• English
  • Business News
Saturday, May 31, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [16]

by Nuhu Ubale Ibrahim
2 months ago
in Addini, Bakon Marubuci, Ilimi
0
Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai

Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rabe-raben Hassada:

Ibnu Juzai a-Kalbi Allah Ya ji ƙan sa yana cewa:

إِنَّ الحَسَدَ عَلَى دَرَجَاتٍ: الأُولَى أَنْ يُحِبَّ الإِنْسَانُ زَوَالَ النِّعْمَةِ عَنْ أَخِيهِ المُسْلِمِ وَإِنْ كَانَتْ لَا تَنْتَقِلُ إِلَيْهِ، بَلْ يَكْرَهُ إِنْعَامَ اللَّهِ عَلَى غَيْرِهِ وَيَتَأَلَّمُ بِهِ. الثَّانِيَةُ أَنْ يُحِبَّ زَوَالَ تِلْكَ النِّعْمَةِ لِرَغْبَتِهِ فِيهَا، رَجَاءَ انْتِقَالِهَا إِلَيْهِ. الثَّالِثَةُ أَنْ يَتَمَنَّى لِنَفْسِهِ مِثْلَ تِلْكَ النِّعْمَةِ مِنْ غَيْرِ أَنْ يُحِبَّ زَوَالَهَا عَنْ غَيْرِهِ، وَهَذَا جَائِزٌ وَلَيْسَ بِحَسَدٍ، وَإِنَّمَا هُوَ غِبْطَةٌ.

Fassara:
“ Tabbas hassada tana da matakai: Matakin farko shi ne mutum ya so ni’imar da ke hannun ɗan’uwansa musulmi ta gushe, ko da kuwa ba zai amfana da ita ba. Sai kawai ya kyamaci ganin wani a cikin ni’imar Allah, ya ji zafin samun wannan ni’ima a hannun wani.

  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [15]
  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [14]

Mataki na biyu shi ne mutum ya so wannan ni’ima ta gushe daga hannun wani saboda yana son ta koma gare shi, saboda kwaɗayinta da fatan amfana da ita.

Labarai Masu Nasaba

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (3)

Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (2)

Mataki na uku shi ne mutum ya so samun irin wannan ni’ima kamar yadda wani yake da ita, ba tare da yana so ta gushe daga hannun wanda yake da ita ba. Wannan kuwa ba hassada ba ce, sai dai ana kiranta da fatan alheri ga kai.” Duba Kitãbu at-Tashīlu Li’ulūmi at-Tanzil [4/226]

Fashin Baƙi:
Ibn Juzai al-Kalbi ya bayyana mana rabe-raben hassada. Inda ya ce:
● Matakin Farko na Hassada:
Shi ne mutum ya so wata ni’ima da Allah Ya ba wa wani ta gushe daga gare shi, ko da kuwa ba zai amfana da ita ba. Wannan shi ne mafi munin nau’in hassada gaba ɗaya, kuma yana ɗaya daga cikin manyan cututtukan zuciya da ke hana albarka a rayuwa.

Wannan nau’in hassada yana nufin mutum yana jin haushin samun wata ni’ima a hannun wani, ba don yana son ita ta koma gare shi ba, sai dai kawai ya ƙi ganin wani yana da ita. Wannan yana iya kasancewa a cikin kowace irin ni’ima, kamar:
• Dukiya da arziki
• Matsayi ko shugabanci
• Ilimi da hikima
• Kyakkyawar rayuwa
Farin ciki da kwanciyar hankali da sauran su.
A wasu lokuta, mai irin wannan hassadar ba shi da watbuƙata a kan ni’imar da yake hassada, amma kawai yana jin cewa wannan mutumin bai cancanci wannan alheri ba. Wannan yana nuna kyashi da mugunta a zuciyar mai hassadar.

Alamomin Wannan Hassada:
Jin haushin duk wani alheri da wani ya samu.
Ƙin fatan wani ya cigaba ko ya sami wadata ko farin ciki. Idan ya ga wani yana cikin alheri, yana jin haushin hakan. Idan wannan ni’ima ta gushe daga hannun mai ita, sai ya ji daɗi. Baya iya ɓoye jin haushinsa idan wani ya sami nasara ko farin ciki.
Misalan Irin Wannan Hassada:

1. Hassadar Iblis ga Annabi Adam (AS): Labarin farko da ya nuna irin wannan hassadar shi ne na Iblis da Annabi Adam (AS). Allah Ya ba Adam matsayi na musamman, amma Iblis ya ƙi yarda, yana jin haushin Allah Ya ba wa Adam daraja. Bai so ya zama kamar annabi Adam (AS), sai dai kawai ya ƙi ganin annabi Adam yana da wannan matsayi har yana cewa:” Yanzu na yi sujjada ga wanda Ka halitta da taɓo?” Suratul Isrã’i aya ta 61. Iblis bai buƙaci wannan matsayi ya koma gare shi ba, amma bai son annabi Adam (AS) ya ci gaba da kasancewa a ciki ba. Wannan ita ce hassada mafi muni.

2. Hassadar Yahudawa ga Musulumi:
A cikin suratul-Baƙara, Allah Ya bayyana cewa Yahudawa sun yi hassada ga Musulumi saboda Allah Ya ba su addinin da ya fi na su. Sun san gaskiya, amma sai suka ƙi amincewa da ita saboda hassada. Allah Ta’ala Ya ce:” Da yawa daga ma’abota littafi sun yi burin jna ma a ce su mayar da ku kafirai bayan imaninku, saboda hassada daga zukatansu, bayan kuma gaskiya ta bayyana a gare su.” Suratul-Baƙara aya ta 109.

