ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

FOCAC Ba Wani Dandali Na Tattaunawa Kawai Ba Ne

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 years ago
FOCAC

Za a kaddamar da taron koli na dandalin tattaunawar hadin gwiwar Sin da Afirka (FOCAC) a birnin Beijing na kasar Sin a ranar 4 ga wata mai zuwa, inda dimbin shugabannin kasashe daban daban na nahiyar Afirka, ciki har da shugaban kasar Najeriya Bola Tinubu, za su halarci taron. Watakila za ka so tambaya kan cewar me ya sa dimbin kasashen dake nahiyar Afirka ke dora matukar muhimmanci kan taron?

 

Don samun amsa ga tambayar, za a iya duba makalar da Charles Onunaiju, darektan cibiyar nazarin kasar Sin ta Najeriya, ya rubuta, wadda aka wallafa a shafin yanar gizo ko Internet ta jaridar The Punch ta Najeriya, a ranar 26 ga watan da muke ciki. Cikin makalar, Mista Onunaiju ya ce, tsarin FOCAC ya riga ya zama wani dandalin hadin kan kasa da kasa mafi tasiri a nahiyar Afirka, wanda ya samar da dimbin ayyukan da suke taimakawa kokarin horar da ma’aikata a nahiyar Afirka, da biyan bukatun jama’ar nahiyar na kyautata zaman rayuwa, da sassanta yanayin da ake ciki na karancin kayayyakin more rayuwa a nahiyar Afirka.

ADVERTISEMENT
  • Tawagar Jiragen Rundunar Sojin Saman Kasar Sin Ta Tafi Masar Domin Halartar Wani Bikin Nune-Nune
  • Inganta Raya Shawarar BRI Zai Zama Daya Daga Manyan Batutuwan Da Za A Tattauna A Gun Taron Kolin FOCAC Na Bana

A cewar Mista Onunaiju, tarukan kolin FOCAC guda 2 da suka gabata sun sa kasashen Afirka samun rancen kudi da yawansa ya kai dalar Amurka biliyan 120, don biyan bukatunsu na raya wasu muhimman bangarori na hadin gwiwa, da suka shafi raya kayayyakin more rayuwa, da masana’antu, da zamanantar da aikin gona, da dai sauransu. Ta wannan hanya aka sa kaimi ga farfadowar tattalin arzikin kasashen Afirka, da haifar da dimbin guraben aikin yi, da habaka cinikin da ake yi tsakanin kasashe daban daban dake nahiyar Afirka. Mista Onunaiju ya kuma takaita ra’ayinsa kamar haka: “Dandalin tattaunawar FOCAC bai tsaya kan kasancewar wani dandali na tattaunawa da musayar ra’ayi kawai ba. Shi ma ya haifar da dimbin sakamako masu amfani, da tabbatar da karuwar tattalin arzikin kasashen Afirka”.

 

LABARAI MASU NASABA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

Hakika Mista Onunaiju ya bayyana dalilin da ya sa kasashen Afirka ke dora muhimmanci kan taron FOCAC, wato saboda FOCAC din ba wani dandalin tattaunawa kawai ba ne, maimakon haka, ya kasance wani tsarin hadin gwiwa na aiwatar da matakai, da cika alkawari, don haifar wa kasashen Afirka da damar samun hakikanin ci gaba.

 

