ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 18, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Jinping: Ba Za A Ci Amanar Jama’a Ba

by CMG Hausa
3 years ago
xi jinping

Yau Litinin 13 ga wata ne, aka rufe taron shekara-shekara na majalisar wakilan jama’ar kasar Sin NPC a nan birnin Beijing, fadar mulkin kasar Sin.

Shugaban kasar Sin, kana babban sakataren kwamitin tsakiyar jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin, kuma shugaban kwamitin kolin rundunar sojan kasar Sin Xi Jinping ya bayyana cikin jawabinsa yayin bikin rufe taron cewa, amincewar da jama’ar suka nuna masa, ta karfafa masa gwiwar neman samun ci gaba, wadda kuma shi ne nauyin da ke wuyansa. Xi ya kara da cewa, zai yi iyakacin kokarinsa wajen ganin ya sauke nauyin da kundin tsarin mulkin kasa ya dora masa. Zai kuma yi aiki tukutu bisa bukatun kasa, da muradun jama’a. Bugu da kari, zai sadaukar da kansa. Ba zai kuma ci amanar wakilan jama’a masu halartar taron da kuma daukacin al’ummomin kabilun kasa ba.

  • Xi Ya Sanya Hannu Kan Umarnin Shugaba Na Nada Li Qiang A Matsayin Firaministan Kasar

Xi Jinping ya jaddada cewa, za mu ci gaba da raya kasar Sin mai karfi gami da farfado da al’ummar Sinawa, kamar yadda kaka da kakaninmu suka yi a baya. Xi ya bayyana cewa, al’ummar Sinawa sun cimma gagaruman nasarori a tarihi, tare da jure wahalhalu masu yawa. Bayan kafuwar jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin, ta hanyar hada kan al’ummomim kabilu daban daban na kasar da kuma ba da jagora wajen yin gwagwarmaya har tsawon shekaru fiye da 100, don sake dawo mutuncinmu. Al’ummar Sinawa sun dawo da makomarsu a hannunsu. Al’ummomin Sinawa sun sake tsayawa da kafaffunsu, sun samu wadata. Yanzu suna kokarin raya kasarsu mai karfi. Ba wanda zai iya hana babban sha’anin farfado da al’ummar Sinawa. Kar a ci amanar jama’a. Wajibi ne a shugabanni su sauke nauyin da zamani da kuma tarihi ya dora musu, su ba da tasu gudummowa wajen kara azama kan raya kasar Sin mai karfi da farfado da al’ummar Sinawa, kamar yadda kaka da kakaninsu suka yi a baya.

ADVERTISEMENT

Xi Jinping ya jaddada cewa, yayin da ake raya kasar Sin mai karfi, tilas ne a karfafa raya jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin, ko da yaushe a tafiyar da harkokin jam’iyyar a tsanake ba tare da kasala ba, kuma a kara yin yaki da cin hanci da karbar rashawa ba kakkautawa.

Xi Jinping ya yi nuni da cewa, za a yi kokarin zamanintar da harkokin tsaron kasa da ma rundunar sojan kasar, ta yadda rundunar sojan kasar za ta taka rawar da ta kamata wajen kare ikon mulkin kai da tsaro da moriyar ci gaban kasar.

LABARAI MASU NASABA

Xi: Sin Na Gudanar Da Ayyukan Hadin Gwiwa Tsakanin Yankunan Gabashi Da Yammacin Kasar

Sin Ta Samar Da Tallafin Jin Kai Na Gaggawa Ga DRC Da AU

Xi Jinping ya ce, ci gaban kasar Sin na haifar da alfanu ga duniya, kuma kasar Sin ba za ta iya ware kanta da sauran kasashen duniya wajen tabbatar da ci gabanta ba. Kasar Sin za ta ci gaba da bude kofarta ga duniya, da yin amfani da kasuwanni da ma albarkatu na duniya don raya kanta, tare kuma da sa kaimin ci gaban duniya baki daya.

