Jagoran jam’iyyar NNPP Sanata Rabiu Kwankwaso ya yi kakkausar suka ga ‘yan siyasar da suka sauya sheƙa bayan samun goyon bayan jama’a, inda ya kira halin hakan a matsayin “babban laifin siyasance.” Ya bayyana hakan ne a wajen karɓar sabbin mambobin jam’iyyar daga Takai a gidansa da ke Kano.
Kwankwaso ya mayar da wannan martani ne bayan wasu manyan ‘yan jam’iyyar da suka koma APC, ciki har da Sanatan Kano ta Kudu Abdurrahman Kawu Sumaila da ɗan majalisar wakilai Kabiru Alhassan Rurum. Ya yi tir da waɗanda suka samu ragamar mulki ta hanyar ƙuri’un jama’a a jam’iyyarsu amma sai suka juya su ga abokan adawa.
“Wannan shi ne mafi girman cin amana a tsarin dimokuraɗiyya. Ban san wani laifi mafi girma ba fiye da lokacin da talakawa suka zaɓe ku don gujewa mayaudara, amma sai ku juya ku shiga cikinsu. Da sun sani, da ba su zaɓe ku ba,”
in ji shi.
Ya kuma yi gargaɗin cewa duk wanda ya yi yunƙurin kai hari kan tsarin Kwankwasiyya zai fuskanci tsayin daka mai ƙarfi. Daga nan yayi kira ga mabiyansa da su ci gaba da faɗaɗa jam’iyyar ta hanyar jawo sabbin mambobi daga matakin gundumomi.
Kwankwaso ya jaddada cewa Kwankwasiyya yunƙuri ne na hidima ga jama’a ba na neman riba ba. Ya yi ishara da zaɓen Kano ta Kudu inda ya ce wasu sun sayar da ƙuri’unsu kan taliya da ₦2,000, amma talakawan Kano sun tsaya tsayin daka ba su sayar da ƴancinsu ba.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp