Kungiyar Malaman Jami’oi ta kasa (ASUU) ta bada guraben tallafi karatu na shekarar 2024 ga dalibai 164 wadanda basu da halin da za’a iya biya masu kudin makaranta,a Jami’ar da take daga dukkan sassan kungiyar a fadin tarayyar Nijeriya.
Jaridar LEADERSHIP ta ranar Lahadi ta bada rahoton cewar sassan kungiyar ASUU 79,an ba dalibai biyu daga kowane sashen,yadda aka zabi mutanen biyu ba karamin aiki aka yi ba.
Mai neman irin wannan tallafin na karatu sai ya nuna cewa lalle babu yadda za ayi a biya ma shi kudin makarantar,bugu da kari kuma ya kasance sakamakon jarabawarsa ta ta zangon daya gabata shi ma yana da kyau, kafin ya samu cancantar samun tallafin.
Shugaban bayar da tallafin karatun na ASUU,kwamitin bincike da kuma wallafawa, Farfesa Christopher Piwuna,shi ne ya bayyana hakan ranar Asabar ta makon daya gabata a wuri kwanan dalibai na Jami’ar Sa’adu Zungur,da ke Yuli,Bauchi.
Ya ce duk wanda ya samu tallafin karatun zai tafi gida da zunzurutun kudi har Naira 200,000.
Farfesa Lawan Abubakar tsohon jagora na ASUU shiyyar Bauchi shi, ya wakilci wanda ya kira taron, ya ce yadda aka yi zaben wadanda suka cancanci samun tallafin kuma an yi amfani da adalci tsakanin jinsin mace da namiji, suma wadanda suke da bukata ta musamman, saboda a taimaka masu wajen bunkasa iiminsu.
Ya ce a shekaru biyu da suka gabata kungiyar ASUU ta kashe fiye da Naira milyan 164.kudaden bada tallafin karatu ga wadanda ba su da halin biyan kudin a Jami’oin da ake da su a fadin tarayyar Nijeriya.
Ya ce“Kungiyarmu ta ci gaba da amfani da kuma kula da lamarin bayar da tallafin karatu na Gani Fawehinmi,tsawon shekrun da suka gabata.Ba kawai mun tsaya bane sai kawai ta shi Chief Fawehinmi, amma muma mu kafa tamu.Wannan damar ta samu ne saboda muka lura da yadda gwamnati take tsauwalawa dalibai kudin makaranta masu wuyar iya biya.’
“Lokacin da muka ce lamarin tallafin karatu na Hukumar NELFUND, muna da wata manufa ce sabod ai bamu ce wani Uba ko wanda ya amfana da tallafin ya biya mu a wani lokaci ba kamar yadda Farfesa Piwuna ya kara jaddadawa,”.
Wasu daga cikin wadanda suka amfana da tallafin na yin karatu da aka yi hira da su,sun nuna jin dadinsu,ga kungiyar ta ASUU saboda tallawa iliminsu da tayi, suka kuma yi alkawarin za su yi amfani kudaden daidai wurin da ya dace.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp