ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, November 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

EFCC Ta Cafke Wadanda Suka Damfari Attajiri Aminu Dantata

by Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
EFCC

Hukumar korafe-korafen al’umma da yaki da cin hanci da rashawa ta Jihar Kano ta sanar da samun nasarar kama wasu mutum biyu da suka damfari wani dattijo Alhaji Aminu Dantata da tsohon minista Alhaji A.T. Gwarzo.

Bugu da kari, hukumar ta kwato Naira miliyan 5, daga hannun wadanda aka kama din sun damfari daga hannun hamshakin dan kasuwar, ciki har da Naira miliyan daya mallakin tsohon ministar bayan gurfanar da su gaban kotu.

  • EFCC Za Ta Binciki Yadda Kudaden Kananan Hukumomi Ke Sulalewa
  • Shugabannin Sin Da UAE Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 40 Da Kafuwar Huldar Diflomasiyya Tsakaninsu

Da yake zantawa da manema labarai jim kadan bayan kammala zaman kotun, lauyan masu shigar da kara Zahraddeen Hamisu Kofarmata ya bayyana cewa Bukar Galadima da Sulyman Ahmed sun shirya tare da aiwatar da wani shiri na damfarar wadanda abin ya shafa.

ADVERTISEMENT

Bukar Galadima ya yi sojan gona da sunan Tsohon Ministan Babban Birnin Tarayya, Mohammed Abba Gana, inda nuna tsohon ministan ba shi da lafiya, ya kuma nemi taimakon Aminu Dantata, inda ya bukaci Naira miliyan 5 domin a yi masa magani, daga nan sai Dantata ya umarce shi da ya ba shi bayanan asusun ajiyarsa. A maimakon ya bayar da nasa, Galadima ya bayar da bayanan matarsa, Sadiyya Abba.

Daga nan ne dan kasuwar ya mika Naira miliyan 5 zuwa asusun ajiyar kudi domin tallafa wa wanda ke jinya.

LABARAI MASU NASABA

An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa

An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

Babban mai laifin da ke zaune a Kano, sai ya aika da Naira 500,000 ga wanda ya taimaka masa a Abuja, yayin da ya ajiye wa kansa Naira miliyan 4.5.

Daga baya, da Dantata ya tuntubi tsohon ministan don duba lafiyarsa, sai ya gane cewa an zambace shi, ya kai karar hukumar korafe-korafen jama’a da yaki da cin hanci da rashawa ta Jihar Kano, inda ta fara bincike.

An kama mutanen biyu ne kuma aka gurfanar da su a gaban Kotun Majistare mai lamba 24 da ke Kano.

Alkaliyar kotun ya yanke wa ’yan damfara hukuncin zaman gidan yari na tsawon shekaru hudu a kowane makon da ya gabata.

An tuhumi mutanen biyu da laifin hada baki, damfara, cin amana, da kuma zamba.

Lokacin da aka karanta Rahoton Bayanin Farko, dukkansu sun amsa laifukan guda hudu. Lauyan masu gabatar da kara Barista Zahraddeen Hamisu Kofarmata ya bukaci a yi masa shari’a a karkashin sashe na 129 (8) na shari’ar ACJL 2019. Daga nan kuma aka yanke musu laifin.

Alkaliyar Kotun Majistare Umma Sani Kurawa ta yanke wa wadanda ake tuhumar hukuncin daurin watanni shida a gidan yari saboda samun su da laifin hada baki (ko tarar Naira 30,000 kowannensu), watanni uku kan aikata laifuka (ko tarar Naira 20,000 kowanne), shekara daya saboda zamba (ko kuma tarar Naira 20,000 kowanne), tarar Naira 30,000 kowanne), da watanni shida kan laifin karya cin amana (ko tarar Naira 20,000 kowanne).

An kuma umarce su da su biya diyyar Naira miliyan 5 ko kuma su fuskanci daurin shekaru biyu a gidan yari bisa bukatar lauyan masu gabatar da kara.

Bugu da kari, masu laifin biyu sun yi amfani da irin wannan dabara wajen damfarar tsohon karamin ministan gidaje Alhaji A.T. Gwarzo na Naira miliyan daya.