To, ta yaya ake kokarin cika alkawari? Kasar Sin ta sanar da manyan ayyukan hadin gwiwar Sin da Afirka guda 9, a taron ministoci karon 8 na dandalin tattaunawar FOCAC na shekarar 2021. Zuwa yanzu, an aiwatar da ayyukan yadda ake bukata, tare da samar da dimbin nasarori. Idan mun dauki aikin rage talauci da tallafawa manoma a matsayin misali, kasar Sin ta aiwatar da ayyuka 47 na rage talauci, da hadin gwiwa a fannin aikin gona, a kasashen Afirka, tare da horar da manoma kimanin dubu 9, da yayata fasahohin zamani fiye da 300, inda aka haifar da alfanu ga iyalai na manoma fiye da miliyan 1 dake nahiyar Afirka. Ban da haka, fasahar noman laimar kwado ta kasar Sin da ake kira fasahar Juncao ta sa mutanen Afirka fiye da dubu 100 samun karin kudin shiga, yayin da fasahar noman shinkafar zamani da aka tagwaita mai samar da yawan iri ko Hybrid ta kasar Sin, ta ba da damar kara yawan shinkafar da ake samu a kasashen Afirka daga ton 2 zuwa ton 7.5 kan kadada guda.

 

Yadda kasar Sin ke cika alkawari shi ma ya shafi yadda kasar ke amsa kiran da kasashen Afirka suka yi mata, don tabbatar da amfanin juna, da samun moriya tare, a hadin gwiwar da ake yi tsakaninsu. Misali, bayan da kasashen Afirka suka gabatar da korafe-korafe kan batun rashin daidaito a cinikayyar da ake yi tsakanin Sin da Afirka, kasar Sin ta fara daukar matakin sa kaimi ga aikin shigar da kayayyaki daga kasashen Afirka. Inda ta yafe ma kasashe marasa karfin tattalin arziki 21 dake nahiyar Afirka harajin kwastam bisa kaso 98% na kayayyakin da suke sayarwa a kasuwannin Sin, haka kuma an bude hanya mai sauki da ake kira “Green Lane” ga aikin shigar da amfanin gonan kasashen Afirka cikin kasar Sin. Haka zalika, kasar Sin ta ba kasashen Afirka damar sayar da karin amfanin gona a kasuwannin Sin ta hanyar kasuwanci ta yanyar gizo ko Internet. Wadannan matakan da aka dauka sun sa yawan amfanin gonan kasashen Afirka da aka sayar zuwa kasar Sin karuwa cikin shekaru 7 a jere. A shekarar 2023, nau’o’in gyada da kasar Sin ta shigar da su daga kasashen Afirka sun karu da kaso 130% bisa makamancin lokacin shekarar 2022, yayin da kayayyakin lambun da kasar ta shigar daga Afirka sun karu da kaso 32%. Ban da haka, a rabin farko na shekarar bana, darajar kayayyakin da kasar Sin ta shigo da su daga kasashen Afirka ta kai dalar Amurka biliyan 60.1, wadda ta karu da kaso 14% bisa makamancin lokacin bara.

 

Mista Onunaiju ya rubuta a cikin makalarsa cewa, “Wata shaharariyar halayyar kasar Sin ita ce: Nacewa ga shirin da aka tsara, gami da kokarin aiwatar da shi. Wadda ta kasance wani babban dalilin da ya tabbatar da tasowar tattalin arzikin kasar. ” A zahiri dai, wannan halayya ita ma ta zama tushen karfafawar hadin gwiwar Sin da Afirka a kai a kai. (Bello Wang)

FOCAC
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Xi Jinping Ya Taya Kim Jong-Un Murnar Cika Shekaru 78 Da Kafuwar Koriya Ta Arewa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
FOCAC
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna
  • Sulaiman
    Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba
  • Sulaiman
    Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa
  • Sulaiman
    Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

MASU ALAKA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta
Ra'ayi Riga

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

September 8, 2026
Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

September 4, 2026
Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa
Ra'ayi Riga

Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa

September 2, 2026
Next Post
Wang Yi Da Jake Sullivan Sun Tattauna Kan Sabon Zagayen Tattaunawa Tsakanin Shugabannin Kasashen Biyu A Nan Gaba

Wang Yi Da Jake Sullivan Sun Tattauna Kan Sabon Zagayen Tattaunawa Tsakanin Shugabannin Kasashen Biyu A Nan Gaba

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

September 9, 2026
Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

September 9, 2026
“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

September 9, 2026
’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

September 9, 2026
Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.