ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bikin Ranar Muhalli Ta Duniya: Akwai Babban Aiki A Gaban Nijeriya

by Leadership Hausa
12 months ago
Muhalli

Duba da yadda Nijeriya ke ci gaba da fuskanatar kalubalen kula da kare muhalli, a nan za a iya cewa, zagayowar bikin ranar kula da muhalli ta duniya, ta zo kan gaba.

Taken taron na 2025, shi ne, yakar zubar da robobi, musaman da ake kira a turance,‘Take Way’ da ke haifar da gurbatar muhalli.

  • Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba
  • Gwamnatin Kano Ta Soke Tsaftar Muhalli A Watan Afrilu Saboda Jarabawar JAMB

Zubar da wadannan robobin, na shafar kiwon lafiyar alumma da lalata ruwan da ke a cikin Koguna da kuma abincin da bil Adama ke ci.

ADVERTISEMENT

Kazalika, zuba su da ake yi a cikin Kona, sukan yi ambaliya, su zuwa cikin gonakai da cikin birane, musaman duba da cewa, a daukacin fadin duniya, an mayar da hankali ne, wajen daukar matakan gaggawa domin kare muhalli.

Ministan Ma’aikatar Kula da Muhalli Balarabe Abbas Lawal, a jawabin da ya yin a bikin ranar ya jaddada bukatar daukar matakan gaggawa, kan gurbata muhalli, mussamman duba da cewa, kalubalen, na shafar lafiyar bil Adama.

LABARAI MASU NASABA

Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?

Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan

Abbas ya kuma jaddada bukatar da dauki matakai, kan aukuwar sauyin yanayi, musamman duba da matsalar talauci da kuma ci gaba da fuskantar kalubalen rashin tsaro, da kasar nan, ke fuskanta.

Bugu da kari, Hukumar kula da ‘yan cirani ta duniya wato IOM ta sanar da cewa, gurbata muhalli da robobin da aka sarrafa zuke haifarwa, suna taka gudunmwa, wajen aukuwar dumamar yanayi da kuma gurbata muhalli.

A cewar Hukumar, matsalar na kuma lalata kasar noma da lalata hanyoyin ruwa, tare da kuma tilasta alumma, tashi daga matsugunan su, zuwa wasu gurare, domin su ci gaba da gudanar da rayuwarsu.

Hakazalika,  a cikin wasu rahotanni da Majalisar Dinkin Duniya ta fitar, sun bayyana cewa, a fadin duniya, ana yin amfani da Lidojin da suka kai, yawan miliyan 500 a duk shekara, wanda kusan tan miliyan 13, suke kwarara zuwa cikin Tekuna, a duk shekara.

Ana kuma yin amfani da Gangunan Mai miliyan 17, da aka sarrafa, aka kuma zuba a cikin Gangunan, inda kuma a fadin duniya, mutane ke sayen Kwalaben Man da suka kai miliyan daya.

An kiyasata cewa, a duk shekara, daobboin da ke rayuwa a cikin Tekuna  guda 100,000 ne, irin wadannan Robobin da aka zuba a cikin Tekunan, suke hallaka su.

Bugu da kari, wasu bincike da aka gudanar, sun nuna cewa, Ruwan sha da ake sarrafawa a sanya a cikin Robobin Shan Ruwa, sun kai kaso 90 a cikin dari, inda kuma Ruwan da ake samu daga Fanfuna, suka ke da kaso  83 a ckin dari, wadanda kuma suke dauke da sanadaran microplastic, da ke makalewa, a cikin Robobin, inda wannan sanadarin, ke shafar kiwon lafiyar bil Adama.

A Nijeriya za a iya cewa, kalubalen na muhalli sun kasance iri-iri, musamman duba da annobar ambaliyar ruwan sama da kasar ke fuskanta a duk lokacin damina da Fari da gurrbatar muhalli da kuma rashin samar da kyakyawan tsarin zubar da shara, musamman na bolar Robobin da aka gama amfani da su.