Hukumar ta lura da cewa, duk da cewa babu wani korafi da tsohuwar ministar ya yi, an gano shirin nasu ne a yayin gudanar da bincike.

Hukumar ta kwato kudaden da aka damfara kuma za a mayar wa Aminu Dantata da Alhaji A.T. Gwarzo.

Dukkanin wadanda aka yankewa hukuncin kuma an bukaci su sanya hannu kan takardar yarjejeniya don su zamto masu kyawawan halaye.

Babban mai laifin da ke zaune a Kano, sai ya aika da Naira 500,000 ga wanda ya taimaka masa a Abuja, yayin da ya ajiye wa kansa Naira miliyan 4.5.

An kuma umarce su da su biya diyyar Naira miliyan 5 ko kuma su fuskanci daurin shekaru biyu a gidan yari bisa bukatar lauyan masu gabatar da kara.

Bugu da kari, masu laifin biyu sun yi amfani da irin wannan dabara wajen damfarar tsohon karamin ministan gidaje Alhaji A.T. Gwarzo na Naira miliyan daya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa
Kotu Da Ɗansanda

An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa

November 8, 2025
An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi
Kotu Da Ɗansanda

An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

November 8, 2025
Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi
Kotu Da Ɗansanda

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

October 4, 2025
Next Post
Shugaba Xi Ya Gana Da Kantoman Yankin Musamman Na Macao Na Kasar Sin

Shugaba Xi Ya Gana Da Kantoman Yankin Musamman Na Macao Na Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Shugabannin Sin Da Comoros Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafa Alakar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu 

Shugabannin Sin Da Comoros Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafa Alakar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu 

November 13, 2025
Sanarwar Taron Ministocin Harkokin Waje Na Kungiyar G7 Ba Ta Da Tushe

Sanarwar Taron Ministocin Harkokin Waje Na Kungiyar G7 Ba Ta Da Tushe

November 13, 2025
NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna

NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna

November 13, 2025
An Kafa Cibiyar Kiwon Lafiya Ta Hadin Gwiwa Ta Farko Tsakanin Sin Da Afirka A Guinea

An Kafa Cibiyar Kiwon Lafiya Ta Hadin Gwiwa Ta Farko Tsakanin Sin Da Afirka A Guinea

November 13, 2025
Jiga Jigan APC Sun Ziyarci Majalisar Wakilai Bayan Sauya Sheƙar Ƴan NNPP 2

Jiga Jigan APC Sun Ziyarci Majalisar Wakilai Bayan Sauya Sheƙar Ƴan NNPP 2

November 13, 2025
NIQS Ta Buƙaci Gwamnati Ta Tsawatar Kan Tsadar Gidajen Haya A Manyan Birane

NIQS Ta Buƙaci Gwamnati Ta Tsawatar Kan Tsadar Gidajen Haya A Manyan Birane

November 13, 2025
Dalilai 5 Da Suka Jefa Ƙungiyar Ƙwallon Ƙafa Ta Kano Pillars Cikin Matsaloli A Kakar Wasa Ta 2024/25

Dalilai 5 Da Suka Jefa Ƙungiyar Ƙwallon Ƙafa Ta Kano Pillars Cikin Matsaloli A Kakar Wasa Ta 2024/25

November 13, 2025
Sau Ɗaya Na Taɓa Da-nasanin Fitowa A Cikin Fim – Tanimu Akawu

Sau Ɗaya Na Taɓa Da-nasanin Fitowa A Cikin Fim – Tanimu Akawu

November 13, 2025
Nijeriya Za Ta Buga Gasar Kofin Duniya Na Shekarar 2026 – Gusau

Nijeriya Za Ta Buga Gasar Kofin Duniya Na Shekarar 2026 – Gusau

November 13, 2025
‘Yan Wasan Ƙwallon Ƙafa 10 Da Za Su Iya Buga Gasar Cin Kofin Duniya Ta Ƙarshe A 2026

‘Yan Wasan Ƙwallon Ƙafa 10 Da Za Su Iya Buga Gasar Cin Kofin Duniya Ta Ƙarshe A 2026

November 13, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.