• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

EFCC Ta Cafke Wadanda Suka Damfari Attajiri Aminu Dantata

by Rabi'u Ali Indabawa
6 months ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
Zambar Kudi: Kotu Ta Tasa Keyar Dillalin Gidaje Zuwa Gidan Kaso
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar korafe-korafen al’umma da yaki da cin hanci da rashawa ta Jihar Kano ta sanar da samun nasarar kama wasu mutum biyu da suka damfari wani dattijo Alhaji Aminu Dantata da tsohon minista Alhaji A.T. Gwarzo.

Bugu da kari, hukumar ta kwato Naira miliyan 5, daga hannun wadanda aka kama din sun damfari daga hannun hamshakin dan kasuwar, ciki har da Naira miliyan daya mallakin tsohon ministar bayan gurfanar da su gaban kotu.

  • EFCC Za Ta Binciki Yadda Kudaden Kananan Hukumomi Ke Sulalewa
  • Shugabannin Sin Da UAE Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 40 Da Kafuwar Huldar Diflomasiyya Tsakaninsu

Da yake zantawa da manema labarai jim kadan bayan kammala zaman kotun, lauyan masu shigar da kara Zahraddeen Hamisu Kofarmata ya bayyana cewa Bukar Galadima da Sulyman Ahmed sun shirya tare da aiwatar da wani shiri na damfarar wadanda abin ya shafa.

Bukar Galadima ya yi sojan gona da sunan Tsohon Ministan Babban Birnin Tarayya, Mohammed Abba Gana, inda nuna tsohon ministan ba shi da lafiya, ya kuma nemi taimakon Aminu Dantata, inda ya bukaci Naira miliyan 5 domin a yi masa magani, daga nan sai Dantata ya umarce shi da ya ba shi bayanan asusun ajiyarsa. A maimakon ya bayar da nasa, Galadima ya bayar da bayanan matarsa, Sadiyya Abba.

Daga nan ne dan kasuwar ya mika Naira miliyan 5 zuwa asusun ajiyar kudi domin tallafa wa wanda ke jinya.

Labarai Masu Nasaba

NDLEA Ta Kama Wani Mutum Mai Shekaru 75 Da Laifin Safarar Muggan Kwayoyi

‘Yansanda Sun Kama Mutum 245 Da Miyagun Kwayoyi Da Makamai A Abuja

Babban mai laifin da ke zaune a Kano, sai ya aika da Naira 500,000 ga wanda ya taimaka masa a Abuja, yayin da ya ajiye wa kansa Naira miliyan 4.5.

Daga baya, da Dantata ya tuntubi tsohon ministan don duba lafiyarsa, sai ya gane cewa an zambace shi, ya kai karar hukumar korafe-korafen jama’a da yaki da cin hanci da rashawa ta Jihar Kano, inda ta fara bincike.

An kama mutanen biyu ne kuma aka gurfanar da su a gaban Kotun Majistare mai lamba 24 da ke Kano.

Alkaliyar kotun ya yanke wa ’yan damfara hukuncin zaman gidan yari na tsawon shekaru hudu a kowane makon da ya gabata.

An tuhumi mutanen biyu da laifin hada baki, damfara, cin amana, da kuma zamba.

Lokacin da aka karanta Rahoton Bayanin Farko, dukkansu sun amsa laifukan guda hudu. Lauyan masu gabatar da kara Barista Zahraddeen Hamisu Kofarmata ya bukaci a yi masa shari’a a karkashin sashe na 129 (8) na shari’ar ACJL 2019. Daga nan kuma aka yanke musu laifin.

Alkaliyar Kotun Majistare Umma Sani Kurawa ta yanke wa wadanda ake tuhumar hukuncin daurin watanni shida a gidan yari saboda samun su da laifin hada baki (ko tarar Naira 30,000 kowannensu), watanni uku kan aikata laifuka (ko tarar Naira 20,000 kowanne), shekara daya saboda zamba (ko kuma tarar Naira 20,000 kowanne), tarar Naira 30,000 kowanne), da watanni shida kan laifin karya cin amana (ko tarar Naira 20,000 kowanne).

An kuma umarce su da su biya diyyar Naira miliyan 5 ko kuma su fuskanci daurin shekaru biyu a gidan yari bisa bukatar lauyan masu gabatar da kara.

Bugu da kari, masu laifin biyu sun yi amfani da irin wannan dabara wajen damfarar tsohon karamin ministan gidaje Alhaji A.T. Gwarzo na Naira miliyan daya.

Hukumar ta lura da cewa, duk da cewa babu wani korafi da tsohuwar ministar ya yi, an gano shirin nasu ne a yayin gudanar da bincike.

Hukumar ta kwato kudaden da aka damfara kuma za a mayar wa Aminu Dantata da Alhaji A.T. Gwarzo.

Dukkanin wadanda aka yankewa hukuncin kuma an bukaci su sanya hannu kan takardar yarjejeniya don su zamto masu kyawawan halaye.

Babban mai laifin da ke zaune a Kano, sai ya aika da Naira 500,000 ga wanda ya taimaka masa a Abuja, yayin da ya ajiye wa kansa Naira miliyan 4.5.

An kuma umarce su da su biya diyyar Naira miliyan 5 ko kuma su fuskanci daurin shekaru biyu a gidan yari bisa bukatar lauyan masu gabatar da kara.

Bugu da kari, masu laifin biyu sun yi amfani da irin wannan dabara wajen damfarar tsohon karamin ministan gidaje Alhaji A.T. Gwarzo na Naira miliyan daya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Aminu DantataDamfaraEFCC
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Dalilin Da Ya Sa ‘Yansanda Suka Kasa Kama Tsohon Gwamnan Kogi’

Next Post

Shugaba Xi Ya Gana Da Kantoman Yankin Musamman Na Macao Na Kasar Sin

Related

Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance
Kotu Da Ɗansanda

NDLEA Ta Kama Wani Mutum Mai Shekaru 75 Da Laifin Safarar Muggan Kwayoyi

1 month ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum 245 Da Miyagun Kwayoyi Da Makamai A Abuja

2 months ago
‘Yansanda A Legas Sun Kama Mutum 35 Da Ake Zargi Da Fashi Cikin Mako Guda
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda A Legas Sun Kama Mutum 35 Da Ake Zargi Da Fashi Cikin Mako Guda

2 months ago
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Na Farautar Wadanda Suka Kashe Dalibi A Katsina

2 months ago
Rikita-rikitar Da Ta Biyo Bayan Mutuwar Mawaki Mohbad
Kotu Da Ɗansanda

MohBad: Nurse Za Ta Fuskanci Shari’a, Sannan Kotu Ta Wanke Naira Marley, Sam Larry Da PrimeBoy

2 months ago
‘Yansanda Sun Kubutar Da Wata Mata Da Aka Yi Garkuwa Da Ita A Otal Din Abuja
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kubutar Da Wata Mata Da Aka Yi Garkuwa Da Ita A Otal Din Abuja

3 months ago
Next Post
Shugaba Xi Ya Gana Da Kantoman Yankin Musamman Na Macao Na Kasar Sin

Shugaba Xi Ya Gana Da Kantoman Yankin Musamman Na Macao Na Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

May 14, 2025
Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

May 14, 2025
Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

May 14, 2025
‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

May 14, 2025
Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

May 14, 2025
Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

May 14, 2025
Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

May 14, 2025
Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

May 13, 2025
Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

May 13, 2025
Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

May 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.