• English
  • Business News
Saturday, November 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

FOCAC Ba Wani Dandali Na Tattaunawa Kawai Ba Ne

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
FOCAC

Za a kaddamar da taron koli na dandalin tattaunawar hadin gwiwar Sin da Afirka (FOCAC) a birnin Beijing na kasar Sin a ranar 4 ga wata mai zuwa, inda dimbin shugabannin kasashe daban daban na nahiyar Afirka, ciki har da shugaban kasar Najeriya Bola Tinubu, za su halarci taron. Watakila za ka so tambaya kan cewar me ya sa dimbin kasashen dake nahiyar Afirka ke dora matukar muhimmanci kan taron?

 

Don samun amsa ga tambayar, za a iya duba makalar da Charles Onunaiju, darektan cibiyar nazarin kasar Sin ta Najeriya, ya rubuta, wadda aka wallafa a shafin yanar gizo ko Internet ta jaridar The Punch ta Najeriya, a ranar 26 ga watan da muke ciki. Cikin makalar, Mista Onunaiju ya ce, tsarin FOCAC ya riga ya zama wani dandalin hadin kan kasa da kasa mafi tasiri a nahiyar Afirka, wanda ya samar da dimbin ayyukan da suke taimakawa kokarin horar da ma’aikata a nahiyar Afirka, da biyan bukatun jama’ar nahiyar na kyautata zaman rayuwa, da sassanta yanayin da ake ciki na karancin kayayyakin more rayuwa a nahiyar Afirka.

  • Tawagar Jiragen Rundunar Sojin Saman Kasar Sin Ta Tafi Masar Domin Halartar Wani Bikin Nune-Nune
  • Inganta Raya Shawarar BRI Zai Zama Daya Daga Manyan Batutuwan Da Za A Tattauna A Gun Taron Kolin FOCAC Na Bana

A cewar Mista Onunaiju, tarukan kolin FOCAC guda 2 da suka gabata sun sa kasashen Afirka samun rancen kudi da yawansa ya kai dalar Amurka biliyan 120, don biyan bukatunsu na raya wasu muhimman bangarori na hadin gwiwa, da suka shafi raya kayayyakin more rayuwa, da masana’antu, da zamanantar da aikin gona, da dai sauransu. Ta wannan hanya aka sa kaimi ga farfadowar tattalin arzikin kasashen Afirka, da haifar da dimbin guraben aikin yi, da habaka cinikin da ake yi tsakanin kasashe daban daban dake nahiyar Afirka. Mista Onunaiju ya kuma takaita ra’ayinsa kamar haka: “Dandalin tattaunawar FOCAC bai tsaya kan kasancewar wani dandali na tattaunawa da musayar ra’ayi kawai ba. Shi ma ya haifar da dimbin sakamako masu amfani, da tabbatar da karuwar tattalin arzikin kasashen Afirka”.

 

LABARAI MASU NASABA

Duk Da Barazanar Tattalin Arzikin Duniya, Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Da Kwanciyar Hankali A Duniyarmu Mai Cike Da Ruɗani

Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Ci Gaban Kasashen Afirka?

Hakika Mista Onunaiju ya bayyana dalilin da ya sa kasashen Afirka ke dora muhimmanci kan taron FOCAC, wato saboda FOCAC din ba wani dandalin tattaunawa kawai ba ne, maimakon haka, ya kasance wani tsarin hadin gwiwa na aiwatar da matakai, da cika alkawari, don haifar wa kasashen Afirka da damar samun hakikanin ci gaba.

 

To, ta yaya ake kokarin cika alkawari? Kasar Sin ta sanar da manyan ayyukan hadin gwiwar Sin da Afirka guda 9, a taron ministoci karon 8 na dandalin tattaunawar FOCAC na shekarar 2021. Zuwa yanzu, an aiwatar da ayyukan yadda ake bukata, tare da samar da dimbin nasarori. Idan mun dauki aikin rage talauci da tallafawa manoma a matsayin misali, kasar Sin ta aiwatar da ayyuka 47 na rage talauci, da hadin gwiwa a fannin aikin gona, a kasashen Afirka, tare da horar da manoma kimanin dubu 9, da yayata fasahohin zamani fiye da 300, inda aka haifar da alfanu ga iyalai na manoma fiye da miliyan 1 dake nahiyar Afirka. Ban da haka, fasahar noman laimar kwado ta kasar Sin da ake kira fasahar Juncao ta sa mutanen Afirka fiye da dubu 100 samun karin kudin shiga, yayin da fasahar noman shinkafar zamani da aka tagwaita mai samar da yawan iri ko Hybrid ta kasar Sin, ta ba da damar kara yawan shinkafar da ake samu a kasashen Afirka daga ton 2 zuwa ton 7.5 kan kadada guda.

