ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bukatar Hukunta Masu Jagorantar Kashe-kashe A Nijeriya

by Leadership Hausa and Sulaiman
11 months ago

A kwanan baya ne, Muyiwa Ige, da ga marigayi Cif Bola Ige, ya yi kira ga shugaba Bola Tinubu, da sake bijiro da batun kisan da aka yi wa mahaifinsa, musamman domin a bankado da wadanda suka aikata kisan, tare da hukunta su.

Yau dai, shekaru 24 ke nan, da aka halka Ige, a gidansa da ke a garin Ibadan, a jihar Oyo, wanda aka kashe shi, a ranar 23 na watan Disambar 2001.

  • Hukumar ‘Yansanda Ta Yi Wa Wasu Manyan Jami’anta Karin Girma
  • Gwamna Lawal Ya Yi Ta’aziyyar Sarkin Katsinan Gusau

A cikin rokon da Muyiwa ya yiwa Tinubu na sake bijro da batun kisan na mahaifinsa, ya bayyana irin halin gallazawa da mahaifinsa, ya tsinci kansa a lokacin kisan, musamman duba da cewa, mahaifin na sa, akawai wasu muradu, na rayuwarsa, da ya so ya cimma, amma kisan ya kawo karashen hakan.

ADVERTISEMENT

An dai hallaka Ige ne, a lokacin da yake rike da mukamin Minitan Shari’a kuma Atoni Janar na kasa.

Bayan gaza cafko wadanda ake zargi da aikata kaisan da kuma yadda akai ta kai Gwaro da Mari a gaban kotu kan batun a wadancan shekaru, haka dai lamarin ya sha ruwa.

LABARAI MASU NASABA

Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?

Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan

Koda ya ke dai, a lokacin ‘yansanda sun yi nisa ban gudanar bincike, amma babu wanda suka iya kamawa, kuma ba a kara shigar da wata sabuwar kara a gaban kotu ba, duk tsawon wadannan shekarun.

Wannan bukatar da Muyiwa ya biro da ita, tamkar bude wani sabon babi ne, kan batun hallaka manyan mutane a kasar, wadda za a iya cewa, tun daga 1999, har zuwa yau, amma shiru ake ji, kan daukar wani kwakwaran mataki.

A wani taro a kwanan baya, babban Lauya SAN Cif Kanu Agabi, ya bijiro da zargin yadda ake gaza hukunta masu aikata manyan laifuka a kasar, inda kuma ake samun dogon jan kafa, kan shari’ar da ta shafi, marasa karfi a kasar.

Wannan zargin na Kanu, ya nuna a zahiri, yadda aka yiwa bangaren shari’ar kasar, rikon Sakainar Kashi, musamman wajen gaza cafko, masu aikata manyan laifuka, domin su fuskanci hunci.

Bugu da kari, a kasidar da ya gabatar a a taron jamia’r NOUN, tsohon shugaban kasa, Cif Olusegun Obasanjo, ya bayyana cewa, yin gaskiya wanzar da zaman lafiya tabbatar da tsaro, tare da bai wa ko wanne dan kasa hakkinsa, su ne, ginshikin da ke bunkasa tattalin arzikin kasa.

Sai abin dubi a nan, wannan yawabin na, Cif Olusegun, ya kasance yana cin karo da juna, domin a lokacin yana kan Karagar shugabancin kasar ne, aka kashe marigayi Ige.

Cafko irin wadannan masu halka manyan mutane a kasar domin a hukunta su, kamar yadda dokar kasa ta tanada, ba wai kawai hakan zai samar da salama ga ahalinsu bane, musamman duba da yadda suka yi babban rashi, amma hakan zai kuma zama wani babban abin ci gaba, ga kasar.

Kazalka, kamo su din, zai zama tamkar wani gargadi ne, da zai nuna cewa, akwai hukuncin da kasar ta tanadar, ga masu aikata irin wannan halin na rashin imani.

A nan, wannan Jaridar, ta yi waiwaye kan kisan rashin imani da aka akatawa mataimakin shugaban PDP na shiyyar Kudu Maso Kudu Cif Aminasoari Kala (A.K) Dikibo shekaru 21 da suka gabata.

Abin takaici, an hallaka shi ne, da tsayiyar rana a kan wata babbar hanya, a ranar ga 4 Fabiraurun 2004.

Sai dai, har zuwa yanzu, babu wani kokari da rundunar ‘yansanda ko hukumar DSS suka yi, na bankado makasan.

Kazalika, tshohon mataimakin shugaba na Kudu Maso Kudu, rusasshiyar jami’iyyar ANPP Marshal Sokari Harry, an kashe shi a Abuja a ranar 5 ga watan Maris na 2003 a lokacin zaben shugaban kasa

Hakazalika, an yiwa dan siyasa Anthony Olufunsho Williams, kisan gilla a gidansa da ke a rukunin gidaje na Dolphin, a jihar da ke Ikoyi, Legas, a ranar 27 ga watan Julin 2005.

An hallaka shi ne, yayin da ake shirin tsayar da shi, dan takarar gwamna a PDP na jihar Legas.

Rashin daukar matakin, na kara zubur da kimar Nijeriya a idon duniya.

Hakazalika, hakan ya sanya, wasu hukumomin a jihohin kasar nan, ke shawartar alumomin, da su dauki matakan kare kansu, daga hare-haren da aka kai wa jama’a, wanda hakan karara, ya nuna gazawar gwamnatin kasar, na kare rayuka da kuma dukiyoyin ‘yan kasar.

A saboda haka, akwai bukatar, a yiwa bangaren shari’a na kasar garanbawul, domin a lalubo da mafita kan lamarin.

Ko da yake dai, majalisar kasa na kan yunkurin sabunta dokar zabe ta 2022.

A matsayin mu a wannan Jaridar, mun kasance kan gaba wajen yin kira da a samar da sauye-sauye a bangaren shari’a, musamman domin a dawo da kimar da bangaren yake da shi, kamar yadda aka san shi, a shekarun baya.

A tunanin mu, samar da wannan sauye-sauyen a bangaren shari’ar, za a samar da kyakyawan yanayi a bangaren na shari’a, tare da gaggawar daukar makai, kan irin wannan kisan gillar da ake yiwa manyan kasar.

Kashe-kashe
Leadership Hausa
Website |  + posts Bio
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
Kashe-kashe
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?
Ra'ayinmu

Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?

May 29, 2026
Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan
Labarai

Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan

May 22, 2026
Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
Ra'ayinmu

Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

May 15, 2026
Next Post
Jiragen NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Lalata Baburansu 40 Da Bindigu 6 A Borno

Wasu Mahara Sun Sake Kashe Mutum 14 A Wani Kauyen Jihar Filato

LABARAI MASU NASABA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.