• English
  • Business News
Monday, August 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [18]

by Nuhu Ubale Ibrahim
5 months ago
in Addini, Bakon Marubuci, Ilimi
0
Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai

Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ci gaba

Mataki na Uku na Hassada:

Shi ne mutum ya so samun ni’ima kamar yadda wani yake da ita, ba tare da yana so ta gushe daga hannun wanda yake da ita ba. Wannan kuwa ba hassada ba ce, sai dai ana kiranta da fatan alheri ga kai.

Wannan nau’i na hassada ana kiran sa da ‘ al-Gibɗatu’ wata kalma ce ta Larabci da ke nufin gasa ta gari ko fatan samun alheri kamar na wani, ba tare da fatan ni’imarsa ta gushe daga hannunsa ba. Wannan hali ne da ya sha bamban da mummunar hassada wanda ke da mummunan tasiri a cikin zuciya da al’umma. Irin wannan fatan alherin Allah Ya zaburar da bayinsa a cikin Suratul Muɗaffifin aya ta 26.

  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [17]
  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [16]

Rabe-raben Irin Wannan Hassada:

Labarai Masu Nasaba

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Yaushe Shugaban Kasa Zai Ba ‘Yan Matan Yobe Nasu Kyaututtukan

1. Gibɗa a cikin Addini:
Wannan ya ƙunshi yin gasa a ibada kamar sallah, ko azumi, ko karatun Alƙur’ani, da sadaka, ko mutum ya so ya zama hamshaƙin mai kuɗi da zai rinƙa taimaka wa addini da bayin Allah. Ko kuma mutum ya nemi ya zama malami ko jagora a addini don ya koyar da mutane.

2. Gibɗa a cikin Duniya:
Wannan shi ne mutum ya so samun ilimi irin na wasu don ya amfanar da kansa da al’umma. Ko kuma son ya zama attajiri ko ɗan kasuwa ko mai wata sana’a da zai rinƙa ba wa mutane horo saboda ya ga wani yana yi shi ma ya so ya ƙware ya taimaka domin samun lada a wurin Allah. Haka nan son samun shugabanci mai kyau domin jagorantar al’umma bisa gaskiya.

Manzon Allah (SAW) ya nuna irin wannanhassadarba laifi ba ce, inda ya ce: “Babu hassada sai a cikin abubuwa biyu: mutumin da Allah Ya ba shi ilimi, sai ya yi aiki da shi yana koyar da mutane, da kuma mutumin da Allah Ya ba shi dukiya, sai ya kashe ta a cikin hanyar da ta dace.” Bukhari da Muslim ne suka ruwaito.

Bambanci Tsakanin Hassada da Gibɗa:

Idan mutum ya ga wani yana da ilimi, sannan ya so ya zama kamar shi ba tare da yana son ilimin wancan ya gushe ba, to wannan ita ce gibɗa. Idan kuma mutum yana jin haushin wani saboda Allah Ya ba shi wata ni’ima, yana kuma son ni’imar ta gushe daga gare shi, to wannan ita ce hassada wacce aka haramta.

Illon Mutum Ya Zama Maras Gibɗa:
Idan mutum bai da hali na gibɗa, to hakan zai haifar masa da:

• Rashin ƙwazo da son ci gaba a rayuwa.
• Rashin yin koyi da na-gari a al’umma.
• Watsi da neman ilimi da kwarewa a sana’a ko addini.
• Rashin gasa a ayyukan ibada, wanda zai iya sa mutum ya ja baya a addini.

Yadda Mutum Zai Zama Mai Gibɗa:

Idan mutjm yana son ya sami ta gari, to dole ne ya zamanto ya:

• Nemi arzƙi ta hanyar halal da nagartaccen ilimi mai amfani.
• Aiki tuƙuru don samun ci gaba, ba tare da cutar da wani ba.
• Yin addu’a don Allah Ya ba shi irin ni’ima da wasu ke da ita.
• Kauracewa hassada da kiyayya a zuciya.
Kallon wasu a matsayin abin koyi, ba makiya ba.

Allah Ya datar da mu. Amin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Abu Razina Nuhu Ubale PakiAl-qur'aniAlƙur’aniIbnu JuzaiRamadanTafsiriTafsirin Alƙur’aniTafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Na Ci Gaba Da Kasancewa Cibiyar Rarraba Hajojin Da Masana’antu Ke Sarrafawa

Next Post

Rasha Da Ukraine Sun Amince Da Tsagaita Wuta A Tekun Black Sea

Related

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu
Ilimi

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

2 days ago
Yaushe Shugaban Kasa Zai Ba ‘Yan Matan Yobe Nasu Kyaututtukan
Bakon Marubuci

Yaushe Shugaban Kasa Zai Ba ‘Yan Matan Yobe Nasu Kyaututtukan

3 days ago
Hoton Kwankwaso da Ganduje da Shekarau
Bakon Marubuci

Daga Sawaba Zuwa Asara: Baje Kolin Kasuwancin Siyasa A Kano – Auwalu Anwar

5 days ago
Kungiyoyi Masu Fada Aji Kan Harkar Ilimi Sun Nemi A Yi Wa Sashen Kwaskwarima
Ilimi

Kungiyoyi Masu Fada Aji Kan Harkar Ilimi Sun Nemi A Yi Wa Sashen Kwaskwarima

1 week ago
Manufofin Hulda Da Kasashen Wajen Da Nijeriya Ke Bukata
Bakon Marubuci

Manufofin Hulda Da Kasashen Wajen Da Nijeriya Ke Bukata

1 week ago
Gwamnatin Yobe Za Ta Yi Taron Girmama Ɗalibar Turanci Ta Duniya, Nafisa Abdullah
Ilimi

Gwamnatin Yobe Za Ta Yi Taron Girmama Ɗalibar Turanci Ta Duniya, Nafisa Abdullah

3 weeks ago
Next Post
Rasha Da Ukraine Sun Amince Da Tsagaita Wuta A Tekun Black Sea

Rasha Da Ukraine Sun Amince Da Tsagaita Wuta A Tekun Black Sea

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mutane 69 Masu Fasa Bututun Mai A Yankin Neja-Delta

Sojoji Sun Kama Mutane 69 Masu Fasa Bututun Mai A Yankin Neja-Delta

August 25, 2025
Ƙungiyar KSCI Ta Nemi Sabon Tsari Don Magance Ƴan Bindiga A Katsina

Ƙungiyar KSCI Ta Nemi Sabon Tsari Don Magance Ƴan Bindiga A Katsina

August 25, 2025
Ƙungiyoyin Farar Hula Sun Nemi A Dakatar Da Jami’an Gwamnatin Kano

Ƙungiyoyin Farar Hula Sun Nemi A Dakatar Da Jami’an Gwamnatin Kano

August 25, 2025
Tinubu Ya Isa Brazil, Zai Nemi Masu Zuba Jarin Biliyoyi A Noma, Makamashi Da Fasaha

Tinubu Ya Isa Brazil, Zai Nemi Masu Zuba Jarin Biliyoyi A Noma, Makamashi Da Fasaha

August 25, 2025

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

August 24, 2025
Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

August 24, 2025
Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

August 24, 2025
An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

August 24, 2025
CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

August 24, 2025
Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

August 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.