• English
  • Business News
Sunday, October 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Farashin Tumatir Ya Karye Bayan Ghana Da Kamaru Sun Turo Shi Kasuwannin Nijeriya

by Abubakar Abba
2 years ago
Tumatir

Biyo bayan turo Tumatir da kasashen Ghana da Kamaru suka yi zuwa wsu manyan kasuwannin Nijeriya, hakan ya janyo farashin na Tumatir ya karye.

Binciken da aka gudanar ya nuna cewa, a kwanukan baya a Nijeriya biyo bayan bullar cutar da ke harbin Tumatir da aka shuka a gonakai wadda ake kira a turance, Tuta Absoluta ta haifar da karancin Tumatir a wasu sassan kasar nan tare da kuma hauhawan farashin na Tumatir a kasar.

  • Gwamnan Bauchi Ya Zama Shugaban Kungiyar Gwamnonin PDP

Wannan ne ya sa manyan masu hada-hadar kasuwancin na Tumatir da ke a kasar nan a suka yanke shawarar shigo da Tumatir daga kasashen na Ghana da kuma Kamaru.

Har ila yau, binciken da aka gudanar ya nuna cewa, farashin Kwandon Tumatir daya, a jihar Kano wanda a baya ake sayarwa Naira 50,000 a wasu sassan kasar nan, a yanzu, ana sayar da Kwandon daya kan Naira 18,000 zuwa Naira 20,000,musamman saboda an samar da wadataccen sa.

A cewar shugaban kungiyar manoman Tumatir na kasa reshen jihar Kano (TOGAN), Alhaji Sani Danladi Yadakwari, karancin na Tumatir da aka fuskanta a baya, ya faru ne saboda harbin da cutar ta Tuta Absoluta ta yiwa Tumatir da aka shuka a gonakai da ke a cikin jihar ta Kano.

LABARAI MASU NASABA

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya

Gwamnatin Jihar Taraba Ta Ayyana Yi Wa Kasuwannin Sayar Da Dabbobi 9 Garanbawul

Yadakwari ya bayar da tabbacin cewa, amma biyo bayan turo Tumatir da aka yi daga jihar Ogun da kuma sauran wasu kasashen da ke a nahiyar Afirka kamar su, Ghana da Kamaru, hakan ya janyo farashin na Tumatir ya karye.
“A yanzu dai, karancin na Tumatir da aka fuskanta a baya, ya faru ne saboda harbin da cutar ta Tuta Absoluta ta yiwa Tumatir da aka shuka a gonakai. ”

A cewarsa, “Amma biyo bayan turo Tumatir da aka yi daga jihar Ogun da kuma sauran wasu kasashen da ke a nahiyar Afirka kamar su, Ghana da Kamaru, hakan ya janyo farashin na Tumatir ya karye.”
Shugaban ya bayyana cewa, biyo bayan shigo da Tumatir da manyan masu hada-hadar kasuwancin sa a kasar nan daga kasashen Ghana da kuma Kamaru, bakan ya sa an samu nasarar karya farashin na Tumatir a kasuwannin kasar nan.

In ba a manta ba, a makwannin baya ta na sayen Kwandon Tumatir a wasu sannan kasar nan ya kai Naira 17,000 zuwa Naira 18,000, inda farashin ya tashi zuwa Naira 48,000.

Har ila yau, a garin Fatakwal an sayar da Kwadon Tumari kan Naira 65,000 zuwa Naira70,000, inda a Enugu, ake sayar da Kwandonsa daga Naira 63,000 zuwa Naira 68,000, wannan ya danganta da irin kasuwar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya
Noma Da Kiwo

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya

October 18, 2025
‘Yansanda Sun Cafke Ɓarayi 13 Tare Da Ƙwato Shanu 27 A Kaduna
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Jihar Taraba Ta Ayyana Yi Wa Kasuwannin Sayar Da Dabbobi 9 Garanbawul

October 18, 2025
Dalilin Bankin AfDB Na Yin Hadaka Da WFP Da IFPRI
Noma Da Kiwo

Dalilin Bankin AfDB Na Yin Hadaka Da WFP Da IFPRI

October 18, 2025
Next Post
Dalilin Da Manoman Rama A Jihar Katsina Ke Kara Habaka

Dalilin Da Manoman Rama A Jihar Katsina Ke Kara Habaka

LABARAI MASU NASABA

JTF Ta Kama Wani Da Ake Zargin Mai Safarar Miyagun Ƙwayoyi Ne Ga ‘Yan Bindiga A Jihar Kogi

JTF Ta Kama Wani Da Ake Zargin Mai Safarar Miyagun Ƙwayoyi Ne Ga ‘Yan Bindiga A Jihar Kogi

October 19, 2025
Abin Da Nijeriya Ke Bukata Kafin Samun Damar Zuwa Gasar Kofin Duniya

Abin Da Nijeriya Ke Bukata Kafin Samun Damar Zuwa Gasar Kofin Duniya

October 19, 2025
Yadda Ake Alkaki

Yadda Ake Alkaki

October 19, 2025
Kar Ki Yi Kuskuren Da Za Ki Yi Da Na Sani A Kai (1)

Kar Ki Yi Kuskuren Da Za Ki Yi Da Na Sani A Kai (2)

October 19, 2025
An Sanya Hannu Kan Yarjejiyar Zaman Lafiya A Gaza

An Sanya Hannu Kan Yarjejiyar Zaman Lafiya A Gaza

October 19, 2025
Nijar

Gwamnatin Nijar Ta Yaye Tsofaffin Mayaka 369 Da Aka Bai Wa Horon Sauya Tunani

October 19, 2025
Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus

‘Yan Siyasa 11 Da Suka Faɗa Dambarwar Takardar Shaidar Karatu Ta Bogi

October 19, 2025
gombe

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

October 18, 2025
Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

October 18, 2025
An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

October 18, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.