ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gangamin Yaki Da Cutar Kuturta A Nijeriya

by Ra'ayinmu
1 year ago

A duk ranar 26, na watan Janairun kowacce shekara ne, ake gudanar da bikin zagayowar ranar tunawa da masu larurar cutar Kuturta.

Nijeriya ta shiga cikin sahun kasashen duniya, wajen gudanar da bikin zagayowar ranar, tunawa da masu larurar Kuturta, ta wannan shekarar.

Mahimmancin wannan ranar ita ce, gano cutar a kan lokaci da kuma yadda za a magance ta.

ADVERTISEMENT

Take taron na wannan shekarar 2025 shi ne, “Hada Kai, Domin Kakkave Cutar, wadda ke da mahimmanci a kawo karshen ta, fadin duniya”.

Manufar ita ce, domin a wayar da kai kan cutar, bayyana kalubalen da masu larurar ke fuskanta, tare da hada kai, domin a dakile cutar.

LABARAI MASU NASABA

Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?

Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan

  • Karon Farko A Shekarar 2025: Turken Rarraba Hasken Wutar Lantarki Ya Fadi A Nijeriya
  • ‘Yan Nijeriya Ku Kauracewa Amfani Da Layukan Waya Na MTN, Airtel Da Glo – NLC

Muna sane da cewa, cutar a yanzu, ta kai akalla shekaru 4,000, inda hakan ya sanya ta kasance daya daga cikin tsoffin cutukan da alumma suka san da su,

Hukumar jin kai ta kasar Faransa wato Raoul Follereau ce, ta zavo wannan ranar, domin girmama rayuwar marigayi Mahatma Gandhi, da ya mutu a watan Janairun 1948.

Gandhi, a lokacin yana raye, ya yi aiki tukuru, domin tallafawa masu larurar.

Kimanin mutane 200,000 da suka kamu da cutar ne, ake duba lafiyarsu ako wacce shekara a kasashe 120, inda kuma wasu da dama, ke ci gaba da rayuwa da wasu nau’ukan cutar, musamman a yankin Asiya, Afrika da kuma a Kudancin Amurka.

Kazalika, cutar ta kasance, ta na daga cikin cututtukan da aka yi watsi da batunsu a yankin nahiyar Afirka wadda kuma ta ci gaba da zama abin damuwa, ga vangaren kiwon lafiya a kasar nan.

Sai dai, za a iya cewa, Nijeriya ta samu nasara a shirinta na kasa, na yakar cutar kusan kasa da yawan alummarta daya a cikin dubu goma a shekarar 1998.

Duk da wannan nasarar ta Nijeriya ta samu, akwai batutuwan maganar al’ada, kin sauya dabi’a da har yanzu, ke ci gaba da janyo samun vullar cutar a kasar.

Idan za a iya tunawa, Shirin Dakile Yaduwar Cutar Fuka da Kuturta ta kasa NTBLCP, da aka faro shirin a shekarar 1989, daga shekarar 1991 zuwa shekarar 2012, kimanin masu larurra su 111,788 aka bai wa magunguna masu karfi domin duba lafiyarsu

Kazalika, Nijeriya ta kuma samun wani tallafi daga Hukumar Kiwon Lafiya ta Duniya WHO na dakile cutar wanda ya kai kasa da duba lafiyar masu larurar su 10,000 a shekarar 2000.

Bisa saurin gano cutar a kasar nan, hakan ya sanya an samu kasa da kashi biyar, a cikin duk mutane 10,000, wanda hakan ya sanya a yanzu a Nijeriya aka samu raguwar cutar.

Sai dai, a wani matakin akwai yankunan da cutar ke yin kamari, inda ta kai ga a cikin duk mutune 10,000 ake samun mutum daya, na dauke da cutar.

Bugu da kari, kashi 10 aka samu na cutar a fadin Afirka a 2019, wanda a Nijeriya, da wasu kasashe 12 aka ruwaito cewa, an samu vullar cutar da ta kai daga 1,000–10,000.

A bikin zagayowar ranar cutar ta shekarar data gabata kungiyar kwarrun Likitocin Kiwon Lafiya ta kasa NMA, ta nuna damuwarta kan ci gaba da yaduwar cuatar, duk da kokarin da aka yi, na yakarata baki daya a kasar.

Har yanzu a kasar nana, ana ci gaba da samun rahoton masu fama da cutar, a wasu jihohin kasar, inda kuma a wasu kasashe 17, aka samu rahoton ana samun cutar a duk shekara, da ta kai 1,000.

Wasu alkaluma sun nuna cewa, daga 2011 zuwa 2021 a duk shekara ana samu sabbin kwayoyin cutar da suka kai guda 2,754, wanda suka kai kashi 93.

A cewar kungiyar, kashi 8.3 na sabbin kwayoyin cutar, ana samun su ne, a jikin yara ‘yan kasa da shekaru 15, wanda kuma sabbin kwayoyin cutar ke nuna cewa kashi 14.3 ke yanyo nakasa, wanda hakan ya nuna cewa, hakan ya faru ne, saboda jinkirin daukar matakan duba lafiyar wadanda suka kamu da kwayar cutar.

Bisa wasu alkamuna da Shirin Dakile Yaduwar Cutar Fuka da Kuturta ta kasa NTBLCP da kuma Shirin Buruli da ke Dakile Ciwon Ulcer ya fitar a 2022, sun nuna cewa, an samu sabbin kwayoyin cutar da suka kai 2393, a shekarar 2022, inda aka samu mata kashi 37, na dauke da kwayoyin cutar yara kuma kasa da goma na dauke da kwayoyin cutar.

Hukumar WHO ta bayyana cewa, akasari cutar ta fi shafar Ftar jikin bil Adma ne wacce kuma take janyowa wanda ya kamu da ita, nakasa, idan har ba a yi masa magani ba.

A cewar WHO, ana kamuwa da cutar na yazuwa ne daga Hanci da Bakin wanda ya kamu da ita.

Ana warke wa daga cutar, ta hanyar yin amfani da magungunan da ake yakarta da kuma yin gwaje-gwaje.

Sai dai, wadanda suka kamu da cutar, suna yin jinkirin zuwa a yi masu gwajinta, musamman domin kar a rinka nuna masu kyama.

Bikin ranar ya yi daidai da manufar cimma burin karnin rayuwa wato (SDGs).

Ranar ta kasance mai matukar mahimmanci wanda taron ke hado kan kwararu a fanin kiwon lafiya domin tattaunawa kan cutar.

Nijeriya
Ra'ayinmu
+ postsBio
  • Ra'ayinmu
    https://hausa.leadership.ng/author/raayinmu/
    Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?
  • Ra'ayinmu
    https://hausa.leadership.ng/author/raayinmu/
    Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan
  • Ra'ayinmu
    https://hausa.leadership.ng/author/raayinmu/
    Ce-ce-ku-ce Kan Batun Biyan Bashin Naira Tiriliyan 3.3 Na Kuɗin Lantarki
  • Ra'ayinmu
    https://hausa.leadership.ng/author/raayinmu/
    Matsalar Ɓacewar Gandun Dazukan Nijeriya

MASU ALAKA

Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?
Ra'ayinmu

Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?

May 29, 2026
Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan
Labarai

Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan

May 22, 2026
Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
Ra'ayinmu

Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

May 15, 2026
Next Post
Jihohi 29 Sun Yi Watsi Da Ayyuka 270 Na Biliyoyin Naira

Jihohi 29 Sun Yi Watsi Da Ayyuka 270 Na Biliyoyin Naira

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.