Xi Jinping ya ci gaba da cewa, kasar Sin za ta tsaya tsayin daka wajen tabbatar da ci gaba mai inganci da kuma mai da jama’a a gaban kome, a kokarinta na raya kanta da ma farfado da al’ummar kasar, za kuma ta yi kokarin tabbatar da manufar “kasa daya amma tsarin mulki iri biyu” da dinkuwar kasar baki daya, tare da kokarin gina al’umma mai kyakkyawar makoma ga dukkan bil’adama. (Tasallah Yuan & Lubabatu Lei)

xi jinping
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Xi: Sin Na Gudanar Da Ayyukan Hadin Gwiwa Tsakanin Yankunan Gabashi Da Yammacin Kasar
Daga Birnin Sin

Xi: Sin Na Gudanar Da Ayyukan Hadin Gwiwa Tsakanin Yankunan Gabashi Da Yammacin Kasar

June 17, 2026
Sin Ta Samar Da Tallafin Jin Kai Na Gaggawa Ga DRC Da AU
Daga Birnin Sin

Sin Ta Samar Da Tallafin Jin Kai Na Gaggawa Ga DRC Da AU

June 17, 2026
Fahimtar Tattalin Arzikin Sin Na Watannin Biyar Na Farkon Bana Ta Kalmomi Guda Uku
Daga Birnin Sin

Fahimtar Tattalin Arzikin Sin Na Watannin Biyar Na Farkon Bana Ta Kalmomi Guda Uku

June 17, 2026
Next Post
Firaministan Sin Ya Nuna Cikakken Kwarin Gwiwa Kan Yanayin Tattalin Arzikin Kasar Sin

Firaministan Sin Ya Nuna Cikakken Kwarin Gwiwa Kan Yanayin Tattalin Arzikin Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Shigo Da Fetur Ya Ƙaru Da Kashi 59.5% A Watan Mayu A Nijeriya — NMDPRA

Shigo Da Fetur Ya Ƙaru Da Kashi 59.5% A Watan Mayu A Nijeriya — NMDPRA

June 18, 2026
Gwamnatin Kwara Ta Kai Saraki Kotu Kan Zargin Ɓata Sunan Gwamna AbdulRazaq

Gwamnatin Kwara Ta Kai Saraki Kotu Kan Zargin Ɓata Sunan Gwamna AbdulRazaq

June 18, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

June 18, 2026
2027: Tsohon Kakakin Majalisar Kaduna Abdulfatah Ya Zama Ɗan Takarar Gwamnan PRP

2027: Tsohon Kakakin Majalisar Kaduna Abdulfatah Ya Zama Ɗan Takarar Gwamnan PRP

June 18, 2026
Sojoji Sun Ceto Mutane 5 Da Aka Sace A Kogi

Sojoji Sun Ceto Mutane 5 Da Aka Sace A Kogi

June 18, 2026
Kotu A Birtaniya Ta Wanke Diezani Daga Zargin Cin Hanci

Kotu A Birtaniya Ta Wanke Diezani Daga Zargin Cin Hanci

June 18, 2026
’Yan Bindiga Sun Kashe Mutum Ɗaya, Sun Sace Limami Da Wasu Mutane 7 A Filato

‘Yan Bindiga Sun Kashe Hakimin Gwande A Jihar Filato

June 18, 2026
Matsalar Tsaro: Davido Ya Mayar Wa Rarara Martani Kan Rashin Tsaro

Matsalar Tsaro: Davido Ya Mayar Wa Rarara Martani Kan Rashin Tsaro

June 18, 2026
Xi: Sin Na Gudanar Da Ayyukan Hadin Gwiwa Tsakanin Yankunan Gabashi Da Yammacin Kasar

Xi: Sin Na Gudanar Da Ayyukan Hadin Gwiwa Tsakanin Yankunan Gabashi Da Yammacin Kasar

June 17, 2026
Sin Ta Samar Da Tallafin Jin Kai Na Gaggawa Ga DRC Da AU

Sin Ta Samar Da Tallafin Jin Kai Na Gaggawa Ga DRC Da AU

June 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.