ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wayar Salula Na Dab Da Kai Mu Wutar Jahannama

by Ibrahim Bala
1 year ago
Salula

Assalamu Alaikum Wa Rahmatullahi Ta’ala Wa Barakatuhu.

Muna godiya ga Allah me kowa me komai daya ba mu ikon numfashi, mu ci mu sha mu kwanta mu tashi cikin yardar sa. Kamar kowane mako yau ma filin na tafe da wani batun wanda ya kamata a duba kuma a rika kulawa domin ingantuwar tarbiyya.

A yau zan yi magana ne a kan abin da ya shafi social media wato yanar gizo-gizo, da yawa daga cikin mutane ba su sani ba ko kuma an sani an danne ko ba a nemi sanin ba.

ADVERTISEMENT

Wayar salula da ake gani ko yanar gizo-gizo tana dab da kai mu wutar jahannama saboda abubuwan da muke yadawa muna kusan fita daga addininmu na musulunci, kusan ma wasu abubuwan mutum yana yin shirka ba tare da ya sani ba.

Na farko muna kusan hada wasu mutane da ubangiji wajen kaunarsu ko wajen yabonsu, wanda kuma Allah baya son kishiya mun riga mun sani. 

LABARAI MASU NASABA

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Mutum ka ga a social media yana ta fostin din wani sai ka ga kamar Allah yake kodawa, wannan kirarin za ka ga Allah kadai ne me shi. Za ka ga mutum ya ce “Kai ne komai nawa, ka ne gata na” da dai sauransu to, wannan kuskure ne.

 

A wani bangaren irin bayanan da muke wani za a ga batsa ce wannan abubuwan sukan yi yaho a kafafen yada labarai ko yanar gizo-gizo, wanda idan wani ya koya ko ya dauka ko ya gani shi ma ya yada to, zunubin mutum yana kanka, ya kamata mu kiyaye.

Duk abin da ka yada idan ka yada alkhairi za ka samu lada, idan ka yada sharri za ka samu sharri. Ita waya da ku ke gani ba wai bature ya yi ta kawai dan ka yada abin da ka ga dama ba.

Na farko ga zumunci sannan zamani ya zo harkar kasuwanci, za ka iya yada abubuwan da ka ke siyarwa, idan fadakarwa ne za ka fadakar, amma dai irin abubuwan da muke yadawa barkatai ‘especially’ ‘yan mata za a ga abubuwan da ake ya wuce misali.

 

Su kan fitar da tsiraici mace ta dauki hoto ta nuna duk fa wanda ya ga wannan abun to, ba zai iya aurenki ba, ya kamata mu gane babu saurayin da zai ga budurwa a social media tana nuna jikinta/ tsiraicinta ya aure ta babu, ko shi waye magana ta domin Allah, ya kamata a kiyaye musamman mata su suke haka.

Sannan su ma samarin a kiyaye domin su suke tayawa ba dan suna tayawar ba matan ba za su rika sakawa ba, dole ya zamto cewa ana jan hankali wajen a bari a daina ko ba kanwarka bace ba kila ‘yarka ce, ko ba ‘yarka bace ba kila ‘yar’uwarka ce ko ba ‘yar’uwarka ba ce ba kila ‘yar’uwar wani ce, ko ‘yar’uwar abokinka ko kanwar abokinka, irin wadannan abubuwan idan muka hana su za mu ga to, gaba ma ‘ya’yanmu da za su taso ba za su tadda su ba.

 

Amma idan tun yanzu muke da damar da zamu hana mu tsawatar mu yi wa’azi mu yi nasiha a kai ba a daina ba to, lokacin kuma da babu kai sai ka ga abun ya zo a kan ‘ya’yanka su ma suna yi in ba a lura an fadakar ba.

Dan Allah dan Annabi mu yada abubuwan da zai zamo mana na alkhairi, za mu samu alkhairi idan muka yi na sharri zai zam mana sharri, ko masu yada yabon mutane musamman a bangare na siyasa mu yi hankali mu daina sa mutane a wani bangare wanda za a ga kamar ubangiji ne wannan.

Allah ya sa mu dace .

Salula
Ibrahim Bala
+ postsBio
  • Ibrahim Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-bala-2/
    2027: Bukatar Zaben Shugabanni Na Gari
  • Ibrahim Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-bala-2/
    Mene Ne Hukuncin Yin Jam’i Na Biyu A Masallacin Da Ke Da Limami Ratibi 

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba
Labarai

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi
Labarai

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Next Post
Ra’ayin Al’umma Game Da Iyaye Masu Furta Muggan Kalamai A Kan ‘Ya’yansu

Ra’ayin Al’umma Game Da Iyaye Masu Furta Muggan Kalamai A Kan ‘Ya’yansu

LABARAI MASU NASABA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.