 

Yadda kasar Sin ke cika alkawari shi ma ya shafi yadda kasar ke amsa kiran da kasashen Afirka suka yi mata, don tabbatar da amfanin juna, da samun moriya tare, a hadin gwiwar da ake yi tsakaninsu. Misali, bayan da kasashen Afirka suka gabatar da korafe-korafe kan batun rashin daidaito a cinikayyar da ake yi tsakanin Sin da Afirka, kasar Sin ta fara daukar matakin sa kaimi ga aikin shigar da kayayyaki daga kasashen Afirka. Inda ta yafe ma kasashe marasa karfin tattalin arziki 21 dake nahiyar Afirka harajin kwastam bisa kaso 98% na kayayyakin da suke sayarwa a kasuwannin Sin, haka kuma an bude hanya mai sauki da ake kira “Green Lane” ga aikin shigar da amfanin gonan kasashen Afirka cikin kasar Sin. Haka zalika, kasar Sin ta ba kasashen Afirka damar sayar da karin amfanin gona a kasuwannin Sin ta hanyar kasuwanci ta yanyar gizo ko Internet. Wadannan matakan da aka dauka sun sa yawan amfanin gonan kasashen Afirka da aka sayar zuwa kasar Sin karuwa cikin shekaru 7 a jere. A shekarar 2023, nau’o’in gyada da kasar Sin ta shigar da su daga kasashen Afirka sun karu da kaso 130% bisa makamancin lokacin shekarar 2022, yayin da kayayyakin lambun da kasar ta shigar daga Afirka sun karu da kaso 32%. Ban da haka, a rabin farko na shekarar bana, darajar kayayyakin da kasar Sin ta shigo da su daga kasashen Afirka ta kai dalar Amurka biliyan 60.1, wadda ta karu da kaso 14% bisa makamancin lokacin bara.

 

Mista Onunaiju ya rubuta a cikin makalarsa cewa, “Wata shaharariyar halayyar kasar Sin ita ce: Nacewa ga shirin da aka tsara, gami da kokarin aiwatar da shi. Wadda ta kasance wani babban dalilin da ya tabbatar da tasowar tattalin arzikin kasar. ” A zahiri dai, wannan halayya ita ma ta zama tushen karfafawar hadin gwiwar Sin da Afirka a kai a kai. (Bello Wang)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Duk Da Barazanar Tattalin Arzikin Duniya, Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Da Kwanciyar Hankali A Duniyarmu Mai Cike Da Ruɗani
Ra'ayi Riga

Duk Da Barazanar Tattalin Arzikin Duniya, Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Da Kwanciyar Hankali A Duniyarmu Mai Cike Da Ruɗani

October 28, 2025
Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Ci Gaban Kasashen Afirka?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Ci Gaban Kasashen Afirka?

October 27, 2025
Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata
Ra'ayi Riga

Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata

October 23, 2025
Next Post
Wang Yi Da Jake Sullivan Sun Tattauna Kan Sabon Zagayen Tattaunawa Tsakanin Shugabannin Kasashen Biyu A Nan Gaba

Wang Yi Da Jake Sullivan Sun Tattauna Kan Sabon Zagayen Tattaunawa Tsakanin Shugabannin Kasashen Biyu A Nan Gaba

LABARAI MASU NASABA

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

October 31, 2025
Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

October 31, 2025
Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

October 31, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

October 31, 2025
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

October 31, 2025
Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

October 31, 2025
Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

October 31, 2025
Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba

Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba

October 31, 2025
Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar

Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar

October 31, 2025
Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi

Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi

October 31, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.