• English
  • Business News
Monday, August 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gangamin Yaki Da Cutar Kuturta A Nijeriya

by Ra'ayinmu
6 months ago
in Ra'ayinmu
0
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A duk ranar 26, na watan Janairun kowacce shekara ne, ake gudanar da bikin zagayowar ranar tunawa da masu larurar cutar Kuturta.

Nijeriya ta shiga cikin sahun kasashen duniya, wajen gudanar da bikin zagayowar ranar, tunawa da masu larurar Kuturta, ta wannan shekarar.

Mahimmancin wannan ranar ita ce, gano cutar a kan lokaci da kuma yadda za a magance ta.

Take taron na wannan shekarar 2025 shi ne, “Hada Kai, Domin Kakkave Cutar, wadda ke da mahimmanci a kawo karshen ta, fadin duniya”.

Manufar ita ce, domin a wayar da kai kan cutar, bayyana kalubalen da masu larurar ke fuskanta, tare da hada kai, domin a dakile cutar.

Labarai Masu Nasaba

Bukatar Hukunta Masu Jagorantar Kashe-kashe A Nijeriya

Akwai Bukatar Daina Cin Zarafin Malaman Makaranta

  • Karon Farko A Shekarar 2025: Turken Rarraba Hasken Wutar Lantarki Ya Fadi A Nijeriya
  • ‘Yan Nijeriya Ku Kauracewa Amfani Da Layukan Waya Na MTN, Airtel Da Glo – NLC

Muna sane da cewa, cutar a yanzu, ta kai akalla shekaru 4,000, inda hakan ya sanya ta kasance daya daga cikin tsoffin cutukan da alumma suka san da su,

Hukumar jin kai ta kasar Faransa wato Raoul Follereau ce, ta zavo wannan ranar, domin girmama rayuwar marigayi Mahatma Gandhi, da ya mutu a watan Janairun 1948.

Gandhi, a lokacin yana raye, ya yi aiki tukuru, domin tallafawa masu larurar.

Kimanin mutane 200,000 da suka kamu da cutar ne, ake duba lafiyarsu ako wacce shekara a kasashe 120, inda kuma wasu da dama, ke ci gaba da rayuwa da wasu nau’ukan cutar, musamman a yankin Asiya, Afrika da kuma a Kudancin Amurka.

Kazalika, cutar ta kasance, ta na daga cikin cututtukan da aka yi watsi da batunsu a yankin nahiyar Afirka wadda kuma ta ci gaba da zama abin damuwa, ga vangaren kiwon lafiya a kasar nan.

Sai dai, za a iya cewa, Nijeriya ta samu nasara a shirinta na kasa, na yakar cutar kusan kasa da yawan alummarta daya a cikin dubu goma a shekarar 1998.

Duk da wannan nasarar ta Nijeriya ta samu, akwai batutuwan maganar al’ada, kin sauya dabi’a da har yanzu, ke ci gaba da janyo samun vullar cutar a kasar.

Idan za a iya tunawa, Shirin Dakile Yaduwar Cutar Fuka da Kuturta ta kasa NTBLCP, da aka faro shirin a shekarar 1989, daga shekarar 1991 zuwa shekarar 2012, kimanin masu larurra su 111,788 aka bai wa magunguna masu karfi domin duba lafiyarsu

Kazalika, Nijeriya ta kuma samun wani tallafi daga Hukumar Kiwon Lafiya ta Duniya WHO na dakile cutar wanda ya kai kasa da duba lafiyar masu larurar su 10,000 a shekarar 2000.

Bisa saurin gano cutar a kasar nan, hakan ya sanya an samu kasa da kashi biyar, a cikin duk mutane 10,000, wanda hakan ya sanya a yanzu a Nijeriya aka samu raguwar cutar.

Sai dai, a wani matakin akwai yankunan da cutar ke yin kamari, inda ta kai ga a cikin duk mutune 10,000 ake samun mutum daya, na dauke da cutar.

Bugu da kari, kashi 10 aka samu na cutar a fadin Afirka a 2019, wanda a Nijeriya, da wasu kasashe 12 aka ruwaito cewa, an samu vullar cutar da ta kai daga 1,000–10,000.

A bikin zagayowar ranar cutar ta shekarar data gabata kungiyar kwarrun Likitocin Kiwon Lafiya ta kasa NMA, ta nuna damuwarta kan ci gaba da yaduwar cuatar, duk da kokarin da aka yi, na yakarata baki daya a kasar.