Misali, a ranar 28 na watan Mayun 2025, garin Mokwa, da ke a jihar Neja, an fuskanci, mummunar ambaliyar ruwan sama, inda jami’ai suka sanar da cewa, sama da mutane 200 da iftila’in ya aukwa, suka rasu tare da kuma bacewar mutane da yawansu ya kai sama da 1,000, wasu 121 suka samu raunuka, gidaje 2,000 suka lalace.

Irin wannan iftila’in na Mokwa, na daya daga cikin rin wadanda suka auku a shekarun baya a wasu sannan kasar.

Ana nan, muma mun goyi bayan furucin da Ministar Kula da Jindadi da Walwalar Mata Hajiya Imaan Sulaiman-Ibrahim ta yi, na ciwar kalubalen na gurbatar muhlaii, na janyo tarwatsa alumomin kasar, daga matsugunan su, musamman duba da yadda iftila’in, yafi shafar mata da yara.

Batun da ake yi na samar da wadataccen abincin a kasar, zai kasance ne tamkar wani mafarki, matukar mahukutna kasar, ba su yi gaggawar daukar matakan da suka kamata, kan batun na gurbatar muhalli, a kasar ba.

Domin samar da tsarin rage zubar da bola, musamman ta Robobi a kasar Gwamnatin Tarayya ta gabatar da wani tsari na  NPPWM.

Sai dai, wannan tsarin ya hadu da cikas, musamman duba da cewa, wanzar da tsarin daga bangaren Gwamnatin, ba ta mayar da hankali akansa ba, inda sai dai kawai, daidaikun ‘yan kasar ne a kashin kansu suke ci gaba da tsaftace guraren da ake jibge bola, musamman a birane da wasu guraren.

Shugabar Babban Majalisi a Majalisar Dinkin Duniya Maria Fernanda Espinosa Garcés, ta bayar da shawarar cewa, batun na gurbar muhalli, abu ne, da ya wajaba a sake tunani akai.

A daukacin jihohi 36 na kasar, Legas da Ekiti ne kawai, suka dauki matakan da suka kamata, kan kare gurbatar muhalli, a jihohinsu.

Kazalika, a matakin Majalisa, Shugaban Kwamiti kan Yada Labarai da Kula da Hudda da Jama’a Hon. Akin Rotimi ya shelanta cewa, daga cikin kudurori 899 da Majalisar ta gabatar a cikin shekaru biyu, guda 27 ne kacal, Majalisar ta mayar da hankali kan na kula da muhalli.

Sai dai, an ruwaito cewa, wani Majalisar na kan kokrin samar da wasu tsare-tsare na yakar yawan amfani da Robobin barkatai a kasar, musamman a biranen kasar.

A ra’ayin wannan Jaridar, muna goyon bayan cewa, ba zai yuwa a bar Nijeriya a baya, wajen shiga cikin kokarin da ake yi, a fadin duniya, na yakar gurbata muhalli ba.

Ya zama wajbi, bikin na wannan shekarar, ya kasance mataki na farko, na yakar gurbata muhalli, ba wai kawai tatsuniya ba.

Muhalli
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
  • Leadership Hausa
    Ikirarin Cewa Sanata Abdul’aziz Yari Abubakar, Marafan Sokoto, Nauyi Ne Ga Jihar Zamfara Da Jam’iyyar APC Ba Ta Da Tushe
  • Leadership Hausa
    Nazarin Kisan Gillar Da ‘Yan Kato Da Gora Suka Yi Wa Wani Matashi A Biniwe

MASU ALAKA

Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?
Ra'ayinmu

Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?

May 29, 2026
Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan
Labarai

Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan

May 22, 2026
Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
Ra'ayinmu

Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

May 15, 2026
Next Post
Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe 8 A Katsina

Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta'adda, Sun Kashe 8 A Katsina

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.