ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Duk Sanda Na Dora Biro Zan Yi Rubutu, Nishadi Da Annashuwa Na Lullube Zuciyata – Maryam

by Sulaiman
2 years ago
nishadi

MARYAM ABDUL’AZIZ wacce aka fi sani da MAI KOSAI tana daya daga cikin matasa marubutu musaman a kafofin sadarwa na zamani. Ta bayyana wa masu karatun irin gwagwarmayar da ta sha wajen ganin ta fara isar da sakonni ga al’umma ta fannin rubuce-rubuce, har ma da wasu bayanan masu yawa. Ga dai tattaunawarta tare da PRINCESS FATIMA ZARAH MAZADU Kamar haka:

Ya sunan marubuciyar?
Sunana Maryam Abdulaziz, wacce a duniyar Marubuta a ka fi sanina da Mai Kosai.

Ko za ki fada wa masu karatu dan takaitaccen tarihinki?
An haife ni a garin Kano na taso a garin Kano, inda na yi karatun firamare da karamar sakandare a makarantar ‘Ikramul-Adfal’, daga nan na zana jarrabawar ‘Science and Technical’ inda na samu nasara har na tafi makarantar ‘Girls Science College (Garko), na kammala babbar sakandare a shekarar 2016 ban samu damar ci gaba da karatuna ba sai a shekarar 2019 in da na tafi makarantar ‘Aminu Kano College Of Education (Akcoe)’ na yi NCE a can. Yanzu haka ina nan ina kasuwancina kasancewar an gama karatu amma ba a samu aiki ba. Bangaren karatun islamiyya kuwa na yi makarantu da dama, daga ciki na yi ‘Madarasutul Tahfizul Kur’an’ da ke nan Mandawari kusa da ‘Sahad Store’, a nan na sauke alkur’ani mai girma, na kuma haddace wani abu daga ciki, na yi ‘As’habul khafi’, ita ma na yi sauka a nan, na yi ‘Sheik Jafar’, sai dai ban kai ga yin sauka ba wani uzuri ya yanko wa rayuwata na bar makarantar, kadan daga cikin makarantun da na yi ke nan na islamiyya. Ina da aure, sannan ina kuma tare da iyayena da kuma kannena.

ADVERTISEMENT

Me ya ja hankalinki har ki ka tsunduma fannin rubutu?
Abin da ya ja hankalina na fara rubutu shi ne; Ganin yadda mutane da dama suke kaunar karanta littafi, sai na ce to ai zan iya ni ma rubuta labarina wanda daga haka zan isar da sakona cikin sauki ga al’umma, tun da na ga sun raja’a kan karatun littafi da saurara, kuma ta wannan hanyar ana iya nunawa al’umma hanyar gyara da ci gaba.

Ya gwagwarmayar farawar ta kasance?
To gwagwarmaya an sha ba a sha ba, sai dai zan iya cewa lokacin da na fara rubutu Alhamdu lillah, kuma a duk sanda na dora biro kan littafi na yi rubutu ina jin wani nishadi da anshuwa suna lullube zuciyata, sai dai kawai na ce Alhamdulillah amma dai an sha gwagwarmaya, musamman da ya kasance lokacin ina Jss 2 na fara rubutu, to ko gida iyayena ba su sani ba haka kuma kullum cikin taka-tsan-tsan nake ka da wani ya ankara, saboda ko littafin idan na yi rubutu cikinsa ajjiya nake bayarwa gudun kada a gani a ce za a hana ni zuwa makarantar ma gaba daya, tun da za a ce ke nan ba karatu nake yi ba sai wasa.

LABARAI MASU NASABA

Tarurrukan Daidaita Ƙa’idojin Rubutun Hausa Cikin Tarihi (1980-2021): Guzurin Ranar Hausa ta Duniya

Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta

nishadi

Ya farkon farawar ya kasance?
To farkon fara rubutuna da dare nake yi, saboda ina ganin kar na yi rubutu a gwasale ni, a ce sam-sam bai yi ba, sannan kuma ga gida ba su sani ba, ko lokacin da nake ‘boarding’ idan na ji ‘idea’ ta fado na kan dau littafi na rubuta, don har ‘yan ajinmu suka gano ai ina rubuta littafi, tunda wani lokacin za a ari littafina to a tsakiya ko can karshe za a ci karo da labari. Haka bayan na gama makaranta ko da na dawo gida ban saki jikina ba saboda gudun kar a gano a yi min fada, wanda daga karshe kuma na jajirce na yi ta maza na cire tsoro na tunkari mamanmu da batun, Alhamdu lillah kuma ta goya min baya ta karfafa min guiwa, mahaifina kuwa da ta sanar masa bai hana ba ya ce ai abu ne mai kyau amma indai san abin da zan dinga rubutawa wanda zai kawo wa al’umma ci gaba, wanda mutane idan sun karanta za su karu ba wanda za a yi Alla-wadai da ni ba.

Kamar wane bangare kika fi maida hankali a kai wajen yin rubutu?
Na fi mayar da hankalina wajen rubuta labarin Soyayya, zamantakewa, musamman tsakanin ma’aurata da kuma yanayin rayuwa.

Za ki yi kamar shekara nawa da fara rubutu?
Na shafe a kalla shekaru goma zuwa sha daya, idan a online ne kuma shekaru takwas.

nishadi
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna
  • Sulaiman
    Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba
  • Sulaiman
    Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa
  • Sulaiman
    Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

MASU ALAKA

Tarurrukan Daidaita Ƙa’idojin Rubutun Hausa Cikin Tarihi (1980-2021): Guzurin Ranar Hausa ta Duniya
Adabi

Tarurrukan Daidaita Ƙa’idojin Rubutun Hausa Cikin Tarihi (1980-2021): Guzurin Ranar Hausa ta Duniya

August 26, 2026
Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta
Adabi

Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta

May 31, 2026
Zambar Kudi: Kotu Ta Tasa Keyar Dillalin Gidaje Zuwa Gidan Kaso
Adabi

EFCC Ta Kama Mutum 11 Masu Hakar Ma’adanai Ba Bisa Ka’ida Ba A Kwara

February 6, 2026
Next Post
Jami’ar MAU Ta Yaye Dalibai Dubu 5,545 A Yola

Jami'ar MAU Ta Yaye Dalibai Dubu 5,545 A Yola

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.