ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jami’ar MAU Ta Yaye Dalibai Dubu 5,545 A Yola

by Muh'd Shafi'u Saleh
2 years ago
Jami'ar

Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri na jihar Adamawa, ya bukaci daliban da suka kammala karatu a jami’ar koyarwa ta Modibbo Adama da ke Yola (MAU), da su tashi tsaye da yin aiki tukuru, wajen tunkarar kalubalen da Nijeriya ke fuskanta a halin yanzu da nan gaba.

Fintiri wanda mataimakiyarsa Farfesa Kaletapwa Farauta ta wakilta, ya bayyana haka lokacin da yake jawabi a taron yaye daliban jami’ar karo na 28 ranar Asabar a Yola, ya ce jami’ar ta yi kokari na kyankyasa, da kuma yaye daliban da za su bayar da tallafin da kasa ke bukata.

  • Cutar Kyanda Ta Yi Ajalin Mutum 42 A Adamawa
  • Dan Majalisa Ya Kaddamar Da Ajujuwa 3 A Firamare A Adamawa

Ya ci gaba da cewa “dukkanmu mun taru ba kawai domin mu muku tafi kawai don kun samu nasara ba, amma sai don taya ku murna don samun kyakkyawar makoma mai dorewa,” in ji Fintiri.

ADVERTISEMENT

Haka kuma gwamna Ahmadu Fintiri, ya taya mataimakin shugaban jami’ar Farfesa Abdullahi Liman, murnar kammala shekaru biyar na shugabancin jami’ar, ya kuma taya mataimakin shugaban jami’ar murnar shirya taron yaye dalibai sau uku a cikin shekaru biyar.

Da yake jawabin bude taron tunda farko shugaban jami’ar Sarkin Akwa Ibom Mai Martaba Okuku Uwa Umoh Adiaka na 3 kuma mai rike da sarautar karamar hukumar Obot Akara, ya taya daliban da aka yayen murna da nasarar da suka samu.

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

Haka shima mataimakin shugaban jami’ar Farfesa Abdullahi Liman Tukur, ya amince da cewa ya cimma nasarorin ciyar da ci gaba da manufa da manufofin jami’ar ne da goyon baya, ya ce da ba zai samu ba idan bai samu hadin Kai da goyon baya ba.

Dalibai jimla dubu 5,545, suka kammala karatu a shekarar karatun ta 2022/3 a jami’ar, da suka hada da masu difloma 458, da 4,282 a fannin Digiri na farko, da zangon farko 53, zango na biyu 1,143 na sama, 2,376 a matakin kasa na biyu, zango uku 682 da digiri 28.

A bangaren digiri na farko, an kuma ba da takardar shaidar kammala digiri ga dalibai 41, masu digiri na biyu 630 da kuma Ph.D 134 a fannoni daban-daban.

Jami'ar
Muh'd Shafi'u Saleh
+ postsBio
  • Muh'd Shafi'u Saleh
    https://hausa.leadership.ng/author/muhd-shafiu-saleh/
    Jami’in Tsaro Ya Mayar da Dala 505 Da Riyal 30 Da Ya Tsinta A Yola
  • Muh'd Shafi'u Saleh
    https://hausa.leadership.ng/author/muhd-shafiu-saleh/
    Shahararren Malamin Addinin Islama A Adamawa Sheikh Ibrahim Abubakar Daware Ya Rasu
  • Muh'd Shafi'u Saleh
    https://hausa.leadership.ng/author/muhd-shafiu-saleh/
    An Yi Wa ‘Yansanda 110 Ƙarin Girma A Adamawa
  • Muh'd Shafi'u Saleh
    https://hausa.leadership.ng/author/muhd-shafiu-saleh/
    Gwamna Fintiri Ya Nada Sabbin Sarakuna 7 A Jihar Adamawa

MASU ALAKA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna
Labarai

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba
Labaran Kasuwanci

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Next Post
‘Yan Mata Mu Yi Karatu Sannan Mu Kama Sana’a – Khadija Sambo

‘Yan Mata Mu Yi Karatu Sannan Mu Kama Sana’a - Khadija Sambo

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.