Ba don Yahudawa suna son addinin Musulunci ya kasance nasu ba, sai dai kawai suna jin haushin Musulumai sun samu wannan ni’ima.

3. Hassadar ‘Yan’uwan Annabi Yusuf (AS):
‘Yan’uwan Annabi Yusuf sun yi hassada a kansa ba don suna son su zama Annabawa ba, sai dai kawai sun ƙi ganin mahaifinsu yana ƙaunarsa fiye da su. Saboda haka, suka nemi hanyar raba shi da wannan ni’ima. Allah Yana cewa:” Ka tuna lokacin da ‘yan’uwan suka ce:” Lalle Yusufu da ɗan’uwansa babammu ya fi son su da mu, ga mu kuwa jama’a masu yawa. Lalle babammu yana cikin kuskure mabayyani.” Suratu Yusuf aya ta 8.

Suna ƙyamar ganin annabi Yusuf yana cikin soyayyar mahaifinsu, har suka yi ƙoƙarin halaka shi. Wannan yana nuna yadda hassada take kai mutum ga zalunci da cutar da wasu.

4. Illolin Wannan Hassara:
Rashin Yarda da Ƙaddarar Allah: Wannan nau’in hassada yana nuna cewa mutum bai yarda da yadda Allah Yake rabon ni’ima ba. Mai irin wannan hali yana ƙin hikimar Allah da yadda Ya tsara rayuwa.

Rashin Farin Ciki da Kwanciyar Hankali: Mutum mai irin wannan hassada yana cikin damuwa a koyaushe. Yana ƙunci idan ya ga wani cikin alheri, yana fushi idan wani ya sami nasara, kuma yana jin baƙin ciki idan wani yana da wadata.

Yana Haifar da Gaba da Ƙiyayya a Tsakanin Mutane: Hassada tana haddasa gaba da ƙiyayya a tsakanin mutane. Mai irin wannan hali baya son ci gaban wasu, wanda hakan ke haifar da matsaloli a cikin al’umma.
Rashin Albarka a Rayuwa: Mutumin da yake da irin wannan hassadar ba ya samun albarka a rayuwarsa, domin Allah ba Ya albarkantar da zuciya mai kyashi da mugunta.

Allah Ya yi mana katangar ƙarfe da hasaada. Amin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Abu Razina Nuhu Ubale PakiAl-qur'aniAlƙur’aniIbnu JuzaiRamadanTafsiriTafsirin Alƙur’aniTafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai
ShareTweetSendShare
Previous Post

Masanin Amurka: Matakan Kariyar Cinikayya Da Amurka Ke Aiwatarwa Babban Kuskure Ne

Next Post

Ƴansandan Sun Gayyaci Sanata Karimi Kan Zargin Shigar Kungiyar Leƙen Asirin Rasha Majalisa’

Related

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (3)
Ilimi

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (3)

25 minutes ago
Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (2)
Addini

Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (2)

1 day ago
Ɗalibai Sun Rubuta Jarrabawar WAEC Cikin Dare A Duhu
Ilimi

Ɗalibai Sun Rubuta Jarrabawar WAEC Cikin Dare A Duhu

2 days ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (2)
Ilimi

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (2)

1 week ago
Kungiyar Tsofaffin Ɗaliban BUK Ta Karrama Dr. Sani Dauda Ibrahim Da Walimar Kammala Digiri Na 3
Ilimi

Kungiyar Tsofaffin Ɗaliban BUK Ta Karrama Dr. Sani Dauda Ibrahim Da Walimar Kammala Digiri Na 3

1 week ago
SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (2)
Bakon Marubuci

SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (2)

1 week ago
Next Post
Ƴansandan Sun Gayyaci Sanata Karimi Kan Zargin Shigar Kungiyar Leƙen Asirin Rasha Majalisa’

Ƴansandan Sun Gayyaci Sanata Karimi Kan Zargin Shigar Kungiyar Leƙen Asirin Rasha Majalisa'

LABARAI MASU NASABA

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (3)

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (3)

May 31, 2025
Ahmed Musa Ya Angwance Da Matarsa Ta 4 A Kano

Ahmed Musa Ya Angwance Da Matarsa Ta 4 A Kano

May 31, 2025
Tsohuwar Firaministar New Zealand: Ya Dace A Koyi Dabarun Sin Na Raya Kasa

Tsohuwar Firaministar New Zealand: Ya Dace A Koyi Dabarun Sin Na Raya Kasa

May 31, 2025
Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

May 31, 2025
Shugaba Tinubu Ya Aika Tawaga Zuwa Jihar Neja Kan Ambaliya Ruwa

Shugaba Tinubu Ya Aika Tawaga Zuwa Jihar Neja Kan Ambaliya Ruwa

May 31, 2025
Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

May 31, 2025
Mutane 21 Sun Mutu A Tawagar Ƴan Wasannin Kano A Hatsarin Mota

Mutane 21 Sun Mutu A Tawagar Ƴan Wasannin Kano A Hatsarin Mota

May 31, 2025
‘Yan Sanda Sun Kama Mutum 2 Kan Zargin Jefe Wani Direba Har Lahira A Ondo

‘Yansanda Sun Gurfanar Da Lauya A Abuja A Kotu Bisa Tuhumarsa Da Aikata Sojan Gona

May 31, 2025
Adadin Mutanen Da Suka Mutu Sanadin Ambaliya A Neja Ya Karu Zuwa 115

Adadin Mutanen Da Suka Mutu Sanadin Ambaliya A Neja Ya Karu Zuwa 115

May 31, 2025
Unity Cup: Yau Nijeriya Za Ta Buga Wasan Ƙarshe Da Ƙasar Jamaica

Unity Cup: Yau Nijeriya Za Ta Buga Wasan Ƙarshe Da Ƙasar Jamaica

May 31, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.