ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, November 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fashi Da Makami: An Yanke Wa ’Yan Nijeriya Hudu Mazauna Birtaniya Hukuncin Daurin Shekara 55 A Gidan Yari

by Rabi'u Ali Indabawa
1 hour ago
Fashi

An yanke wa ’yan Nijeriya hudu da ke cikin wata kungiyar fashi ta wayoyi da ta addabi birnin Landan hukuncin daurin shekaru 55 gaba daya, a kotun Kingston Crown Court da ke Birtaniya.

Jaridar PUNCH Metro ta samo wannan bayanin ne daga wata sanarwa da aka wallafa a shafin Intanet UK Metropolitan Police a ranar Litinin.

  • BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani
  • Sin Ta Yi Tsokaci Kan Kalaman Da Firaministar Japan Takaichi Sanae Ta Yi A Kanta

A cewar sanarwar, wadanda aka yanke wa hukuncin sun hada da Dabid Akintola, Ayomide Olaribiro, Olabiyi Obasa, da Dabid Okewole.

ADVERTISEMENT

Sauran da ke cikin kungiyar sun hada da James Adodo, Robert Hills, Nelson Joel, Michael Babo, Mushtakim Miah, da Labille Bloise.

Sanarwar ta bayyana cewa tsakanin Satumba da Nuwamba 2024, kungiyar ta gudanar da akalla fashi 13 a shagunan waya daban-daban a fadin Birtaniya.

LABARAI MASU NASABA

’Yansanda Sun Cafke Wani Da Ake Zargin Dan Ta’adda Ne A Jihar Kebbi

NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

Ta ce, “Kungiyar ta fi kai hare-hare a shagunan EE, inda suke amfani da barazana da tashin hankali wajen tilasta ma’aikata su bude dakunan ajiya na sirri kafin su gudu da wayoyi masu tsada da sauran na’urori.”

A jimlace, sun sace kayayyaki da darajarsu ta kai fam miliyan £240,000.

Jami’an tsaro sun gano masu laifin ta hanyar shaidar DNA, da kuma bayanan kira da rikodin motocin da suka yi amfani da su.

An ce sun ci gaba da bibiyar kungiyar yayin da take shirin sake kai wani hari, inda a ranar 19 ga Nuwamba, 2024, jami’ai suka yi musu kwanton bauna suka kama mutane hudu daga cikinsu a lokacin da suke kokarin yin fashi a wani shagon EE da ke Kilburn.

“Bincike a gidajen da ake danganta su da wadanda ake zargin ya kai ga gano kayan da aka sace da karin shaidu da ke hada kungiyar da fashi-fashin.”

Sanarwar ta bayyana cewa mutane 10 da aka kama a lokacin aikin an gurfanar da su a kotu, inda takwas suka amsa laifi na hadin gwiwa wajen fashi a ranar 30 ga Janairu.

Sanarwar ta kara da cewa bayan amsa laifin, an yanke musu hukuncin a ranar Jumma’a, 7 ga Nuwamba.

Ta bayyana tsawon lokacin da za su yi a gidan yari kamar haka:

James Adodo na St Martins Road, Dartford, Kent, an yanke masa hukuncin shekaru 10 a gidan yari.

Dabid Akintola na Samuel Street, Woolwich, an yanke masa hukuncin shekaru 6 da watanni 6 a gidan yari.

Michael Babo na Gilbert Close, Woolwich, an yanke masa hukuncin shekaru 6 da watanni 10 a gidan yari.

Robert Hills na Mayfield Road, Grabesend, Kent, an yanke masa hukuncin shekaru 5 da watanni 3 a gidan yari.

Ayomide Olaribiro na Warrior Skuare, Manor Park, an yanke masa hukuncin shekaru 4 da watanni 6 a gidan yari.

Nelson Joel na St Martins Road, Dartford, Kent, an yanke masa hukuncin shekaru 3 da watanni 3 a gidan yari.

Olabiyi Obasa na Norfolk Close, Dartford, Kent, an yanke masa hukuncin shekaru 3 da watanni 6 a gidan yari.

Dabid Okewole na Bale Road, Northfleet, Kent, an yanke masa hukuncin shekaru 7 da watanni 6 a gidan yari.

Sanarwar ta kuma nuna cewa wasu da aka yi kara biyu sun amsa laifin kokarin fashi, inda aka yanke musu hukuncin da ya dace.

Labille Bloise na Goldcrest Close, Thamesmead, an yanke masa hukuncin shekaru 2, wanda aka dage har tsawon shekaru 2.

Mushtakim Miah na Artillery Place, Woolwich, an yanke masa hukuncin shekaru 8 da watanni 6 a gidan yari.

Wannan shari’a ta zo ne a daidai lokacin da ake karuwa da rahotannin ’yan Nijeriya da ke kasashen waje da ake yanke musu hukuncin laifuka.

Jaridar PUNCH Metro ta ruwaito a ranar Laraba da ta gabata cewa wani dalibi dan Nijeriya mai digiri na biyu da ke zaune a Birtaniya, Chiemka Okoronta, zai yi kaura daga kasar bayan ya yi zaman gidan yari na shekaru 10, saboda an same shi da laifin fyade kan wata yarinya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Cafke Wani Da Ake Zargin Dan Ta’adda Ne A Jihar Kebbi

November 15, 2025
NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano
Kotu Da Ɗansanda

NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

November 14, 2025
An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa
Kotu Da Ɗansanda

An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa

November 8, 2025
Next Post
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje

LABARAI MASU NASABA

Wasu Mahara Sun Kashe Mata 2, Tare Da da Ƙona Gidansu A Tudun Yola

Wasu Mahara Sun Kashe Mata 2, Tare Da da Ƙona Gidansu A Tudun Yola

November 15, 2025
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje

November 15, 2025
Fashi Da Makami: An Yanke Wa ’Yan Nijeriya Hudu Mazauna Birtaniya Hukuncin Daurin Shekara 55 A Gidan Yari

Fashi Da Makami: An Yanke Wa ’Yan Nijeriya Hudu Mazauna Birtaniya Hukuncin Daurin Shekara 55 A Gidan Yari

November 15, 2025
Shugaban APC Na Kano Ya Nemi Afuwa Daga Al’ummar Fagge Kan Kalamansa

Shugaban APC Na Kano Ya Nemi Afuwa Daga Al’ummar Fagge Kan Kalamansa

November 15, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Cafke Wani Da Ake Zargin Dan Ta’adda Ne A Jihar Kebbi

November 15, 2025
Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

November 14, 2025
NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

November 14, 2025
NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

November 14, 2025
Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

November 14, 2025
Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

November 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.