubutu –Maryam Faruk
Adabi

Mahaifiyata Ce Ta Karfafe Ni Shiga Harkar Rubutu –Maryam Faruk

7 months ago
Yadda Malaminmu Na Hausa Ya Karfafa Min Kwarin Gwiwar Fara Rubutu – Salma Ahmad
Adabi

Yadda Malaminmu Na Hausa Ya Karfafa Min Kwarin Gwiwar Fara Rubutu – Salma Ahmad

9 months ago
Next Post
Jami’ar MAU Ta Yaye Dalibai Dubu 5,545 A Yola

Jami'ar MAU Ta Yaye Dalibai Dubu 5,545 A Yola

LABARAI MASU NASABA

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 5, 2025
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

June 5, 2025
Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

June 5, 2025
Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

June 5, 2025
‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

June 5, 2025
Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

June 5, 2025
Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

June 5, 2025
Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

June 5, 2025
Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

June 5, 2025
Wani Injin Jirgi Mai Saukar Ungulu Kirar Kasar Sin Ya Samu Shaidar Amincewa 

Wani Injin Jirgi Mai Saukar Ungulu Kirar Kasar Sin Ya Samu Shaidar Amincewa 

June 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.