ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

G20: Kaduna Ce Jihar Da Tafi Dacewa Da Zuba Jari A Nijeriya – Gwamna Uba Sani 

by Shehu Yahaya and Sulaiman
4 weeks ago
G20

Gwamnatin Jihar Kaduna ta ƙara jaddada kudirinta na jawo masu zuba jari na ƙasa da ƙasa zuwa jihar. 

 

Yayin da yake gabatar da Jawabi a taron koli na manyan ‘yan kasuwa na duniya wanda ya gudana a kasar Afrika ta Kudu, Gwamna Uba Sani ya gabatar da jihar Kaduna a matsayin jihar da tafi dacewa wajen zubar jari a Nijeriya.

ADVERTISEMENT
  • Yaushe Ne Ƙarshen Rikicin Yajin Aiki Tsakanin ASUU Da Gwamnatin Tarayya A Nijeriya?
  • Wasu Kura-kurai Da Matan Aure Ke Yi Ke Sa ‘Yan Aiki Aure Mazajensu

A cikin wata sanarwa da Kwamishinan Yaɗa Labarai, na jihar Kaduna Malam Ahmed Maiyaki, ya fitar, ya ce taron wanda Hukumar Kula da Zuba Jari ta Nijeriya (NIPC) da Ofishin Jakadancin Nijeriya tare da haɗin gwiwar MTN suka shirya, ya samu halartar manyan masu zuba jari na duniya, da jami’an gwamnati na matakai daban-daban.

 

LABARAI MASU NASABA

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

A cewar sanarwar, Gwamna Sani ya gabatar da Jihar Kaduna a matsayin jihar da ta fi dacewa da zuba jari a Nijeriya, wadda aka gina bisa sauye-sauyen manufofi, kwanciyar hankali, dokoki da yanayin kasuwanci mai sauƙi. Ya bayyana muhimman fannonin zuba jari guda huɗu kamar Noma, Sufuri, Ma’adinai da Makamashin Sabuntawa wanda su na daga cikin ginshiƙan dabarun ci gaban jihar.

 

Gwamnan ya kuma gana da shugabannin wata masana’antar tace ƙarafa masu daraja da ke Afirka ta Kudu, PMT Inda ta gabatar da tayin haɗin gwiwa ta hannun Kamfanin Samar da Ma’adinai na Kaduna (KMDC) domin saka hannun jari a ɓangaren ma’adinai da fasaha, gina ƙwarewa, da aiwatar da shirin kafa cibiyar tarawa da sarrafa ma’adinai a Kaduna.

 

Sanarwar ta ƙara da cewa, gwamnan ya tabbatar da cewa, ƙofar Kaduna a bude take ga masu zuba jari waɗanda ke bin ka’idoji masu dorewa tare da mayar da hankali kan samar da darajar dogon lokaci.

 

Hakazalika, sanarwar ta kuma ruwaito Gwamna Uba Sani yana yabawa Shugaba Bola Ahmed Tinubu bisa sauye-sauyen da suka inganta yanayin zuba jari a Najeriya tare da ƙarfafa jihohi wajen neman haɗin gwiwar ƙasashen duniya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli
Labarai

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani
Manyan Labarai

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Next Post
Rashin Tsaro: An Rufe Jami’ar Jihar Kebbi

Rashin Tsaro: An Rufe Jami'ar Jihar Kebbi

LABARAI MASU NASABA

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025
Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

December 20, 2025
Matasa Miliyan 80 Ne Ba Su Da Aikin Yi A Nijeriya

Matasa Miliyan 80 Ne Ba Su Da Aikin Yi A Nijeriya

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.