• Leadership Hausa
Monday, October 2, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Farashin Tumatir Ya Karye Bayan Ghana Da Kamaru Sun Turo Shi Kasuwannin Nijeriya

by Abubakar Abba
4 months ago
in Noma Da Kiwo
0
Farashin Tumatir Ya Karye Bayan Ghana Da Kamaru Sun Turo Shi Kasuwannin Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Biyo bayan turo Tumatir da kasashen Ghana da Kamaru suka yi zuwa wsu manyan kasuwannin Nijeriya, hakan ya janyo farashin na Tumatir ya karye.

Binciken da aka gudanar ya nuna cewa, a kwanukan baya a Nijeriya biyo bayan bullar cutar da ke harbin Tumatir da aka shuka a gonakai wadda ake kira a turance, Tuta Absoluta ta haifar da karancin Tumatir a wasu sassan kasar nan tare da kuma hauhawan farashin na Tumatir a kasar.

  • Gwamnan Bauchi Ya Zama Shugaban Kungiyar Gwamnonin PDP

Wannan ne ya sa manyan masu hada-hadar kasuwancin na Tumatir da ke a kasar nan a suka yanke shawarar shigo da Tumatir daga kasashen na Ghana da kuma Kamaru.

Har ila yau, binciken da aka gudanar ya nuna cewa, farashin Kwandon Tumatir daya, a jihar Kano wanda a baya ake sayarwa Naira 50,000 a wasu sassan kasar nan, a yanzu, ana sayar da Kwandon daya kan Naira 18,000 zuwa Naira 20,000,musamman saboda an samar da wadataccen sa.

A cewar shugaban kungiyar manoman Tumatir na kasa reshen jihar Kano (TOGAN), Alhaji Sani Danladi Yadakwari, karancin na Tumatir da aka fuskanta a baya, ya faru ne saboda harbin da cutar ta Tuta Absoluta ta yiwa Tumatir da aka shuka a gonakai da ke a cikin jihar ta Kano.

Labarai Masu Nasaba

Cibiyar Binciken Harkar Noma (IAR) Ta Samar Da Irin Masara Mai Inganci

Kungiyoyin CONESAM Sun Baje Kolin Fasahar Sarrafa Kayan Amfanin Gona

Yadakwari ya bayar da tabbacin cewa, amma biyo bayan turo Tumatir da aka yi daga jihar Ogun da kuma sauran wasu kasashen da ke a nahiyar Afirka kamar su, Ghana da Kamaru, hakan ya janyo farashin na Tumatir ya karye.
“A yanzu dai, karancin na Tumatir da aka fuskanta a baya, ya faru ne saboda harbin da cutar ta Tuta Absoluta ta yiwa Tumatir da aka shuka a gonakai. ”

A cewarsa, “Amma biyo bayan turo Tumatir da aka yi daga jihar Ogun da kuma sauran wasu kasashen da ke a nahiyar Afirka kamar su, Ghana da Kamaru, hakan ya janyo farashin na Tumatir ya karye.”
Shugaban ya bayyana cewa, biyo bayan shigo da Tumatir da manyan masu hada-hadar kasuwancin sa a kasar nan daga kasashen Ghana da kuma Kamaru, bakan ya sa an samu nasarar karya farashin na Tumatir a kasuwannin kasar nan.

In ba a manta ba, a makwannin baya ta na sayen Kwandon Tumatir a wasu sannan kasar nan ya kai Naira 17,000 zuwa Naira 18,000, inda farashin ya tashi zuwa Naira 48,000.

Har ila yau, a garin Fatakwal an sayar da Kwadon Tumari kan Naira 65,000 zuwa Naira70,000, inda a Enugu, ake sayar da Kwandonsa daga Naira 63,000 zuwa Naira 68,000, wannan ya danganta da irin kasuwar.

ShareTweetSendShare
Previous Post

Shanun Buhari Sun Ragu Saboda Yawan Kyautarsa — Garba Shehu

Next Post

Dalilin Da Manoman Rama A Jihar Katsina Ke Kara Habaka

Related

Wa’adin Da Tinubu Ya Bai Wa Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Ya Cika
Noma Da Kiwo

Cibiyar Binciken Harkar Noma (IAR) Ta Samar Da Irin Masara Mai Inganci

2 days ago
Kungiyoyin CONESAM Sun Baje Kolin Fasahar Sarrafa Kayan Amfanin Gona
Noma Da Kiwo

Kungiyoyin CONESAM Sun Baje Kolin Fasahar Sarrafa Kayan Amfanin Gona

2 days ago
Wa’adin Da Tinubu Ya Bai Wa Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Ya Cika
Noma Da Kiwo

Wa’adin Da Tinubu Ya Bai Wa Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Ya Cika

2 days ago
Shanu
Noma Da Kiwo

Bayan Tsawon Shekaru: Hada-Hadar Shanu Da Rakuma Ta Farfado A Jihar Yobe 

1 week ago
Dabarun Kasuwancin Man Darbejiya
Noma Da Kiwo

Dabarun Kasuwancin Man Darbejiya

2 weeks ago
Shanu
Noma Da Kiwo

Hanyoyi Hudu Na Samun Kudin Shiga A Kasuwancin Shanu

2 weeks ago
Next Post
Dalilin Da Manoman Rama A Jihar Katsina Ke Kara Habaka

Dalilin Da Manoman Rama A Jihar Katsina Ke Kara Habaka

LABARAI MASU NASABA

Mata

Ilimin ‘Ya’ya Mata: Kano Ta Fara Bai Wa ‘Yan Mata 45,000 Tallafin N20, 000

October 2, 2023
Kotu A Amurka Ta Umarci Jami’ar Chicago Ta Bai Wa Atiku Bayanan Karatun Tinubu

Kotu A Amurka Ta Umarci Jami’ar Chicago Ta Bai Wa Atiku Bayanan Karatun Tinubu

October 1, 2023
Tinubu

Ranar ‘Yanci: Tinubu Ya Kara Wa Kananan Ma’aikata N25,000 Kan Albashinsu

October 1, 2023
Hangzhou

Birnin Hangzhou Ya Samu Karuwar Masu Yawon Bude Ido Albarkacin Gasar Wasanni Ta Asiya Dake Gudana

October 1, 2023
Syria

Shugaban Syria: Manyan Tsare-tsare Uku Na duniya Su Ne Jagororin Sabuwar Duniya

October 1, 2023
BUA

Daga Gobe 2 Ga Oktoba Farashin Buhun Simintin BUA Ya Koma N3,500 – Kamfanin

October 1, 2023
Kasar Sin

Ofishin Jakadancin Kasar Sin Dake Najeriya Ya Shirya Bikin Murnar Cikar Sin Shekaru 74 Da Kafuwa

October 1, 2023
Yadda ‘Arewa Peace Ambassador Forum’ Ta Nada Sheikh Muhajjadina Jakadan Zaman Lafiya

Yadda ‘Arewa Peace Ambassador Forum’ Ta Nada Sheikh Muhajjadina Jakadan Zaman Lafiya

October 1, 2023
Amurka

Amurka Ita Ce “Daular Karya”Ta Ko Wace Fuska

October 1, 2023
Gwamnatin Tarayya Ta Yaba Da Ayyukan Bello Koko Na Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Amince Da Kafa Sashi Na Musamman A NPA Don Inganta Ayyukanta

October 1, 2023
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.