Har yanzu a kasar nana, ana ci gaba da samun rahoton masu fama da cutar, a wasu jihohin kasar, inda kuma a wasu kasashe 17, aka samu rahoton ana samun cutar a duk shekara, da ta kai 1,000.

Wasu alkaluma sun nuna cewa, daga 2011 zuwa 2021 a duk shekara ana samu sabbin kwayoyin cutar da suka kai guda 2,754, wanda suka kai kashi 93.

A cewar kungiyar, kashi 8.3 na sabbin kwayoyin cutar, ana samun su ne, a jikin yara ‘yan kasa da shekaru 15, wanda kuma sabbin kwayoyin cutar ke nuna cewa kashi 14.3 ke yanyo nakasa, wanda hakan ya nuna cewa, hakan ya faru ne, saboda jinkirin daukar matakan duba lafiyar wadanda suka kamu da kwayar cutar.

Bisa wasu alkamuna da Shirin Dakile Yaduwar Cutar Fuka da Kuturta ta kasa NTBLCP da kuma Shirin Buruli da ke Dakile Ciwon Ulcer ya fitar a 2022, sun nuna cewa, an samu sabbin kwayoyin cutar da suka kai 2393, a shekarar 2022, inda aka samu mata kashi 37, na dauke da kwayoyin cutar yara kuma kasa da goma na dauke da kwayoyin cutar.

Hukumar WHO ta bayyana cewa, akasari cutar ta fi shafar Ftar jikin bil Adma ne wacce kuma take janyowa wanda ya kamu da ita, nakasa, idan har ba a yi masa magani ba.

A cewar WHO, ana kamuwa da cutar na yazuwa ne daga Hanci da Bakin wanda ya kamu da ita.

Ana warke wa daga cutar, ta hanyar yin amfani da magungunan da ake yakarta da kuma yin gwaje-gwaje.

Sai dai, wadanda suka kamu da cutar, suna yin jinkirin zuwa a yi masu gwajinta, musamman domin kar a rinka nuna masu kyama.

Bikin ranar ya yi daidai da manufar cimma burin karnin rayuwa wato (SDGs).

Ranar ta kasance mai matukar mahimmanci wanda taron ke hado kan kwararu a fanin kiwon lafiya domin tattaunawa kan cutar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: GangamiNijeriaWHO
ShareTweetSendShare
Previous Post

Dogaro Da Kasashen Yamma Ba Zai Tabbatar Da Tsaro A Philippines Ba

Next Post

Jihohi 29 Sun Yi Watsi Da Ayyuka 270 Na Biliyoyin Naira

Related

Ra'ayinmu

Bukatar Hukunta Masu Jagorantar Kashe-kashe A Nijeriya

1 month ago
Yadda Rashin Isassun Malaman Turanci Da Lissafi Ke Shafar Ingancin Ilimi A Nijeriya (3)
Ra'ayinmu

Akwai Bukatar Daina Cin Zarafin Malaman Makaranta

1 month ago
Bikin Ranar Muhalli Ta Duniya: Akwai Babban Aiki A Gaban Nijeriya
Ra'ayinmu

Bikin Ranar Muhalli Ta Duniya: Akwai Babban Aiki A Gaban Nijeriya

2 months ago
Bukatar Kara Yawan Masu Fitowa Kada Kuri’a A Zabuka Nan Gaba
Ra'ayinmu

Bukatar Kara Yawan Masu Fitowa Kada Kuri’a A Zabuka Nan Gaba

2 months ago
Wajibi A Mayar Da Hankali Kan ‘Yancin Yara
Ra'ayinmu

Wajibi A Mayar Da Hankali Kan ‘Yancin Yara

3 months ago
Daurarru
Ra'ayinmu

Bukatar Inganta Rayuwar Daurarru A Gidajen Yarin Kasar Nan

4 months ago
Next Post
Jihohi 29 Sun Yi Watsi Da Ayyuka 270 Na Biliyoyin Naira

Jihohi 29 Sun Yi Watsi Da Ayyuka 270 Na Biliyoyin Naira

LABARAI MASU NASABA

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

August 24, 2025
Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

August 24, 2025
Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

August 24, 2025
An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

August 24, 2025
CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

August 24, 2025
Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

August 24, 2025
An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

August 24, 2025
Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

August 24, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

August 24, 2025
Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

August 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.