• English
  • Business News
Saturday, May 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Firaministan Sin Ya Nuna Cikakken Kwarin Gwiwa Kan Yanayin Tattalin Arzikin Kasar Sin

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Firaministan Sin Ya Nuna Cikakken Kwarin Gwiwa Kan Yanayin Tattalin Arzikin Kasar Sin
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sabon firaministan kasar Sin Li Qiang ya bayyana cewa, kasar Sin tana da cikakken kwarin gwiwa kan makomar tattalin arzikin kasar. Yana mai cewa, za ta magance abubuwan dake neman hana ruwa gudu, don samun kyakkyawar makoma.

Li Qiang ya shaidawa taron manema labarai hakan ne Litinin din nan, bayan kammala taron farko na majalisar wakilan jama’ar kasar Sin karo na 14.
Li ya ce, idan har ana fatan cimma burin samun bunkasuwar yawan GDP da ya kai kusan kashi 5 bisa 100 a shekarar 2023, bisa babban tushen da ake samu a fannin tattalin arzikin kasar a halin yanzu, to hakan ba abu ne mai sauki ba, kuma yana bukatar kara zage damtse.

Ya kara da cewa, babban makasudin aikin jam’iyyar da ma gwamnati shi ne, kyautata jin dadin jama’a. Don haka wajibi ne a ko da yaushe gwamnati ta yi shiri tare da gudanar da ayyukanta bisa laakari da abin da jamaa ke ji da kuma aiwatar da bukatun jamaa.

Li Qiang ya bayyana cewa, kamfanoni masu zaman kansu dake kasar Sin, za su more yanayi mai kyau da kuma babbar dama ta samun ci gaba.

Li ya fadawa taron manema labarai cewa, gwamnati za ta kara zage damtse wajen samar da yanayin kasuwanci mai dogaro da kasuwa, bisa tsarin doka da kuma kasa da kasa, da kula da dukkan nauoin kamfanoni ba tare da nuna wani bambanci ba, da kare yancin mallakar kamfanoni da hakkoki da muradun yan kasuwa bisa doka.

Labarai Masu Nasaba

Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Farko Ta Sin Ta Dawo Daga Abyei Cikin Nasara

An Fara Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Matakin Koli Tsakanin Sin Da Amurka A Geneva

Li ya bayyana cewa, kasar Sin za ta samar da daidaito ga kowane nau’in kasuwanci, da kara tallafawa kamfanoni masu zaman kansu, wajen bunkasa harkokinsu na kasuwanci.

Li Qiang ya bayyana cewa, kasar Sin za ta kara fadada bude kofa ga kasashen waje bisa manyan ka’idojin cinikayya na kasa da kasa, kuma za ta kara bude kofarta ga duniya tare da kyautata yanayin kasuwanci da samar da hidimomi.

Da yake karin hakse game da dangantakar Sin da Amurka kuwa, Li ya ce, Sin da Amurka za su iya yin hadin gwiwa, kuma dole ne su yi aiki tare, akwai kuma abubuwa da dama da kasashen biyu za su cimma ta hanyar yin aiki tare.
Li ya kara da cewa, matsayar da aka cimma tsakanin manyan shugabannin kasashen Sin da Amurka a yayin ganawar da suka yi a watan Nuwamban da ya gabata, na bukatar a fassara ko aiwatar da su zuwa hakikanin manufofi da ayyuka na zahiri. (Ibrahim Yaya)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Jinping: Ba Za A Ci Amanar Jama’a Ba

Next Post

Da Dumi-Dumi: CBN Ya Ba Wa Bankuna Umarnin Su Fitar Da Tsofaffin Kudade — Soludo

Related

Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Farko Ta Sin Ta Dawo Daga Abyei Cikin Nasara
Daga Birnin Sin

Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Farko Ta Sin Ta Dawo Daga Abyei Cikin Nasara

22 minutes ago
An Fara Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Matakin Koli Tsakanin Sin Da Amurka A Geneva
Daga Birnin Sin

An Fara Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Matakin Koli Tsakanin Sin Da Amurka A Geneva

1 hour ago
Sharhi: Sin Da Rasha Suna Sauke Nauyin Dake Wuyansu
Daga Birnin Sin

Sharhi: Sin Da Rasha Suna Sauke Nauyin Dake Wuyansu

3 hours ago
Sin Ta Nemi Indiya Da Pakistan Su Muhimmanta Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali
Daga Birnin Sin

Sin Ta Nemi Indiya Da Pakistan Su Muhimmanta Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali

5 hours ago
Xi Jinping Ya Gana Da Shugabannin Kasashe Daban-Daban A Moscow
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Gana Da Shugabannin Kasashe Daban-Daban A Moscow

6 hours ago
Likitocin Sin Sun Ba Da Jinya Kyauta A Yankunan Karkara Na Saliyo
Daga Birnin Sin

Likitocin Sin Sun Ba Da Jinya Kyauta A Yankunan Karkara Na Saliyo

24 hours ago
Next Post
Da Dumi-Dumi: CBN Ya Kara Wa’adin Daina Amfani Da Tsoffin Kudade A Nijeriya

Da Dumi-Dumi: CBN Ya Ba Wa Bankuna Umarnin Su Fitar Da Tsofaffin Kudade — Soludo

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Farko Ta Sin Ta Dawo Daga Abyei Cikin Nasara

Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Farko Ta Sin Ta Dawo Daga Abyei Cikin Nasara

May 10, 2025
An Fara Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Matakin Koli Tsakanin Sin Da Amurka A Geneva

An Fara Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Matakin Koli Tsakanin Sin Da Amurka A Geneva

May 10, 2025
Sharhi: Sin Da Rasha Suna Sauke Nauyin Dake Wuyansu

Sharhi: Sin Da Rasha Suna Sauke Nauyin Dake Wuyansu

May 10, 2025

Kungiyar Malaman Jami’o’i Ta Ba Dalibai 164 Tallafin Karatu

May 10, 2025
Dalilan Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmaci (5)

Dalilan Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmaci (5)

May 10, 2025
Sin Ta Nemi Indiya Da Pakistan Su Muhimmanta Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali

Sin Ta Nemi Indiya Da Pakistan Su Muhimmanta Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali

May 10, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Shugabannin Kasashe Daban-Daban A Moscow

Xi Jinping Ya Gana Da Shugabannin Kasashe Daban-Daban A Moscow

May 10, 2025
Ra’ayin Al’umma Game Da Iyaye Masu Furta Muggan Kalamai A Kan ‘Ya’yansu

Ra’ayin Al’umma Game Da Iyaye Masu Furta Muggan Kalamai A Kan ‘Ya’yansu

May 10, 2025
Wayar Salula Na Dab Da Kai Mu Wutar Jahannama

Wayar Salula Na Dab Da Kai Mu Wutar Jahannama

May 10, 2025
Martanin Kwankwaso Ga Kawu Sumaila Da Sauran Masu Ficewa Daga NNPP

Martanin Kwankwaso Ga Kawu Sumaila Da Sauran Masu Ficewa Daga NNPP

May 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.